Google69490f6862051cb8
google-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlBasheer journalist sharfadi14

Basheer journalist sharfadi14.jpg6
Basheer journalist sharfadi 11 1
Maraba Da Zuwa Wannan
Shafi Mai Al-barka 1

☀ Zabi inda kake son shiga ☀
Menunks
→Home
→Akidojin Ahlussunnah
→Addinin musulunci (35)
→40 Hadith (50)
→Fadakarwa (120)
→Neman labarai (20)
→Shi'a Kafirci (50)
→Hadith (55)
→Khudubobi (24)
→Tarihin magabata (60)
→Raddi / Maida martani (99)
→Face book post (30)
→Monthly Archives (60)
→Tambaya da Amsa (20)
→Sahabban Annabi {s.aw} (50)
→Taskar maluman sunnah (25)
→Akidar Y'an Shi'a Dangane da Al'kur'ani
→Fassarar Usulussunnah (20)
→Sheik Ja'afar {Rahimahullah} (65)
→Sheik Abubakar Gumi {Rahimahullah} (30)
→Sheik Dr. Muhammad Sani R/Lemo
→Salafiyyah Network Nigeria (100)
→Adam Sani Abu-Umayrah (99)
→Salaf Ustaz (79)
→Malama Ummi Ahmad Katsina
→Malama Amina Saleh Mande
→Labarai (40)
→Nishadantarwa (10)
→Siyasar Nigeria (9)
→Vidio (33)
→Audio (66)
→Hotuna (120)
→Internet Cheat (90)
→Site Achieve
→Application (10)
→Games (8)
→About me (01)

Wannan shafin mallakarCoollogo com-1281358 3
Ne




SHAFI DON KARUWAR MUSULMI
Fassarar littafin
*** Usulus sunnah ***
Na
Imam Ahmad Bin Hambal
Shirin da dan uwanku
Abu Jareer Ameer bn Hamza Zakigold
Yake GabatarwaKuna iya binsa ta face book
Wanda ya tsara kuma ya shirya
Basheer journalist sharfadi (Abu Hafsat)
A sha karatu lapiya

FASSARAN USULUS SUNNAH NA IMAM AHMAD BIN HANBALI
.
Darasina 1
.
Dasunan ALLAH mai Rahma maijin Kai, tsira da aminci sukara tabbata ga shugaban duk wani Ahlussunnah, abin kaunarsa kuma abin koyinsa Annabi Muhammad s.a.w da iyalan gidansa da almajiransa da duk wanda yabiyo bayansu da kyautatawa.
.
bayan haka muna fatan ALLAH ya daidaita tinaninmu da fahimtarmu ya datar damu gaskiya kuma ya bamu ikon aiki da abinda zamu karanta.
.
Mallam yace:- Abdus dan Malik ya labartamin cewa: yaji baban Abdullah wato Ahmad dan Muhammad dan Hanbali(ALLAH yamasa Rahma) yanacewa:-
.
Asali/ginshikai na Sunnah awajenmu:
.
1-Riko da/Bin abinda sahabban manzon ALLAH s.a.w suke kai(cikin addini)
.
2-Yin koyi dasu(sahabbai). kenan duk mai daawar shi Ahlussunnahne to muganshi yana koyi da sahabban Annabinmu s.a.w.
.
3-Barin aikata bidi'ah(kowace irice).
.
4-Dukkanin bidi'a batace.kai Alhamdulillah ashe karyane kawai akema shehul Islam na cewa wai shine yafara daurama dalibai fahimtar hakan.
.
5-Barin husuma dakuma zama tareda ma'abota son rai(yan bidi'a).
.
6- Barin Jayayya, kace nace, musu cikin Addini (kalubale gareku yan uwana Ahlussunnah).
.
.
zamu kwana anan sai in ALLAH yakaimu darasi nagaba.
.
.
FADAKARWA: Isnadin da muka kawo na wannan littafin ba shikai bane mun zabeshine kawai don takaita Rubutu, amma wannan Littafi an ruwaitotane ta hanyoyi tara, maison dubawa saiya nemi bugun Maktabatu ibn Taimiyya wanda ke Misra, tahqiqin Walid bin Saif Annasr.
.
.
Sannan duk wanda yaga gyara ko karin bayani zai iya tuntubana ta:-
.
hamzaameer236@gmail.­com,
hamzaameer708@gmail.­com,
zakigold16@ yahoo.com
.
.
Ko kayi mana comment ta nan


