Old school Swatch Watches
Google69490f6862051cb8
google-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlBasheer journalist sharfadi14

Basheer journalist sharfadi14.jpg6
Basheer journalist sharfadi 11 1
Maraba Da Zuwa Wannan
Shafi Mai Al-barka 1

☀ Zabi inda kake son shiga ☀
Menunks
→Home
→Akidojin Ahlussunnah
→Addinin musulunci (35)
→40 Hadith (50)
→Fadakarwa (120)
→Neman labarai (20)
→Shi'a Kafirci (50)
→Hadith (55)
→Khudubobi (24)
→Tarihin magabata (60)
→Raddi / Maida martani (99)
→Face book post (30)
→Monthly Archives (60)
→Tambaya da Amsa (20)
→Sahabban Annabi {s.aw} (50)
→Taskar maluman sunnah (25)
→Akidar Y'an Shi'a Dangane da Al'kur'ani
→Fassarar Usulussunnah (20)
→Sheik Ja'afar {Rahimahullah} (65)
→Sheik Abubakar Gumi {Rahimahullah} (30)
→Sheik Dr. Muhammad Sani R/Lemo
→Salafiyyah Network Nigeria (100)
→Adam Sani Abu-Umayrah (99)
→Salaf Ustaz (79)
→Malama Ummi Ahmad Katsina
→Malama Amina Saleh Mande
→Labarai (40)
→Nishadantarwa (10)
→Siyasar Nigeria (9)
→Vidio (33)
→Audio (66)
→Hotuna (120)
→Internet Cheat (90)
→Site Achieve
→Application (10)
→Games (8)
→About me (01)

Wannan shafin mallakarCoollogo com-1281358 3
Ne




SHAFI DON KARUWAR MUSULMI
"SARKIN MUMINAI MU'AWIYYA BN ABI SUFYAN [RA]"

Ya Musulunta kafin Fathu Makkah ,amma ya boye Musuluncin sa saboda tsoron Mahaifinsa.
Mu'awiyya na daya daga cikin sakatarori [marubuta] na Annabi[SAW]masu rubuta masa wahayi. Kai kasan koda a ma'aikatar ku akace wane sakatare ne to lalle yanada daraja, balle Fada irinta Annabi[SAW]wadda kaf duniya babu irinta.Ya kuma samu kyakkyawar addu'a a dalilin kokarin sa inda Annabi[SAW] ya roka Masa Allah ya sanya shi shiryayye mai shiryarwa.
Mu'awiyya na daga cikin mayakan Hunaini wanda Allah ya shede su da imani kuma ya ba da sanarwar saukar da nutsuwa a kansu a cikin Taubah 91. Yana kuma cikin mutanen da Allah ya yi wa alkawarin Al Husna wadda itace Aljanna saboda sun ciyar da dukiya saboda Allah bayan cin garin Makka. Ya kuma samu martabar kasancewa shugaba na farko da ya kaddamar da Jihadi a teku, kuma Annabi [SAW] ya yabama wadanda zasu yi yaki a teku, yayi murna da Allah yanuna masa su zazzaune kamar sarakuna a kan gadaje.

Zamu cigaba.
Umar Lajin Kofar wambai
19-4-2015

"JARUNTAKA DA SARAUTA A RAYUWAR MU'AWIYAH [RA]"

Bayan Musuluntar Mahaifinsa Abu Sufyan iyalan gidansu sunyi hijira tare dashi zuwa Madina wurin Annabi [SAW]. Don haka Mu'awiyah ya samu halartar sauran yake-yaken da suka biyo baya.
Game da sha'anin sarauta Mu'awiyah ya dade da tunaninta a ransa tun ranar da Annabi [SAW] ya ce masa, ya kai Mu'awiyah! Idan ka Jibinci wani Al'amari kaji tsoron Allah kuma kayi adalci.
Mutum na farko daya gabatar da Mu'awiyah a sha'anin Mulki shine Khalifa Abubakar Siddik a lokacin daya shugabantar dashi akan wata runduna da zata kai gudummawa ga dan uwan sa Yazid, daya daga cikin jagorori 4 da suke yaki a kasar Sham.
Mu'awiyah ya cigaba da yaki a karkashin tutar dan uwansa in da bajintar sa tasa aka rinka shugabantar dashi akan kananan rundunoni yana cin nasara. Daga baya a zamanin sarkin Musulmi Umar Bn Khaddab aka ba Yazidu umarni ya shugabantar da kanin nasa don cin garin kaisariyyah, ya tafi kuma Allah yabashi nasara a can.

