XtGem Forum catalog
Google69490f6862051cb8
google-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlBasheer journalist sharfadi14

Basheer journalist sharfadi14.jpg6
Basheer journalist sharfadi 11 1
Maraba Da Zuwa Wannan
Shafi Mai Al-barka 1

☀ Zabi inda kake son shiga ☀
Menunks
→Home
→Akidojin Ahlussunnah
→Addinin musulunci (35)
→40 Hadith (50)
→Fadakarwa (120)
→Neman labarai (20)
→Shi'a Kafirci (50)
→Hadith (55)
→Khudubobi (24)
→Tarihin magabata (60)
→Raddi / Maida martani (99)
→Face book post (30)
→Monthly Archives (60)
→Tambaya da Amsa (20)
→Sahabban Annabi {s.aw} (50)
→Taskar maluman sunnah (25)
→Akidar Y'an Shi'a Dangane da Al'kur'ani
→Fassarar Usulussunnah (20)
→Sheik Ja'afar {Rahimahullah} (65)
→Sheik Abubakar Gumi {Rahimahullah} (30)
→Sheik Dr. Muhammad Sani R/Lemo
→Salafiyyah Network Nigeria (100)
→Adam Sani Abu-Umayrah (99)
→Salaf Ustaz (79)
→Malama Ummi Ahmad Katsina
→Malama Amina Saleh Mande
→Labarai (40)
→Nishadantarwa (10)
→Siyasar Nigeria (9)
→Vidio (33)
→Audio (66)
→Hotuna (120)
→Internet Cheat (90)
→Site Achieve
→Application (10)
→Games (8)
→About me (01)

Wannan shafin mallakarCoollogo com-1281358 3
Ne




SHAFI DON KARUWAR MUSULMI
"SARKIN MUMINAI MU'AWIYYA BN ABI SUFYAN [RA]"

Ya Musulunta kafin Fathu Makkah ,amma ya boye Musuluncin sa saboda tsoron Mahaifinsa.
Mu'awiyya na daya daga cikin sakatarori [marubuta] na Annabi[SAW]masu rubuta masa wahayi. Kai kasan koda a ma'aikatar ku akace wane sakatare ne to lalle yanada daraja, balle Fada irinta Annabi[SAW]wadda kaf duniya babu irinta.Ya kuma samu kyakkyawar addu'a a dalilin kokarin sa inda Annabi[SAW] ya roka Masa Allah ya sanya shi shiryayye mai shiryarwa.
Mu'awiyya na daga cikin mayakan Hunaini wanda Allah ya shede su da imani kuma ya ba da sanarwar saukar da nutsuwa a kansu a cikin Taubah 91. Yana kuma cikin mutanen da Allah ya yi wa alkawarin Al Husna wadda itace Aljanna saboda sun ciyar da dukiya saboda Allah bayan cin garin Makka. Ya kuma samu martabar kasancewa shugaba na farko da ya kaddamar da Jihadi a teku, kuma Annabi [SAW] ya yabama wadanda zasu yi yaki a teku, yayi murna da Allah yanuna masa su zazzaune kamar sarakuna a kan gadaje.

Zamu cigaba.
Umar Lajin Kofar wambai
19-4-2015

"JARUNTAKA DA SARAUTA A RAYUWAR MU'AWIYAH [RA]"

Bayan Musuluntar Mahaifinsa Abu Sufyan iyalan gidansu sunyi hijira tare dashi zuwa Madina wurin Annabi [SAW]. Don haka Mu'awiyah ya samu halartar sauran yake-yaken da suka biyo baya.
Game da sha'anin sarauta Mu'awiyah ya dade da tunaninta a ransa tun ranar da Annabi [SAW] ya ce masa, ya kai Mu'awiyah! Idan ka Jibinci wani Al'amari kaji tsoron Allah kuma kayi adalci.
Mutum na farko daya gabatar da Mu'awiyah a sha'anin Mulki shine Khalifa Abubakar Siddik a lokacin daya shugabantar dashi akan wata runduna da zata kai gudummawa ga dan uwan sa Yazid, daya daga cikin jagorori 4 da suke yaki a kasar Sham.
Mu'awiyah ya cigaba da yaki a karkashin tutar dan uwansa in da bajintar sa tasa aka rinka shugabantar dashi akan kananan rundunoni yana cin nasara. Daga baya a zamanin sarkin Musulmi Umar Bn Khaddab aka ba Yazidu umarni ya shugabantar da kanin nasa don cin garin kaisariyyah, ya tafi kuma Allah yabashi nasara a can.