FASSARAN USULUS SUNNAH NA IMAM AHMAD DAN HANBALI
.
Wanda dan uwanku Abu Jareer Ameer bn Hamza Zakigold yake gabatarwa
.
Darasina Biyu:2
.
Dasunan ALLAH mai Rahma maijin Kai, tsira da aminci sukara tabbata ga shugaban duk wani Ahlussunnah, abin kaunarsa kuma abin koyinsa Annabi Muhammad s.a.w da iyalan gidansa da almajiransa da duk wanda yabiyo bayansu da kyautatawa.
.
bayan haka
.
muna fatan ALLAH ya daidaita tinaninmu da fahimtarmu ya datar damu gaskiya kuma ya bamu ikon aiki da abinda zamu karanta.
.
Inbamu mantaba wancan makon daya gabata mun tsayane agaba ta shida yau zamu tashi ana Bakwai, Mallam yace:
.
7-Sunnah awajenmu: sune Hadisan Annabi s.a.w.
.
8-kuma su Hadisan suna fassara Qur'ani, domin sudin dalilaine/hujjojine na alqur'ani..
.
9-Babu kiyasi cikin sunnah. anan wurin sunnah yana nufin Tauhidine ba rassa na fiqhuba kamar yanda Shehul Fauzan a fassara irin wannan gaba a Sharhus sunnah na Imamul Barbahari, haka shima Sheikh Ahmad dan Yahaya Annajami ya fassara wannan gaba a littafinsa
"Irshadu sari fi sharhu sunnah lilbarbahari".
.
10-Ita Sunnah(Tauhidi/­aqida) baa buga mata misali(wato bada misalai ake tabbatar da itaba), baa riskanta da hankali ko son rai(ba kawai abinda yai dai-dai da hankalinka shine zaka yarda dashiba), ita Sunnah ba wata aikine saboba face bi(wato bin Qur'ani da Hadisan Annabi s.a.w bisa fahimtar sahabbansa da wadanda suka biyo tafarki irintasu) da barin son zuciya.
.
.
zamu kwana anan, sai in ALLAH yabamu aron rai zuwa darasi na gaba,
.
ya ALLAH ka kara Tsira Aminci Ni'ima ga shugabanmu Annabi Muhammad s.a.w
.
Via:- Haqqin ALLAH AKAN Bayinsa
.
https://­m.facebook.com/­HaqqinAllahAkanBayins­a


FASSARAN USULUSSUNNAH NA IMAM AHMAD DAN HANBALI
.
Darasi na uku
.
11-Mallam yace: yana daga cikin Sunnoni wajibai wadanda duk wanda yabar wani abu daga ciki(bai yarda dashiba), kuma baiyi imani dashiba, to wannan ba Ahlussunnah bane(sune tindaga gaba na 12 harzuwa na 50):
.
12-Imani da kaddara na alhairi kona sharri, da gasgata Hadisanda suke bayani gameda Kaddaran, da sallama mata/yarda da ita, kuma kada kace: don me?(misali donme Allah ya halicci kaza da kaza?), kuma kada kace: ya akayi? abinda ake bukata kawai gasgatawa dakuma imani da ita(Kaddaran). Duk wanda baisan fassaran Hadisiba amma malamai sukamasa bayani ta littafan fiqhu to wannan ya isheshi kuma za'amar hukunci da abinda ya karanta, dolene yayi Imani da Hadisin dakuma duk abinda ya kunsa kuma ya Sallamawa bayanin magabata akai, misali: Hadisin(Ibn Mas'ud radiyallahu anhu, da Annabi s.a.w yakecewa: lallai dayanku ana tattara halittansa cikin cikin mahaifiyarsa kwana arba'in yana maniyi, harzuwa karken hadisin duba Buhari(3208) da Muslim(2643) da dai sauran Hadisanda suke magana akan kaddara da Hadisanda suke magana gameda ganin Allah dukkansu dana Sunayen Allah dolene ayi Imani dasu kuma kada ayi musun koda harafi daya rak acikin duk Hadisin dayazo gameda hakan ta hanyar Amintattu.
.
kuma kada kayi jayayya da kowa cikin lamarin kaddara hakama kada kayi gogaiyya da kowa, kuma kada ka koyi musu domin musu gameda Kaddara da Kur'ani da makamantansu suna daga ababen ki wadanda aka hana, duk mai aikata haka baya dacewa da Sunnah idan kuma ya dace da Sunnah to dole saiyabar musu da jayayya ya sallama kuma ya yarda da duk ababenda suka inganta.
.
zamu kwana anan, sai in ALLAH yabamu aron rai zuwa darasi na gaba,
.
ya ALLAH ka kara Tsira Aminci Ni'ima ga shugabanmu Annabi Muhammad s.a.w
.
Via:- Haqqin ALLAH AKAN Bayinsa https://­m.facebook.com/­HaqqinAllahAkanBayins­a


FASSARAN USULUSSUNNAH NA IMAM AHMAD DAN HANBALI

.Darasi na Hudu

13-Alkur'ani maganan ALLAHne ba halittansa bane, bawani abune saboba don ance Kur'ani ba hallitta bane, mallam yace: domin shi maganar ALLAH(Kur'ani) babu wani abu aciki daya nuna cewa Kur'ani halittane, ballantana daman ba halittan bane.