Zamu cigaba.
Umar Lajin kofar wambai
21-4-2015

"AYYUKAN SA A ZAMANIN SARAUTAR SA SARKIN MUMINAI MU'AWIYAH [RA]"

Sarkin Musulmi Mu'awiyah ya kula sosai da sha'anin tsaro a kasar musulunci, shine shugaba na farko a musulunci da ya fara sa matsara a dalilin yunkurin kisansa da khawarij sukayi. Yakuma kafa ma'aikatu da dama don cimma wannan manufa. A dalilin haka gwamnatinsa ta samu karfinda yasa tazamo babbar barazana ga duk sauran al'ummai na duniya a wannan lokaci.
Sannan shi ya fara kafa ma'aikatar kula da wasikun Sarki don gudun kar a sauya su.
Haka kuma Mu'awiya ya kula da sha'anin ilimi da jin dadin Malamai. A kan haka ne ya kafa cibiyar nazari da fassara wadda aka bata suna Baitul Hikmah. Ya kuma mayar da hankali ga inganta rayuwar talaka. Haka kuma ya mayar da hidimar alhazai kyauta.
A zamanin sa ne kuma yasa akayi magudanan ruwa a Madina, abinda yakawo karshen matsalar cushewar ruwa musamman a lokacin damina a cikin garin Madina a wancan lokaci.

Zamu cigaba
Umar Lajin Kofar Wambai
22-4-2015



SUHAIBUR RUMIY[RA]
.
.
Ya Musulunta tun da wuri, yana cikin wadanda aka dandana musu azaba saboda imaninsu ga Allah[SWT].
Suhaib sun Musulunta rana 1 da Ammaru.
.
Ammaru yace, "Wata rana na hadu da Suhaib a kofar gidan Arkam bn Abul Arkam, a lokacin Annabi[SAW] yana ciki, sai nace masa, "Me kazo yi? Sai ya amsa mini da cewa, "kai me kazo yi? Sai na ce, Nazo da nufin shiga wajen Muhammadu, sai Suhaib yace, Nima hakan ne ya kawo ni". Sai muka shiga wajen Annabi [SAW], Sai ya bijirar mana da musulunci. Sannan muka zauna a gidan har yamma tayi. Sannan muka fito muna boyewa domin tsoron mushrikan Makka.
.
Lokacin da zai yi hijra, mushrikai sun tsare shi cewa bazai yi hijrar ba sai ya bar dukkan dukiyarsa, sai kuwa yabasu dukkan abinda ya mallaka.
.
An ruwaito shi yana cewa, "Annabi [SAW] bai taba halartar wani guri ba sai na kasance na halarce shi, ban taba ganin wani abin tsoro a gaban sa ko bayansa ba sai na kasance na kare shi".
.
ALLAHU AKBAR
.
Ya Allah ka kara yarda da aminci ga Sahabbai.



ABDULLAHI BN MAS'UD [RA]
.
Yana cikin wanda suka fara musulunta tun kafin Annabi[SAW] ya shiga gidan Arkam bn Abul Arkam, sababin musuluntar kuwa shine a lokacin da yake kiwon dabbobi ne a Makka Annabi [SAW] yazo wucewa shida Abubakar [RA], sai ya tambaye shi yabasu nono. Sai yace,
.
"Dukkan dabbobin basu da nono". Sai Annabi [SAW] ya sanya hannun sa ya ambaci sunan Allah take nonon ya bulbulo, dukkan su suka sha suka koshi.
.
Wannan abu da Abdullahi ya gani sai mamaki ya rufe shi, ya ce da Annabi [SAW]
.
"koya min abinda ka fada haka ta kasance".
.
Sai Annabi [SAW] ya koyar dashi surori 70 daga bakin sa.
.
Yayi hijira sau 2, ya halarci yakin Badar da dukkan yakoki tare da Annabi[SAW].
.
Yana cikin manyan hadiman Annabi [SAW].
.
Shine gaba da kowa wajan iya karanta alqur'ani.
.
Shine Mutum na farko daya fara bayyanar da karatun alqur'ani a fili a gaban mushrikan Makka.
.
A zamanin Umar [RA] ya turashi kufa domin ya dinga karantar dasu alqur'ani da hukuncin shari'a.
.
Allah yakara masa yarda