Zamu cigaba.
Umar Lajin kofar wambai
21-4-2015

"AYYUKAN SA A ZAMANIN SARAUTAR SA SARKIN MUMINAI MU'AWIYAH [RA]"

Sarkin Musulmi Mu'awiyah ya kula sosai da sha'anin tsaro a kasar musulunci, shine shugaba na farko a musulunci da ya fara sa matsara a dalilin yunkurin kisansa da khawarij sukayi. Yakuma kafa ma'aikatu da dama don cimma wannan manufa. A dalilin haka gwamnatinsa ta samu karfinda yasa tazamo babbar barazana ga duk sauran al'ummai na duniya a wannan lokaci.
Sannan shi ya fara kafa ma'aikatar kula da wasikun Sarki don gudun kar a sauya su.
Haka kuma Mu'awiya ya kula da sha'anin ilimi da jin dadin Malamai. A kan haka ne ya kafa cibiyar nazari da fassara wadda aka bata suna Baitul Hikmah. Ya kuma mayar da hankali ga inganta rayuwar talaka. Haka kuma ya mayar da hidimar alhazai kyauta.
A zamanin sa ne kuma yasa akayi magudanan ruwa a Madina, abinda yakawo karshen matsalar cushewar ruwa musamman a lokacin damina a cikin garin Madina a wancan lokaci.

Zamu cigaba
Umar Lajin Kofar Wambai
22-4-2015



SUHAIBUR RUMIY[RA]
.
.
Ya Musulunta tun da wuri, yana cikin wadanda aka dandana musu azaba saboda imaninsu ga Allah[SWT].
Suhaib sun Musulunta rana 1 da Ammaru.
.
Ammaru yace, "Wata rana na hadu da Suhaib a kofar gidan Arkam bn Abul Arkam, a lokacin Annabi[SAW] yana ciki, sai nace masa, "Me kazo yi? Sai ya amsa mini da cewa, "kai me kazo yi? Sai na ce, Nazo da nufin shiga wajen Muhammadu, sai Suhaib yace, Nima hakan ne ya kawo ni". Sai muka shiga wajen Annabi [SAW], Sai ya bijirar mana da musulunci. Sannan muka zauna a gidan har yamma tayi. Sannan muka fito muna boyewa domin tsoron mushrikan Makka.
.
Lokacin da zai yi hijra, mushrikai sun tsare shi cewa bazai yi hijrar ba sai ya bar dukkan dukiyarsa, sai kuwa yabasu dukkan abinda ya mallaka.
.
An ruwaito shi yana cewa, "Annabi [SAW] bai taba halartar wani guri ba sai na kasance na halarce shi, ban taba ganin wani abin tsoro a gaban sa ko bayansa ba sai na kasance na kare shi".
.
ALLAHU AKBAR
.
Ya Allah ka kara yarda da aminci ga Sahabbai.



ABDULLAHI BN MAS'UD [RA]
.
Yana cikin wanda suka fara musulunta tun kafin Annabi[SAW] ya shiga gidan Arkam bn Abul Arkam, sababin musuluntar kuwa shine a lokacin da yake kiwon dabbobi ne a Makka Annabi [SAW] yazo wucewa shida Abubakar [RA], sai ya tambaye shi yabasu nono. Sai yace,
.
"Dukkan dabbobin basu da nono". Sai Annabi [SAW] ya sanya hannun sa ya ambaci sunan Allah take nonon ya bulbulo, dukkan su suka sha suka koshi.
.
Wannan abu da Abdullahi ya gani sai mamaki ya rufe shi, ya ce da Annabi [SAW]
.
"koya min abinda ka fada haka ta kasance".
.
Sai Annabi [SAW] ya koyar dashi surori 70 daga bakin sa.
.
Yayi hijira sau 2, ya halarci yakin Badar da dukkan yakoki tare da Annabi[SAW].
.
Yana cikin manyan hadiman Annabi [SAW].
.
Shine gaba da kowa wajan iya karanta alqur'ani.
.
Shine Mutum na farko daya fara bayyanar da karatun alqur'ani a fili a gaban mushrikan Makka.
.
A zamanin Umar [RA] ya turashi kufa domin ya dinga karantar dasu alqur'ani da hukuncin shari'a.
.
Allah yakara masa yarda