Ahir dinku daduk wanda ya kirkira magana ya jinginama Kur'ani koda da lafazine(kalma daya tak) ko makamancin hakan, duk wanda ya tsaya musu gameda Kur'ani yace: bansaniba halittane koba halittaba, ammadai maganan ALLAHne to wannan shima dan Bidi'ane, dai-dai yake da wanda yace: Kur'ani halittane.

Abin sanidai Kur'ani maganan ALLAHne ba halittansaba.

zamu kwana nan, sai in ALLAH yabamu aron rai zuwa darasi na gaba,

ya ALLAH ka kara Tsira da Aminci Ni'ima ga shugabanmu Annabi Muhammad s.a.w

Via:- Haqqin ALLAH AKAN Bayinsa https://­m.facebook.com/­HaqqinAllahAkanBayins­a


FASSARAN USULUSSUNNAH NA IMAM AHMAD DAN HANBALI
.
.Darasi na Biyar
.
14:-Ahlussunnah sunyi Imani za aga Allah ranar Alkiyama kamar yanda yazo a Hadisai ingantattu.
15:- kuma lallai Annabi s.a.w yaga ubangijinsa, haka aka ruwaito daga Annabi s.a.w ta hanya ingantacciya, Qatada ya ruwaito daga Ikrama daga dan Abbas, dakuma Hakamu ta hanyar Aban daga Ikrama daga dan Abbas. Haka shima Aliyu bin Zaid ya ruwaito daga Yusuf dan Mihran, daga dan Abbas. Hadisin awajenmu yananan a bisa zahirinsa kamar yanda yazo daga Annabi s.a.w, magana game dashi(Hadisin) Bidi'ane, sai dai mu munyi Imanine dashi azahirin yanda hadisin yazo bama gogaiya dakowa cikin hakan.
.
FADAKARWA GAMEDA WANNAN GABAN NA SHABIYAR
Anan mallam yana nufin Annabi s.a.w yaga Ubangijine da zuciyarsa bada Idanunsaba, saboda babu wani baya dazai iya ganin ubangijinsa anan Duniya sai dai inya mutu kamar yanda Annabi s.a.w yafada: (ku sani babu wani cikinku dazaiga Ubangijinsa har sai inya mutu), kamar yanda shima Annabin s.a.w baiga Allahba da idanunsa kamar yanda Abu zar ya tambayeshi sai yace: (Haske nagani) awata ruwayar kuma yace Haskene nagani. Dukkanin Hadisan Imam Muslim ya ruwaitosu, atakaice dai baa ganin Allah aduniya sai a Lahira amma akan iya ganinsa cikin Mafarki kamar yanda Annabi s.a.w yabada labari amma ganinsa a Duniya a farke bashi yiwuwa sai a Lahira kamar yanda Hadisai suka nuna Muminai zasu gansa hakama yan Aljanna acikin Aljanna, wannan shine Ijimain Ahlussunnah wal Jamaa.
.
zamu kwana nan, sai in ALLAH yabamu aron rai zuwa darasi na gaba,
.
ya ALLAH ka kara Tsira da Aminci Ni'ima ga shugabanmu Annabi Muhammad s.a.w
.
Via:- Haqqin ALLAH AKAN Bayinsa https://­m.facebook.com/­HaqqinAllahAkanBayins­a


FASSARAN USULUSSUNNAH NA IMAM AHMAD
DAN HANBALI
.
Darasi na shida
.
Mallam yaci gaba da jero mana Aqidun Ahlussunnah kamar haka:
.
16- Duk Ahlussunnah waljamaah sunyi Imani da zaa auna aiyukan bayi ranar Kiyama, kamar yadda Hadisi ya tabbata Annabi s.a.w yace za'a auna aikinbawa ranar kiyama, saikaga ko nauyin fiffiken saura aikin bai kaiba. Buhari
4729, Muslim 2785. Kamar dai yanda ya tabbata a Hadisai da dama, Mallam yace Imani
da hakan wajibine da yarda dahakan, da kaucema duk wani wanda yai musun hakan,
da barin jayayya dashi duk wajibine.
17- Kuma lallai Allah madaukakin sarki zaiyi magana da Bayinsa ranar kiyama batare da wani mai fassaraba a tsakani, munyi Imani
kuma mun gasgata hakan.
18-Munyi Imani da tafkin alkausara, lallai Annabi s.a.w yana tafki ta musamman aranar
kiyama zaa bijiro da al-ummansa zuwaga tafkin, fadinsa tafiyan wata gudane hakama tsawonsa, yanada kwazazzabai kamar adadin taurarin sama kamar yadda Hadisai ingantattu suka tabbatar ta hanyoyi masu yawa.
.
zamu kwana nan, sai in ALLAH yabamu aron rai zuwa darasi na gaba,
.
ya ALLAH ka kara Tsira da Aminci Ni'ima ga
shugabanmu Annabi Muhammad s.a.w
.
Kuziyarcemu ashafinmu mai suna Haqqin
.
ALLAH AKAN Bayinsa https://m.facebook.com/­HaqqinAllahAkanBayinsa