SA'AD BN ABI WAKKAS
.
Yana 1 daga cikin wanda suka fara karbar musulunci,
.
kuma yana cikin mutane 10 da aka yiwa bushara da aljannah tun a duniya, kuma 1 daga cikin mutane shida masu zaben khalifa, kuma 1 daga cikin yardaddu a wajen Annabi [SAW].
.
Ya halarci yakin Badar da dukkan yakoki tare da Annabi [SAW].
.
Yana cikin jarumai maharba na Annabi [SAW], Shine ya fara harba kibiyar sa saboda Allah.
.
Annabi [SAW] yayi masa addu'ar dacewa a duk lokacin da yayi harbi,da kuma amsawar addu'a a wurin Allah, yace,
.
"Ya Ubangiji ka datar da harbin sa, kakuma amsa addu'ar sa".
.
Sa'ad shine ya jagoranci musulmi a zamanin khalifancin Umar wajen rusa Daular Farisa, shine ya bude babban birnin Farisa Mada'in, yakuma kafa garin Kufa.
.
Sa'ad yayi rayuwa mai tsawo cikin tsananin biyayya ga Allah da gudun duniya, ance shi mutum ne mai tsananin tsoron Allah da yawan kuka musamman ma idan Annabi [SAW] yana yimusu huduba da wa'azi.
.
Ya Allah ka kara masa yarda da aminci bisaga aikin da yaiwa musulunci.



ABUBAKAR AS-SIDDIK
.
kashi na 1
.
An haifi Abubakar As-siddik a garin Makka. Yataso cikin nagarta da kyawawan halaye,tarihi yanuna tunda yake baitaba yin sujjada ga gunki ba,
.
kuma baitaba shan giya ba tun a Jahiliyya.
.
Lokacin da Manzon Allah (SAW) ya bayyana kiran musulunci shine mutum na farko daya fara karbar musulunci,
.
wannan kuwa bai rasa nasaba da aminci da kyakkyawar dangantaka da alakarsa da Manzon Allah (SAW).
.
Tun bayan daya amsa kiran musulunci,sai ya mika rayuwar sa da duk abinda ya mallaka wajan cigaban musulunci.
.
Babu tantama cewa Abubakar shine mafificin dukkan Sahabban Manzon Allah (SAW) kamar yadda Aliyu dan Abi Dalib ya tabbatar.
.
Kasancewarsa hamshakin attajiri, ya saukakawa addinin musulunci ta hanyar bayar da dukkan abin daya mallaka wajen ganin yunkurawar addinin musulunci.
.
Manzon Allah (SAW) yana cewa,
.
"Babu wata dukiya data amfane ni, kamar yadda dukiyar Abubakar ta amfane ni".
.
Cikin halin takura da aka jefa raunanan musulmi musamman bayi na cutarwa da gallazawa.
.
Zamu cigaba



AL-HASSAN BN ALIYU
.
Mahaifiyar sa itace Fadimatu 'yar Annabi [SAW]. Yayi kama da Annabi [SAW].
.
Haka kuma shi da dan uwansa Hussain Annabi [SAW] yafiso cikin jikokin sa.
.
An ruwaito daga Usamatu dan Zaid yace: Annabi [SAW] yana cewa,
.
"Alhassan da Hussain jikoki nane ya Ubangiji ni ina sonsu, kaima kaso su, kaso dukkan mai sonsu".
.
Alhassan ya kasance kyakkyawa ne kuma mai kyawun hali.
.
Yayi kyakkyawar rayuwa yana tare da Annabi [SAW] har yayi wafati, bayan wafati ya kasance tare da khalifofi.
.
Yana cikin wadanda suka kawo dauki domin kare Khalifa Usman lokacin da makiya suke kokarin kashe shi.
.
Haka kuma ya kasance tare da Baban sa a matsayin mashawarci.
Anyi masa mubayi'a a matsayin Sarkin Muminai, amma bayan kankanin lokaci sai ya kirawo Mu'awiyya Bn Abu sufyan yabashi jagorancin musulmi.
.
Wannan kuwa gaskata fadin Annabi [SAW] ne da yake cewa
.
"Lalle wannan jika nawa shugaba ne kuma ina fatan ta dalilin sa Allah zai sulhunta wasu bangarorin musulmai masu girma".
.
Allah ka kara masa yarda.