SA'AD BN ABI WAKKAS
.
Yana 1 daga cikin wanda suka fara karbar musulunci,
.
kuma yana cikin mutane 10 da aka yiwa bushara da aljannah tun a duniya, kuma 1 daga cikin mutane shida masu zaben khalifa, kuma 1 daga cikin yardaddu a wajen Annabi [SAW].
.
Ya halarci yakin Badar da dukkan yakoki tare da Annabi [SAW].
.
Yana cikin jarumai maharba na Annabi [SAW], Shine ya fara harba kibiyar sa saboda Allah.
.
Annabi [SAW] yayi masa addu'ar dacewa a duk lokacin da yayi harbi,da kuma amsawar addu'a a wurin Allah, yace,
.
"Ya Ubangiji ka datar da harbin sa, kakuma amsa addu'ar sa".
.
Sa'ad shine ya jagoranci musulmi a zamanin khalifancin Umar wajen rusa Daular Farisa, shine ya bude babban birnin Farisa Mada'in, yakuma kafa garin Kufa.
.
Sa'ad yayi rayuwa mai tsawo cikin tsananin biyayya ga Allah da gudun duniya, ance shi mutum ne mai tsananin tsoron Allah da yawan kuka musamman ma idan Annabi [SAW] yana yimusu huduba da wa'azi.
.
Ya Allah ka kara masa yarda da aminci bisaga aikin da yaiwa musulunci.



ABUBAKAR AS-SIDDIK
.
kashi na 1
.
An haifi Abubakar As-siddik a garin Makka. Yataso cikin nagarta da kyawawan halaye,tarihi yanuna tunda yake baitaba yin sujjada ga gunki ba,
.
kuma baitaba shan giya ba tun a Jahiliyya.
.
Lokacin da Manzon Allah (SAW) ya bayyana kiran musulunci shine mutum na farko daya fara karbar musulunci,
.
wannan kuwa bai rasa nasaba da aminci da kyakkyawar dangantaka da alakarsa da Manzon Allah (SAW).
.
Tun bayan daya amsa kiran musulunci,sai ya mika rayuwar sa da duk abinda ya mallaka wajan cigaban musulunci.
.
Babu tantama cewa Abubakar shine mafificin dukkan Sahabban Manzon Allah (SAW) kamar yadda Aliyu dan Abi Dalib ya tabbatar.
.
Kasancewarsa hamshakin attajiri, ya saukakawa addinin musulunci ta hanyar bayar da dukkan abin daya mallaka wajen ganin yunkurawar addinin musulunci.
.
Manzon Allah (SAW) yana cewa,
.
"Babu wata dukiya data amfane ni, kamar yadda dukiyar Abubakar ta amfane ni".
.
Cikin halin takura da aka jefa raunanan musulmi musamman bayi na cutarwa da gallazawa.
.
Zamu cigaba



AL-HASSAN BN ALIYU
.
Mahaifiyar sa itace Fadimatu 'yar Annabi [SAW]. Yayi kama da Annabi [SAW].
.
Haka kuma shi da dan uwansa Hussain Annabi [SAW] yafiso cikin jikokin sa.
.
An ruwaito daga Usamatu dan Zaid yace: Annabi [SAW] yana cewa,
.
"Alhassan da Hussain jikoki nane ya Ubangiji ni ina sonsu, kaima kaso su, kaso dukkan mai sonsu".
.
Alhassan ya kasance kyakkyawa ne kuma mai kyawun hali.
.
Yayi kyakkyawar rayuwa yana tare da Annabi [SAW] har yayi wafati, bayan wafati ya kasance tare da khalifofi.
.
Yana cikin wadanda suka kawo dauki domin kare Khalifa Usman lokacin da makiya suke kokarin kashe shi.
.
Haka kuma ya kasance tare da Baban sa a matsayin mashawarci.
Anyi masa mubayi'a a matsayin Sarkin Muminai, amma bayan kankanin lokaci sai ya kirawo Mu'awiyya Bn Abu sufyan yabashi jagorancin musulmi.
.
Wannan kuwa gaskata fadin Annabi [SAW] ne da yake cewa
.
"Lalle wannan jika nawa shugaba ne kuma ina fatan ta dalilin sa Allah zai sulhunta wasu bangarorin musulmai masu girma".
.
Allah ka kara masa yarda.