FASSARAN LITTAFIN USULUS SUNNAH NA IMAMU AHMAD DAN HANBALI
.
Bugun Maktabatu Ibn Taimiyyah dake Misra.
.
Daga shafin Haqqin ALLAH AKAN Bayinsa
.
Darasi na bakwai
.
Mallam yacigaba da jero mana Akidu na Ahlussunnah wadanda suke yarda dasu wajibine kuma duk wanda yayi musu ko yaki wani abu daga ciki toba Ahlussunnah bane, mallam yajera mana gabobi goma sha takwas a baya yanxu zamu tashi ana sha tara.
.
19-Yin Imani da Azabar kabari.
.
20- Lallai wannan Al-umma ta Annabi s.a.w zaa fitineta acikin kabarinta, zaa mata tambaya danganeda Imani, da Muslunci, dakuma waye Ubangijinta? Dakuma waye Annabinta? Munkarun da Nakirun zasu zo ta yadda Allah s.w yaso dakuma yanda yanufa, imani da gasgata hakan wajibine ga duk wani Ahlussunnah.
.
Zan dakata anan sai nasake samun lokaci, danna wannan blue din kai like din page dinmu Haqqin ALLAH AKAN Bayinsa­


FASSARAN LITTAFIN USULUS SUNNAH NA IMAMU AHMAD DAN HANBALI
.
Bugun Maktabatu Ibn Taimiyyah dake Misra.
.
Darasi na Takwas

adarasinmu na baya mun tsaya a gaba na Ashirin cikin jeren Akidu na Ahlussunnah wal jamaah wadanda suke dolene yin Imani dasu dakuma gasgatasu kuma duk wanda kaga yana MUSUN dayansu toba Ahlussunnah bane, yau zamu tashi a gaba na Ashirin da daya
.
21- YIN IMANI DA CETON ANNABI S.A.W,dakuma cetonsa ga wasu Mutane da za'a fitar dasu daga Wuta bayan sun konu sun zama Toka, yayinda za'a Umurcesu zuwa wata korama a Kofar Aljannah kamar yadda ya tabbata a Hadisi, ta yanda Allah kuma yaga dama, mudai munyi Imani kuma mun gasgata.
.
22- Dayin Imani cewa Dajjal mai shafaffen Albarka zai fito, an rubuta a tsakanin Idanuwansa KAFIRUN, kamar yanda Hadisai suka tabbar, dolene yin Imani cewa hakan zai faru.
.
23- Kuma lallai Annabi Isa dan Maryam s.a.w zai sauko(daga sama) yakashe Dujjal a kofar Luddin.
.
Zamuci gaba da yardan ALLAH da Amincewarsa
.
ku ziyarcemu a wannan shafin:
Haqqin ALLAH AKAN Bayinsa­
Haqqin ALLAH AKAN Bayinsa­
Haqqin ALLAH AKAN Bayinsa­
Haqqin ALLAH AKAN Bayinsa­
Haqqin ALLAH AKAN Bayinsa­ Haqqin ALLAH AKAN Bayinsa­ Haqqin ALLAH AKAN Bayinsa­


FASSARAN LITTAFIN USULUS SUNNAH NA IMAM AHMAD DAN HANBALI
.
Bugun Maktabatu Ibni Taimiyya dake Misra
,
DARASI NA TARA//009
,
Inbamu mantaba a darasi na takwas mun tsayane a gaba 23 cikin jerin Aqidun Ahlussunnah wadanda suke dolene yin Imani dasu, yau zamu tashi ana 24.
.
24- Imani furucine da akeyi da Baki dakuma Aiki na gabobi, Imani yana raguwa yana karuwa, kamar yanda Hadisi ya tabbata Annabi s.a.w yace: ((Mumininda Imaninsa yacika shine wanda yake kyautata dabi'a)) Sahihul Jami'i 1230.
.
25-Duk wanda yabar Sallah hakika tabbas ya kafirta, babu wani aiki wanda barinsa kafircine bayan Sallah, duk wanda yabarta kafirine, hakika Allah ya halasta kasheshi.
.
Zamu tsaya haka sai darassi na gaba in Allah ya bamu aron rai, subhanallahumma wabihamdika ashhadu anlailaha illa huwa astagfiruka waatubu ilaik,


FASSARAR USULUS SUNNAH NA IMAMU AHMAD BIN HANBAL
DARASI NA //10

A yau zamu tashi agaba na ashirin da shida kicin aqidun ahlussunnah wadanda imani dasu wajibine.