AL-HUSSAINI BN ALIYU
.
Shima dai kamar dan uwansa yayi kama da Annabi [SAW].
.
Hussaini da dan uwansa sun sami albarkar kasancewa Sahabban kakansu duk da suna yara yabar duniya. Haka kuma Abubakar, Umar da Usman suna girmama su da kuma nuna tsananin soyayya a garesu.
.
Bayan rasuwar Mu'awiyya, aka yiwa dansa Yazid mubayi'a. Wanda a wannan lokaci Hussaini bai amince ba. A wannan lokaci sai mafi sharrin wannan al'umma mutanen kufa suka yi ta yimasa wasiku suna kiransa yazo su yimasa mubayi'a. Da farko yaki amincewa saboda 'yan uwansa da kuma wasu daga cikin Sahabbai suka hanashi. Amma daga baya suka yaudare shi yaje.
.
Daga karshe dai sun kashe shi Hussaini, yayi shahada a karbala kasar Iraki, ranar Ashura goma ga watan Muharram.
.
ABIN LURA ANAN:
Annabi [SAW] bai ware wani daga cikin jikokin nan nasaba da yafi so, dukkan su yanuna musu soyayya ba bambanci, hakama Sahabban sa sun so su. Bakamar yarda wasu sukafi nuna soyayyar su ga Hussaini ba.
.
Ya Allah ka kara musu yarda da aminci.



MUS'AB BN UMAIR
.
Ya taso a cikin jin dadi, gashi dan gata kuma kyakkyawa mai iya ado, dukkan wani taro baya cika idan babu Mus'ab a cikinsa.
.
Yana cikin wannan hali ne ya sami labarin kiran musulunci ta bakin amintacce Muhammadu[SAW],bai yi jinkiri ba wajen amsa kiran duk da sanin irin matsin da zai fuskanta.
Mus'ab ya hakura da dukkan jin dadin duniya, ya maye shi da dandanar kuda da azabtarwa daga mutanensa.
.
Wata rana mus'ab ya taho gurin Annabi [SAW] sahabbai sun kewaye shi, lokacin da suka hango Mus'ab sukaga irin halin da ya shiga na kunci da takura sai suka sunkuyar da kawunan su suna kuka saboda tausaya masa.
.
A ranar yakin Badar shine yake rike da tutar Annabi [SAW] babbar ta Muhajirun hakama a yakin Uhudu inda a ranar yai shahada.
.
An ruwaito Annabi [SAW] ya tsaya a gaban Mus'ab da sauran wanda sukai shahada a Uhudu yana cewa:
.
"Lallai zanyi muku shaida cewa ku shahidai ne a gurin Allah ranar Alkiyama".
.
Ya Allah ka kara yarda da amincinka a garesu