AL-HUSSAINI BN ALIYU
.
Shima dai kamar dan uwansa yayi kama da Annabi [SAW].
.
Hussaini da dan uwansa sun sami albarkar kasancewa Sahabban kakansu duk da suna yara yabar duniya. Haka kuma Abubakar, Umar da Usman suna girmama su da kuma nuna tsananin soyayya a garesu.
.
Bayan rasuwar Mu'awiyya, aka yiwa dansa Yazid mubayi'a. Wanda a wannan lokaci Hussaini bai amince ba. A wannan lokaci sai mafi sharrin wannan al'umma mutanen kufa suka yi ta yimasa wasiku suna kiransa yazo su yimasa mubayi'a. Da farko yaki amincewa saboda 'yan uwansa da kuma wasu daga cikin Sahabbai suka hanashi. Amma daga baya suka yaudare shi yaje.
.
Daga karshe dai sun kashe shi Hussaini, yayi shahada a karbala kasar Iraki, ranar Ashura goma ga watan Muharram.
.
ABIN LURA ANAN:
Annabi [SAW] bai ware wani daga cikin jikokin nan nasaba da yafi so, dukkan su yanuna musu soyayya ba bambanci, hakama Sahabban sa sun so su. Bakamar yarda wasu sukafi nuna soyayyar su ga Hussaini ba.
.
Ya Allah ka kara musu yarda da aminci.



MUS'AB BN UMAIR
.
Ya taso a cikin jin dadi, gashi dan gata kuma kyakkyawa mai iya ado, dukkan wani taro baya cika idan babu Mus'ab a cikinsa.
.
Yana cikin wannan hali ne ya sami labarin kiran musulunci ta bakin amintacce Muhammadu[SAW],bai yi jinkiri ba wajen amsa kiran duk da sanin irin matsin da zai fuskanta.
Mus'ab ya hakura da dukkan jin dadin duniya, ya maye shi da dandanar kuda da azabtarwa daga mutanensa.
.
Wata rana mus'ab ya taho gurin Annabi [SAW] sahabbai sun kewaye shi, lokacin da suka hango Mus'ab sukaga irin halin da ya shiga na kunci da takura sai suka sunkuyar da kawunan su suna kuka saboda tausaya masa.
.
A ranar yakin Badar shine yake rike da tutar Annabi [SAW] babbar ta Muhajirun hakama a yakin Uhudu inda a ranar yai shahada.
.
An ruwaito Annabi [SAW] ya tsaya a gaban Mus'ab da sauran wanda sukai shahada a Uhudu yana cewa:
.
"Lallai zanyi muku shaida cewa ku shahidai ne a gurin Allah ranar Alkiyama".
.
Ya Allah ka kara yarda da amincinka a garesu



SALMANUL FARISI [RA]
.
Ana kiransa Salmanu bnil Islam, ana kuma yimasa lakabi da Salmanul Khair, ana kuma yimasa alkunya da Abu Abdullahi.
.
Asalinsa Mutumin Asbahan ne ta kasar Farisa. Ya sami labarin za a aiko Annabi [SAW], sai yayi shiri ya fita nemansa, domin ya kasance cikin wadanda suka yi Imani dashi.
.
A hanya ne wasu suka sayar dashi a matsayin Bawa, bayan tsananin wahala da yasha har yazo Madina.
Ya sadu da Annabi [SAW] daf da lokacin yakin khandak, ya halarci yakin, shine ya bawa Annabi [SAW] shawarar a haka ramin gwalalo domin hana kafirai haurowa su shigo Madina.
.
Ya halarci dukkan yakokin da suka biyo bayan Khandak. Khalifa Umar [RA] yanada shi Gwamnan Birnin Mada'in.
.
Abu Burdah ya ruwaito daga Baban sa cewa, Annabi[SAW] ya ce,
.
" Lallai Allah yanason mutum 4 daga Sahabbai na daga cikin su akwai Salmanu".
.
Mutum ne shi mai tsananin tsoron Allah da gudun duniya da kaifin kwakwalwa, tsantseninsa kuwa ana kwatantashi da Khalifa Umar [RA].
.
Allah yakara masa yarda da aminci.





Koma saman shafi

→Labarai

SAKON BANGAJIYA DAN GANE DA ZIYARAR SHUGABA A BIRNIN KANO:

SAKON BANGAJIYA DAN GANE DA ZIYARAR SHUGABA A BIRNIN KANO:

A madadin shugabannin kungiyar Izala ta Jihar kano tun daga kan hukumar gudanarwa hukumar Agaji kwamitin Malamai kwamitn Social media kano karkashin jagorancin sarkin izalar kano Shekh Dr. Abdallah Saleh Pakistan (P.H.D).

•Suna mika sakon bangajiya ga Shugaban kungiyar Izala ta kasa baki daya Sheik Abdullahi Bala Lau da yan tawagar sa wanda suka hada:

-Sheik Dr Al'hassan Sa'eed Adam Jos.
-Sheik Rabi'u Daura.
-Sheik Kabiru Haruna Gombe.
-Sheik Tukur Isah.
-Sheik Abdulbasir Unguwar mai kawo.
-Sheik Musa yusuf Asadussunnah.
-Daraktan Agaji nakasa Injinya Mustapha Imam Sitti.
-Shugaban Kwamitin Jibwis Social Media ta kasa: Ustaz Ibrahim Baba Sulaiman.