26: Mafificin wannan Al-ummah bayan Annabinta shine Abubakar sadiq, sannan UMARU dan Haddabi sannan Usman dan Affan, Imam Ahmad hace muna gabatarda wadannan ukunne Kalmar yadda SAHABBAN ANNABI S.A.W suka gabatar dasu, basuyi savaniba.
Sannan bay an wadannan ukun, Ashabu shura su Bihar: Aliyu dan Abi Dalib, da Dalha, Zubair, da Abdulrahman dan Auf, da Sa'ad, dukkanninsu sun can canci Halifanci, kuma dukkaninsu jagororine.

Mina hujjane da Hadisin dan Umar(mun kasance muna kididdigewa alhalin Annabi s.a.w yana Raye kuma sahabbansa suna Raye, muna cewa Abubakar sannan Umar sannan Usman, said muyi shiru). Cuba musnad hadisi na 4612, Buhari 3655.

Sannan bayan Ashabus shura: wadanda suka halarci yakin Bandar cikin muhajirai, sannan wadanda suka halarci Bandar cikin mutanen madina cikin sahabbab Annabi s.a.w qwarqwadon hijira dakuma wadanda suka rigayi, mataki-mataki.

27:Sannan mafifitan mutane bayan wadannan sune: sahabban Annabi s.a.w wadanda aka aikoshi acikinsu, Wanda ya tattara dukwani Wanda ya zauna dashI name tsawon shekara ko wata days, ko yini guda ko awa guda koya ganshi yana mai Imani dashi to yana saga cikin sahabbansa, dukkanin wadannan sahabbaine kowanne gwargwadon zamansa da Annabi s.a.w da gwargwadon yanda yaji daga gareshi dakuma yanda ya ganshi.

mafi kasa kasa amatsayi cikin sahabbai yafi duk wata al-umma da bataga Annabiba falala koda wannan al-umma tazo da duck wani aiki na alhairi.

Alhamdulillah ya Allah kabamu ikon koyi dasu


FASSARAN LITTAFIN USULUS SUNNAH NA IMAM AHMAD DAN HANBALI

Darasi na //011

A darasi na goma mun tsayane a gaba na ashirin da bakwai ciki jerin akidoji dasuka zama wajibi gaduk wani Ahlussunnah yai imani dasu kuma ya yardu dasu Kalmar yanda Imamu Ahlussunnati waljamaa ya ambata, agurguje zamu tashi gaba na 28.

28-Da sauraro tareda biyayya ga jagorori dakuma shugaba acikin addini,wannan shugaban yakasance mai yima Allah biyayyane koko mai bijirema dokokinsane, Halifaneshi da jamaa suka zaba suka yarda dashi koko juyin mulki yayi yake mulkansu da karfin tuwo, yimasa biyayya wajibine.

29-Kai hari da yake-yake tareda shuwagabanni na Addini yananan har tashin kiyama akan Mumini da fajiri-baa dainawa.

Ya Allah kasanyamu cikin Ahlussunnah wall jamaa kabamu ikon aiki da sunnah, Amiin



Koma saman shafi

→Labarai

HASSADA MUGUN CIWO, ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA,(Imam Aliyu Indabawa)