SALMANUL FARISI [RA]
.
Ana kiransa Salmanu bnil Islam, ana kuma yimasa lakabi da Salmanul Khair, ana kuma yimasa alkunya da Abu Abdullahi.
.
Asalinsa Mutumin Asbahan ne ta kasar Farisa. Ya sami labarin za a aiko Annabi [SAW], sai yayi shiri ya fita nemansa, domin ya kasance cikin wadanda suka yi Imani dashi.
.
A hanya ne wasu suka sayar dashi a matsayin Bawa, bayan tsananin wahala da yasha har yazo Madina.
Ya sadu da Annabi [SAW] daf da lokacin yakin khandak, ya halarci yakin, shine ya bawa Annabi [SAW] shawarar a haka ramin gwalalo domin hana kafirai haurowa su shigo Madina.
.
Ya halarci dukkan yakokin da suka biyo bayan Khandak. Khalifa Umar [RA] yanada shi Gwamnan Birnin Mada'in.
.
Abu Burdah ya ruwaito daga Baban sa cewa, Annabi[SAW] ya ce,
.
" Lallai Allah yanason mutum 4 daga Sahabbai na daga cikin su akwai Salmanu".
.
Mutum ne shi mai tsananin tsoron Allah da gudun duniya da kaifin kwakwalwa, tsantseninsa kuwa ana kwatantashi da Khalifa Umar [RA].
.
Allah yakara masa yarda da aminci.





Koma saman shafi

→Labarai

HASSADA MUGUN CIWO, ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA,(Imam Aliyu Indabawa)