Dasauran yan tawagar shugaba bisa ziyarar ta'aziyyar Sheik Dr. Aminuddeen Abubakar na rasuwar sa da suka kawo jiya Talata 4/8/2015.

A lokacin ziyarar tawagar shugaban ta je gidan marigayin inda yayiwa 'ya'ya da iyalan marigayin Ta'aziyya.

Daga nan ya wuce hukumar Sakatariyar Hisba ta Jihar kano inda yayi musu gaisuwa karkashin jagorancin Babban kwamandan Rindinar Sheik Aminu Ibrahim Daurawa wanda shi marigayin yake shugabantar hukumar alokacin rayuwar sa.

Daga nan ne asafiyar yau laraba kuma shugaba Abdullahi Bala lau ya ziyarci Fadar Gwamnatin Jihar inda nan ma yayi masa ta'aziyya da sauran bayanai.

Muna Addu'ar Allah ya maida kowa gidansa lafiya.

Abu-Unaisa
Mataimakin shugaban
Jibwis Social media
Kano state
5/8/2015.

Back to posts
Comments:
[2015-12-24 12:33:23] Muhammad lukhman alhassan :

Allah yakara wa malaman sunnah lafiya

[2018-08-14 22:44:22] Josephvok :

Social service essay writing What is the one gadget that you could not live without Explain essay writing Is anything private anymore Discuss how companies track your habits essay writing The season you like most essay writing A college theatrical essay writing <a href=https://academic365.site/>write movie reviews online</a>
Sweet are the uses of adversity essay writing Literature and society essay writing Science and agriculture essay writing Leisure essay writing Broadcasting essay writing A boat-trip in moonlight essay writing The concept op peaceful co-existence essay writing Peace hath her victories no less renowned than war essay writing All things both great and small essay writing Atomic bomb and the domino theory essay writing The importance of music essay writing The place of literature in education essay writing Agriculture and industrial growth essay writing Parliamentary democracy essay writing Most typical cyber crimes essay writing https://academic365.site/ cheap paper writing service resume service writing chemistry coursework recommended essay writing service how can i write resume

[2018-08-17 21:13:59] buy a cover letter :

What is the best advice you have ever received essay writing The choice of professions essay writing Specialization in education essay writing Careers open to a young man essay writing The night before an examination essay writing <a href=https://academic365.site/>write movie reviews online</a>
Conference makes a ready man essay writing Charity begins at home essay writing Art and morality essay writing co-operative farming essay writing A thrilling experience in your life essay writing What is the best advice you have ever received essay writing An ideal college essay writing Should people stop using Facebook Why or why not essay writing College sports essay writing The peaceful use of atomic power essay writing Science and religion essay writing Journalism essay writing Leisure essay writing Science in the modern world essay writing How do you propose to spend the long vacation essay writing https://academic365.site/ general essay topics coordinated science igcse write a essay online cv professional writing paper


UNDER MAINTENANCE

Share|

Kaima shiga a tattauna da kai
* No boards.

Online: Guests: 1


→Ra'ayin jama'a game damu

 IDAN KANA BUKATAR A TALLATA MAKA HAJAR KA A WANNAN SHAFIN DA SAURAN SHAFUKAN MU KANA IYA TUNTUBAR MU TA WADANNAN HANYOYIN KAMAR HAKA:


Email: bjournalist55@hotmail.com

Phone No: 09035830253

Facebook: Basheer Journalist Sharfadi

Address: Ittihad Computer Centre,  No 92 Daneji Kano


MAI TALLA SHI KE DA RIBA


*Bayanan ka*
Browser din da ka hawo Mozilla

Kasar da kake

Adadin Maziyarta 317556

Adadin Wadanda Sukayi Comment 65691

A Wadanda Suka Shiga Tattaunawar Mu 54


Follow @bjournalist55
→Yi Adding Dina Ta Facebook
→Yi Like Na Dakarun Sunnah Page
→Yi Like Dina Ta Facebook

*Shafuka Masu Alaka Da Mu*

→Basheer Sharfadi wordpress
Basheer Sharfadi Blog Spot
UP
→Home

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah)
ISLAMIC DATE
  • phpimg2.php?it&ic=yellow



  • Click to Sms
    Click to Call


    Basheer journalist sharfadi3
    Coollogo com-1281358