HASSADA MUGUN CIWO, ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA,(Imam Aliyu Indabawa)
.
Wannan da kuke gani shine Dr kalifa qaribullah nasiru kabara, wanda ya kasance shine halifan dariqar qadiriyya, kuma muna girmama shi saboda halayensa na kawaici da sanin ya kamata, sai Allah ya jarrabe shi da wani taqadarin kani wanda ya addabe shi da hassada kullum cikin zaginsa yakeyi yana kushe shi yana aibata shi,
.
Asali abinda yasa yake masa wannan hassadar shine saboda halifa qaribullahi Allah yayi masa ni'imomi da baiwarwaki wanda shi kanin nasa bashi dasu, yafi shi duk wani abu da ake so, ta bangaren daukaka, da Ilmi da 'yaya da kudi da magoya baya da manyan mutane Sarakuna, uwa uba kuma yana da hankali wanda shi kanin nasa yayi rashinsa,
.
Sannan ga mukamin Halifa da yake rike dashi wanda shine yafi komai kona masa zuciya da motsa masa hassada, saboda shi a tunaninsa ai shine yafi cancanta daya gaji mahaifinsa ya zama halifan qadiriya saboda tunaninsa wai yafi Qaribu Ilmi shine yasa ya dade yana zagin Halifa karibu yana cutar da shi ta ko'ina yana nuna hassadarsa gare shi, dayake dama hassada ga mai rabo taki ce, shi kuma halifa Qaribu kullum sai kara gaba yakeyi har wasu kashashen ma suna bashi lambar yabo ta girmamawa amman duk da haka har yanzu Abdun jabberun yaki ya gane,
.
Ku duba Ko A haife qaribu ya haifi Audujanbiri amman saboda tantiranci da rashin tarbiya babu irin zagin da bayayi masa akwai Lokacin Audu janbiri yace,"qaribu wai babarsa da cikinsa ta shigo gidan malam wai qaribu ba dan malam bane wai shege ne kuma a duba dashi qaribun dashi Audu janbirin waye yake kama da malam kabara, kuma wai a cikin taron daruruwan mutane yayi wannan maganar, ba wannan kadai ba da dai sauran maganganu masu muni wanda shi kuma qaribun dayake yasan kanin nasa yana da ragaggen hankali baya biye ta tashi kullum hakuri yake dashi, lokacin da magoya bayan qaribu suka ga abin nasa fa ya wuce tunani ya koma tsantsar iskanci da rashin mutunci sai sukace suma dai dai suke da dan iska, inda duk lokacin da yazo wani taro ko maukibi sai suki su barshi ya shiga idan ma ya shigo sai su jefe shaidani, haka suka dinga yiwa dan banza daga karshe dayaga uwar bari da kansa yaje ya bawa halifa Qaribu hakuri akayi salhu tun daga lokacin abu ya danyi shiru,
.
Sai yanzu ya tsiro da wani iskancin, yana zagin Halifa qaribullah, dama tun asali kasancewarsa mutum mai neman Suna kota halin qaqa, amman hakan yaki samuwa yasa yake cin zarafi da cin mutuncin mutane sai kaji shi yana zagin babban malami wanda ya haife ya haife shi,
.
haka ya koma ta6o 'yan siyasa wanda duk gomnatin da take kai to sai yayi ta zaginta kenan har sai an bashi wani abun, misali lokacin mulkin kwankwaso na farko haka ya dinga bi yana zagin kwankwaso har sai da kwankwaso ya bashi fili a gwale filin mushe, wanda yanzu haka a cikin filin yayi gidansa yayi masallacin juma'a filin ma hakkin mutane, lokacin da kwankwaso ya tafi shekarau yazo sai ya koma 6angaren shekarau yana masa jagaliya da yaga shekarau baya bukatar tafiya da 'yan jagaliya irinsu sai ya dinga zagin shekarau har yake cewa idan yabi shekarau to shi dan zina ne, ana nan sai malam shekarau yayi masa wani babban Alkhairi wanda ya fito yace duk duniya ibrahim masu girma guda uku ne, da Annabi ibrahim da ibrahim inyass da ibrahim shekarau, lokacin da kwankwaso ya dawo be tafi dashi ba sai ya koma zagin kwankwaso ko lokacin da kwankwaso ya ta6a Annabi S.A.W sai ya dinga zagin kwankwaso har yace dashi ya zama kafiri, haka ya tara mutanensa har ya dauki sulke da kwalkwali ya saka a jikinsa , ya umarci 'yan jagaliyar yaransa suka rike makamai suka fito gari suna zanga zanga, amman yadda zakasan munafiki ne sai gashi lokacin da yake wa 'yan tijjaniya raddi yana siffanta Muhammadu Rabi'u kwankwaso da mai kishin musulunci,
.
Ba 'yan siyasa kadai ba, tuntuni shine yau ya ta6o 'yan izala gobe kaji ya ta6o 'yan tijjaniyya jibi ya ta6o 'yan qadiriya ko wani malami wanda bashi da dariqa, tun mutane suna biye masa har suka gane manufarsa suka gane cewa yana fama da ta6in hankali ta yaya zasu tsaya suna rigima da mahaukaci sai duk suka kyale karen yaje yayi ta haushinsa shi kadai, daya ga haka sai ya canza dabara akan ya samu masoya wanda zai dinga damfararsu 'yan kudaden su, haka yayi ya dinga tara karatu da sunan kishin Annabi da soyayyarsa nan ko babu abinda yake koyawa sai jahilci da dure duren ashariya, Kunji AMIRUL FASIKINA HUJJATUL JAHILINA kenan,
.