HASSADA MUGUN CIWO, ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA,(Imam Aliyu Indabawa)
.
Wannan da kuke gani shine Dr kalifa qaribullah nasiru kabara, wanda ya kasance shine halifan dariqar qadiriyya, kuma muna girmama shi saboda halayensa na kawaici da sanin ya kamata, sai Allah ya jarrabe shi da wani taqadarin kani wanda ya addabe shi da hassada kullum cikin zaginsa yakeyi yana kushe shi yana aibata shi,
.
Asali abinda yasa yake masa wannan hassadar shine saboda halifa qaribullahi Allah yayi masa ni'imomi da baiwarwaki wanda shi kanin nasa bashi dasu, yafi shi duk wani abu da ake so, ta bangaren daukaka, da Ilmi da 'yaya da kudi da magoya baya da manyan mutane Sarakuna, uwa uba kuma yana da hankali wanda shi kanin nasa yayi rashinsa,
.
Sannan ga mukamin Halifa da yake rike dashi wanda shine yafi komai kona masa zuciya da motsa masa hassada, saboda shi a tunaninsa ai shine yafi cancanta daya gaji mahaifinsa ya zama halifan qadiriya saboda tunaninsa wai yafi Qaribu Ilmi shine yasa ya dade yana zagin Halifa karibu yana cutar da shi ta ko'ina yana nuna hassadarsa gare shi, dayake dama hassada ga mai rabo taki ce, shi kuma halifa Qaribu kullum sai kara gaba yakeyi har wasu kashashen ma suna bashi lambar yabo ta girmamawa amman duk da haka har yanzu Abdun jabberun yaki ya gane,
.
Ku duba Ko A haife qaribu ya haifi Audujanbiri amman saboda tantiranci da rashin tarbiya babu irin zagin da bayayi masa akwai Lokacin Audu janbiri yace,"qaribu wai babarsa da cikinsa ta shigo gidan malam wai qaribu ba dan malam bane wai shege ne kuma a duba dashi qaribun dashi Audu janbirin waye yake kama da malam kabara, kuma wai a cikin taron daruruwan mutane yayi wannan maganar, ba wannan kadai ba da dai sauran maganganu masu muni wanda shi kuma qaribun dayake yasan kanin nasa yana da ragaggen hankali baya biye ta tashi kullum hakuri yake dashi, lokacin da magoya bayan qaribu suka ga abin nasa fa ya wuce tunani ya koma tsantsar iskanci da rashin mutunci sai sukace suma dai dai suke da dan iska, inda duk lokacin da yazo wani taro ko maukibi sai suki su barshi ya shiga idan ma ya shigo sai su jefe shaidani, haka suka dinga yiwa dan banza daga karshe dayaga uwar bari da kansa yaje ya bawa halifa Qaribu hakuri akayi salhu tun daga lokacin abu ya danyi shiru,
.
Sai yanzu ya tsiro da wani iskancin, yana zagin Halifa qaribullah, dama tun asali kasancewarsa mutum mai neman Suna kota halin qaqa, amman hakan yaki samuwa yasa yake cin zarafi da cin mutuncin mutane sai kaji shi yana zagin babban malami wanda ya haife ya haife shi,
.
haka ya koma ta6o 'yan siyasa wanda duk gomnatin da take kai to sai yayi ta zaginta kenan har sai an bashi wani abun, misali lokacin mulkin kwankwaso na farko haka ya dinga bi yana zagin kwankwaso har sai da kwankwaso ya bashi fili a gwale filin mushe, wanda yanzu haka a cikin filin yayi gidansa yayi masallacin juma'a filin ma hakkin mutane, lokacin da kwankwaso ya tafi shekarau yazo sai ya koma 6angaren shekarau yana masa jagaliya da yaga shekarau baya bukatar tafiya da 'yan jagaliya irinsu sai ya dinga zagin shekarau har yake cewa idan yabi shekarau to shi dan zina ne, ana nan sai malam shekarau yayi masa wani babban Alkhairi wanda ya fito yace duk duniya ibrahim masu girma guda uku ne, da Annabi ibrahim da ibrahim inyass da ibrahim shekarau, lokacin da kwankwaso ya dawo be tafi dashi ba sai ya koma zagin kwankwaso ko lokacin da kwankwaso ya ta6a Annabi S.A.W sai ya dinga zagin kwankwaso har yace dashi ya zama kafiri, haka ya tara mutanensa har ya dauki sulke da kwalkwali ya saka a jikinsa , ya umarci 'yan jagaliyar yaransa suka rike makamai suka fito gari suna zanga zanga, amman yadda zakasan munafiki ne sai gashi lokacin da yake wa 'yan tijjaniya raddi yana siffanta Muhammadu Rabi'u kwankwaso da mai kishin musulunci,
.
Ba 'yan siyasa kadai ba, tuntuni shine yau ya ta6o 'yan izala gobe kaji ya ta6o 'yan tijjaniyya jibi ya ta6o 'yan qadiriya ko wani malami wanda bashi da dariqa, tun mutane suna biye masa har suka gane manufarsa suka gane cewa yana fama da ta6in hankali ta yaya zasu tsaya suna rigima da mahaukaci sai duk suka kyale karen yaje yayi ta haushinsa shi kadai, daya ga haka sai ya canza dabara akan ya samu masoya wanda zai dinga damfararsu 'yan kudaden su, haka yayi ya dinga tara karatu da sunan kishin Annabi da soyayyarsa nan ko babu abinda yake koyawa sai jahilci da dure duren ashariya, Kunji AMIRUL FASIKINA HUJJATUL JAHILINA kenan,
.
Koda matasan suka fuskanci babu wata tsiya na karatu da ake karuwa da Abdun jabberun sai duk suka dinga watsewa suna karewa kamar hatsin guziri, daya fuskanci neman Sunan dayake har yanzu a kano ba'asan da wani Abdun jabberun ba, wanda ko a gwale filin mushe babu wanda yasan dashi, kuma gashi na cefane yana gagararsa sai ya tsiro da wani iskanci da zindikanci na zagin sahabban Annabi inda yaje ya kar6o kwangilar kudi wajen Iro jakin zariya L.A don ya samu magoya baya, lokacin daya fara zagin sahabbai irinsu sayyadi Mu'awiya A,S yana kawo hadisai ta karfin tuwo yana juya musu ma'ana malaman Sunnah sun zabura suna mayar masa da raddi wanda shi dama abinda yake so kenan ayi ta zancensa yayi suna a san dashi, bayan lokacin da malam Alqasim yayi buji buji dashi akan littafinsa muqaddimatul Khaziba, haka aka dinga fama dashi akan yazo a zauna ayi muqabala akan wannan mas'alar ta fi'atul bagiya, amman hakan yaki yuyuwa kullum ya zauna sai dai dure duren ashariya da tsine tsine da karya da cika baki da alfhari da ihu da kowayee, a haka yanzu zindiqancin nasa da iskancin nasa har yazo ya fara zaginsu sayyadi Abubakar yana karyatashi akan hadisin gadon Annabi, yana zagin sayyadi usman akan wai azzalumi ne a lokacin mulkinsa, yanzu da malaman Sunna suka gane cewar bamagujen dan shi'ar yanada ta6in hankali sai duk suka kyale shi, don idan banda me ta6in hankali babu wanda zai dinga zagin sahabbai yana tuhumarsu,
.
To sai rannan mai tatsinen a wani shirmen sa dayake yi wai da sunan karatu yana karanto wani soki burutsun littafinsa mai suna MUQADDIMATUL KHAZIBAH babi mai taken LA TASABBU AS'HABI sai yazo maganar akan wani Hadisi da Halifa Qaribullah ya rawaito akan Sayyadi Ali inda ya dinga ciwa halifa Qaribullah mutunci yana fada masa maganganu na 6atanci yana cewa zasu 6ata dashi akan imami, ba don komai yake haka ba wai don kawai halifa shi yana girmama sahabban Annabi baya zaginsu sannan yana fadar gaskiya a duk inda ta dace, ko a wani haukan karatun Amirul jahilina na baya naji wai har yana cewa wai qaribu yayi maja da 'yan izala yana kiransa da nasibi,
.
To janbiri idan ma izalar qaribu ya koma ai ya gano itace gaskiya ne, tunda gaskiya yake bi, kuma kowa yayi shaidar cewa qaribu malami ne me koyar da karatu wanda yakanyi tafsiri a gidan sarki, sannan a ranaku yakan karanta sahih muslim da Algunya da ishreniyya, ba kamar ka ba wanda babu abinda ka iya sai dai ka tara mutane kayi ta dura ashariya kana tsine tsine kana sheka karya kana hauka suna ihu kana koya musu ta'addanci kana cewa su dauki makamai suje masallacin da akai rikici a baya su kashe 'yan izala, kai saboda ci da qarfi irin na mai mai tatsine sai kaje ka rubuto hadisai da ayoyi kazo kayi ta karantasu da kyar kana kuskure a cikin ayoyin, mutumin da ko haddar simini daya bashi da ita a Qur'ani, kai ko Ayar Muhammadur rasulillah ma daya karanto akwai kusa kurai a cikinta, kai Abduljbbar wallahi jahili ne na karshe, na tabbata ko fatiha ma idan zai karanta sai an ci gyaransa, ayar suratul ma'ida IN TU AZZIBHUM FA INNAHUM IBADUK WA IN TAGFIR LAHUM FA INNAKA ANTAL AZIZUL HAKIM duk da rubuto ayar yayi amman shi jahilin sai cewa yayi FA INNAKA ANTAL GAFURUR RAHIM haka farkon raddinsa ga 'yan tijjaniya yace" ALLAZINA HUM IZA ASABATHUM sai ya sake cewa" ALLAZINA IZA ASABSATUM.. Kunji chakwakiya fa, haka a wani karatunsa yana karanta tarihin matan Annabi S.A.W wai ayar da take suratul Ahzab tana gargadi ga Matan Annabi itace" INKUNTUNNA TURIDNAL HAYATUD DUNYA WAZINATAHA FATA A LAINA UMATTI U KUNNA WA USARRIH KUNNA amman jahilin wai sai yace." FATA A LAINI UDALLIQUKUNNA WA USARRIH KUNNA, kuji jahili wanda beyi karatun Qur'ani ba, sannan ayar ta suratu Ahbaz yazo kan kissar Zainab da zaid ayar itace WAMA KANA LI MU'UMINUN WALA MU'UMINATUN IZA QADALLAHU WARA SULUHU AMRAN AY YAKUNA LAHUMUL KIYARATU MIN AM RIHIM WAYAY YA'ASILLAH WARA SULAHU FAQAD DALLA DALALAN MUBINA amman kasgin jahilin sai yace" FAQAD DALLA DALALAN BA'IDA kunji jahili wanda beyi karatun qur'ani ba. Idan nace zan dinga kawo kuskuren wannan hanfefen sai na kawo sunfi hamsin, don ko aya daya bazai iya ba ammn ya dinga wa Qur'ani Hawan qawara.
.
To wai wannan kuhungun jahilin kasgi, wai a fadar wasu wawayen shine malami kuma wai hanferen shine jagoransu, kai godiya ta tabbata ga Allah daya saka mabiya wannan zindiqin suka kasance wawaye mahaukata, tabbas kamar yadda suke fada na yarda Amirul jahilina shine mujaddadin wawaye na wannan zamani.
.
Abdun jabbarun sai dai kayi hakuri, na gaba yayi gaba na baya sai labari, halifa qaribullah yayi maka nisan da har abada bazaka ta6a kamo koda farcensa saba, sai dai ka cigaba da haukanka da zagin nasa idan bakayi wasa ba hassada itace zata sheke ka har lahira, kuma ko shi Halifa Qaribun yasan kanada matsalar kwakwalwa, wanda ya kamata yasan yadda za'ayi a kaika dawanau tun kafin haukan naka yakai ka fara zagin annabawa kana tuhumarsu, abduljabbar nidai ina maka Addu'ar Allah ya baka lafiya ya rabaka da wannan cutar ta ta6in hankali da take damunka, su kuma jahilan da suke biye maka. Allah ya ganar dasu su fara zuwa makaranta suy karatu, don babu wani mai ilmi da hankalin da zai dauki wannan galmashoran mai dure duren ashariya da zagin sahabban Annabi wai da sunan malami.
.
Tofah dama ance duk yadda akai da jaki dai yaci kara, yanzu gaskiyar nan dana fada fa sai ka samu wasu jakunan sun fara tunkuyi koh? To jakunan kogo ayi ta tunkuyi lafiya, nidai babu jakin daya isa ya tunkuye ni na juya nace zan rama, ko shi kansa babban jakin naku na kogo be isa balle wasu karnukan farauta, saboda haka 'ya'yan mutu'a. Karnukan farauta haihuwar mutu'a kuy ta haushi lafiya.
.
Har yau dai
.
Angom Fatima ne Abban Sadiq
.
I.A.I