Koda matasan suka fuskanci babu wata tsiya na karatu da ake karuwa da Abdun jabberun sai duk suka dinga watsewa suna karewa kamar hatsin guziri, daya fuskanci neman Sunan dayake har yanzu a kano ba'asan da wani Abdun jabberun ba, wanda ko a gwale filin mushe babu wanda yasan dashi, kuma gashi na cefane yana gagararsa sai ya tsiro da wani iskanci da zindikanci na zagin sahabban Annabi inda yaje ya kar6o kwangilar kudi wajen Iro jakin zariya L.A don ya samu magoya baya, lokacin daya fara zagin sahabbai irinsu sayyadi Mu'awiya A,S yana kawo hadisai ta karfin tuwo yana juya musu ma'ana malaman Sunnah sun zabura suna mayar masa da raddi wanda shi dama abinda yake so kenan ayi ta zancensa yayi suna a san dashi, bayan lokacin da malam Alqasim yayi buji buji dashi akan littafinsa muqaddimatul Khaziba, haka aka dinga fama dashi akan yazo a zauna ayi muqabala akan wannan mas'alar ta fi'atul bagiya, amman hakan yaki yuyuwa kullum ya zauna sai dai dure duren ashariya da tsine tsine da karya da cika baki da alfhari da ihu da kowayee, a haka yanzu zindiqancin nasa da iskancin nasa har yazo ya fara zaginsu sayyadi Abubakar yana karyatashi akan hadisin gadon Annabi, yana zagin sayyadi usman akan wai azzalumi ne a lokacin mulkinsa, yanzu da malaman Sunna suka gane cewar bamagujen dan shi'ar yanada ta6in hankali sai duk suka kyale shi, don idan banda me ta6in hankali babu wanda zai dinga zagin sahabbai yana tuhumarsu,
.
To sai rannan mai tatsinen a wani shirmen sa dayake yi wai da sunan karatu yana karanto wani soki burutsun littafinsa mai suna MUQADDIMATUL KHAZIBAH babi mai taken LA TASABBU AS'HABI sai yazo maganar akan wani Hadisi da Halifa Qaribullah ya rawaito akan Sayyadi Ali inda ya dinga ciwa halifa Qaribullah mutunci yana fada masa maganganu na 6atanci yana cewa zasu 6ata dashi akan imami, ba don komai yake haka ba wai don kawai halifa shi yana girmama sahabban Annabi baya zaginsu sannan yana fadar gaskiya a duk inda ta dace, ko a wani haukan karatun Amirul jahilina na baya naji wai har yana cewa wai qaribu yayi maja da 'yan izala yana kiransa da nasibi,
.
To janbiri idan ma izalar qaribu ya koma ai ya gano itace gaskiya ne, tunda gaskiya yake bi, kuma kowa yayi shaidar cewa qaribu malami ne me koyar da karatu wanda yakanyi tafsiri a gidan sarki, sannan a ranaku yakan karanta sahih muslim da Algunya da ishreniyya, ba kamar ka ba wanda babu abinda ka iya sai dai ka tara mutane kayi ta dura ashariya kana tsine tsine kana sheka karya kana hauka suna ihu kana koya musu ta'addanci kana cewa su dauki makamai suje masallacin da akai rikici a baya su kashe 'yan izala, kai saboda ci da qarfi irin na mai mai tatsine sai kaje ka rubuto hadisai da ayoyi kazo kayi ta karantasu da kyar kana kuskure a cikin ayoyin, mutumin da ko haddar simini daya bashi da ita a Qur'ani, kai ko Ayar Muhammadur rasulillah ma daya karanto akwai kusa kurai a cikinta, kai Abduljbbar wallahi jahili ne na karshe, na tabbata ko fatiha ma idan zai karanta sai an ci gyaransa, ayar suratul ma'ida IN TU AZZIBHUM FA INNAHUM IBADUK WA IN TAGFIR LAHUM FA INNAKA ANTAL AZIZUL HAKIM duk da rubuto ayar yayi amman shi jahilin sai cewa yayi FA INNAKA ANTAL GAFURUR RAHIM haka farkon raddinsa ga 'yan tijjaniya yace" ALLAZINA HUM IZA ASABATHUM sai ya sake cewa" ALLAZINA IZA ASABSATUM.. Kunji chakwakiya fa, haka a wani karatunsa yana karanta tarihin matan Annabi S.A.W wai ayar da take suratul Ahzab tana gargadi ga Matan Annabi itace" INKUNTUNNA TURIDNAL HAYATUD DUNYA WAZINATAHA FATA A LAINA UMATTI U KUNNA WA USARRIH KUNNA amman jahilin wai sai yace." FATA A LAINI UDALLIQUKUNNA WA USARRIH KUNNA, kuji jahili wanda beyi karatun Qur'ani ba, sannan ayar ta suratu Ahbaz yazo kan kissar Zainab da zaid ayar itace WAMA KANA LI MU'UMINUN WALA MU'UMINATUN IZA QADALLAHU WARA SULUHU AMRAN AY YAKUNA LAHUMUL KIYARATU MIN AM RIHIM WAYAY YA'ASILLAH WARA SULAHU FAQAD DALLA DALALAN MUBINA amman kasgin jahilin sai yace" FAQAD DALLA DALALAN BA'IDA kunji jahili wanda beyi karatun qur'ani ba. Idan nace zan dinga kawo kuskuren wannan hanfefen sai na kawo sunfi hamsin, don ko aya daya bazai iya ba ammn ya dinga wa Qur'ani Hawan qawara.
.
To wai wannan kuhungun jahilin kasgi, wai a fadar wasu wawayen shine malami kuma wai hanferen shine jagoransu, kai godiya ta tabbata ga Allah daya saka mabiya wannan zindiqin suka kasance wawaye mahaukata, tabbas kamar yadda suke fada na yarda Amirul jahilina shine mujaddadin wawaye na wannan zamani.
.
Abdun jabbarun sai dai kayi hakuri, na gaba yayi gaba na baya sai labari, halifa qaribullah yayi maka nisan da har abada bazaka ta6a kamo koda farcensa saba, sai dai ka cigaba da haukanka da zagin nasa idan bakayi wasa ba hassada itace zata sheke ka har lahira, kuma ko shi Halifa Qaribun yasan kanada matsalar kwakwalwa, wanda ya kamata yasan yadda za'ayi a kaika dawanau tun kafin haukan naka yakai ka fara zagin annabawa kana tuhumarsu, abduljabbar nidai ina maka Addu'ar Allah ya baka lafiya ya rabaka da wannan cutar ta ta6in hankali da take damunka, su kuma jahilan da suke biye maka. Allah ya ganar dasu su fara zuwa makaranta suy karatu, don babu wani mai ilmi da hankalin da zai dauki wannan galmashoran mai dure duren ashariya da zagin sahabban Annabi wai da sunan malami.
.
Tofah dama ance duk yadda akai da jaki dai yaci kara, yanzu gaskiyar nan dana fada fa sai ka samu wasu jakunan sun fara tunkuyi koh? To jakunan kogo ayi ta tunkuyi lafiya, nidai babu jakin daya isa ya tunkuye ni na juya nace zan rama, ko shi kansa babban jakin naku na kogo be isa balle wasu karnukan farauta, saboda haka 'ya'yan mutu'a. Karnukan farauta haihuwar mutu'a kuy ta haushi lafiya.
.
Har yau dai
.
Angom Fatima ne Abban Sadiq
.
I.A.I