Back to posts
Comments:
[2016-02-24 21:46:57] Moh'd B. Ussaini :

To Maza Kaje Ka Tuba Domin Kayi Karya Gami Da Hahilci Bataimiye

[2016-07-01 22:33:04] ANAS AMEEN :

ALLAH YA SAWAKE AMEEN.

[2016-05-12 19:18:42] ummu aisha :

SLM

[2016-07-24 20:41:23] Aminu Rabiu Garun Gudinya Babura :

Ya Allah kaganar damu gaskiya katseratar da diga diganmu daga saba maka amin

[2016-07-30 18:45:55] MHD SANI :

Allah yasaka wa abduljabbar anyi masa kage kuma baze yafeba

[2016-09-17 05:21:32] ibrahimaliyusumaila@gmail.com :

kai arasa wanda za aiwa sharri sai abduljabbar

[2016-08-28 22:57:17] Shamsuddeen lawal anchau :

Tofa!

[2018-02-07 15:24:04] Zaharaddeen m.abubakar deen :

to allah yaimana jagora amin mudai sunnah sak.


UNDER MAINTENANCE

Share|

Kaima shiga a tattauna da kai
* No boards.

Online: Guests: 1


→Ra'ayin jama'a game damu

 IDAN KANA BUKATAR A TALLATA MAKA HAJAR KA A WANNAN SHAFIN DA SAURAN SHAFUKAN MU KANA IYA TUNTUBAR MU TA WADANNAN HANYOYIN KAMAR HAKA:


Email: bjournalist55@hotmail.com

Phone No: 09035830253

Facebook: Basheer Journalist Sharfadi

Address: Ittihad Computer Centre,  No 92 Daneji Kano


MAI TALLA SHI KE DA RIBA


*Bayanan ka*
Browser din da ka hawo Mozilla

Kasar da kake

Adadin Maziyarta 317406

Adadin Wadanda Sukayi Comment 65691

A Wadanda Suka Shiga Tattaunawar Mu 54


Follow @bjournalist55
→Yi Adding Dina Ta Facebook
→Yi Like Na Dakarun Sunnah Page
→Yi Like Dina Ta Facebook

*Shafuka Masu Alaka Da Mu*

→Basheer Sharfadi wordpress
Basheer Sharfadi Blog Spot
UP
→Home

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah)
ISLAMIC DATE
  • phpimg2.php?it&ic=yellow



  • Click to Sms
    Click to Call


    Basheer journalist sharfadi3
    Coollogo com-1281358