Back to posts
Comments:
[2016-02-24 12:46:57] Moh'd B. Ussaini :

To Maza Kaje Ka Tuba Domin Kayi Karya Gami Da Hahilci Bataimiye

[2016-07-01 13:33:04] ANAS AMEEN :

ALLAH YA SAWAKE AMEEN.

[2016-05-12 10:18:42] ummu aisha :

SLM

[2016-07-24 11:41:23] Aminu Rabiu Garun Gudinya Babura :

Ya Allah kaganar damu gaskiya katseratar da diga diganmu daga saba maka amin

[2016-07-30 09:45:55] MHD SANI :

Allah yasaka wa abduljabbar anyi masa kage kuma baze yafeba

[2016-09-16 20:21:32] ibrahimaliyusumaila@gmail.com :

kai arasa wanda za aiwa sharri sai abduljabbar

[2016-08-28 13:57:17] Shamsuddeen lawal anchau :

Tofa!

[2018-02-07 06:24:04] Zaharaddeen m.abubakar deen :

to allah yaimana jagora amin mudai sunnah sak.


UNDER MAINTENANCE

Share|

Kaima shiga a tattauna da kai
* No boards.

Online: Guests: 2


→Ra'ayin jama'a game damu

 IDAN KANA BUKATAR A TALLATA MAKA HAJAR KA A WANNAN SHAFIN DA SAURAN SHAFUKAN MU KANA IYA TUNTUBAR MU TA WADANNAN HANYOYIN KAMAR HAKA:


Email: bjournalist55@hotmail.com

Phone No: 09035830253

Facebook: Basheer Journalist Sharfadi

Address: Ittihad Computer Centre,  No 92 Daneji Kano


MAI TALLA SHI KE DA RIBA


*Bayanan ka*
Browser din da ka hawo Mozilla

Kasar da kake United States

Adadin Maziyarta 210710

Adadin Wadanda Sukayi Comment 65691

A Wadanda Suka Shiga Tattaunawar Mu 54


Follow @bjournalist55
→Yi Adding Dina Ta Facebook
→Yi Like Na Dakarun Sunnah Page
→Yi Like Dina Ta Facebook

*Shafuka Masu Alaka Da Mu*

→Basheer Sharfadi wordpress
Basheer Sharfadi Blog Spot
UP
→Home

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah)
ISLAMIC DATE
  • phpimg2.php?it&ic=yellow



  • Click to Sms
    Click to Call


    Basheer journalist sharfadi3
    Coollogo com-1281358

    Ring ring