The Soda Pop
Google69490f6862051cb8
google-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlBasheer journalist sharfadi14

Basheer journalist sharfadi14.jpg6
Basheer journalist sharfadi 11 1
Maraba Da Zuwa Wannan
Shafi Mai Al-barka 1

☀ Zabi inda kake son shiga ☀
Menunks
→Home
→Akidojin Ahlussunnah
→Addinin musulunci (35)
→40 Hadith (50)
→Fadakarwa (120)
→Neman labarai (20)
→Shi'a Kafirci (50)
→Hadith (55)
→Khudubobi (24)
→Tarihin magabata (60)
→Raddi / Maida martani (99)
→Face book post (30)
→Monthly Archives (60)
→Tambaya da Amsa (20)
→Sahabban Annabi {s.aw} (50)
→Taskar maluman sunnah (25)
→Akidar Y'an Shi'a Dangane da Al'kur'ani
→Fassarar Usulussunnah (20)
→Sheik Ja'afar {Rahimahullah} (65)
→Sheik Abubakar Gumi {Rahimahullah} (30)
→Sheik Dr. Muhammad Sani R/Lemo
→Salafiyyah Network Nigeria (100)
→Adam Sani Abu-Umayrah (99)
→Salaf Ustaz (79)
→Malama Ummi Ahmad Katsina
→Malama Amina Saleh Mande
→Labarai (40)
→Nishadantarwa (10)
→Siyasar Nigeria (9)
→Vidio (33)
→Audio (66)
→Hotuna (120)
→Internet Cheat (90)
→Site Achieve
→Application (10)
→Games (8)
→About me (01)

Wannan shafin mallakarCoollogo com-1281358 3
Ne




SHAFI DON KARUWAR MUSULMI
***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Huraira (r.a) yace: Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
'Wanda yayi karya a gareni. to ya tanadi mazaunin sa a wuta'
.
(Muslim).
.
Allah ya kiya shemu.
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Huraira (r.a) yace: Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
'Ku laqqantawa mamatanku 'LA ILA HA ILLALLAH'
.
(muslim).
.
.
Note:
Ma'ana: daga sanda kuka fahimci dan uwanki yazo gar-gara to ku laqanta ma sa kalmar shahada.
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Huraira (r.a) yace: Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
'Idan mutum ya mutu Ayyukan sa sun yanke sai dai guda uku (3).
1.Sadaqatu Jariya (sadaka mai gudana).
2.Ilmi da ake amfanuwa da shi.
3.'Da na gari da zai dinga yi masa Addu'a.
.
(Muslim)
.
.
Allah ka sa muma mubar irin wadannan baya domin dinga samun Incom a lahira.
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Huraira (r.a) yace: Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
'Wanda ya tuba kafin Rana ta bullo da ga Mafitarta Allah ya kar6i tuban sa'
.
(Muslim)
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Huraira (r.a) yace: Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
'Salloli biyar da Jumu'a Izuwa Jumu'a. Da Ramadhana Izuwa Ramadhana Ana kankare zunuban da suke tsakanin su. Idan (mutum) ya nisanci manyan zunubai'
.
(Muslim)
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Huraira (r.a) yace: Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
'Ba zaku shiga Al'jannah ba Har sai kunyi Imani. Baza kuyi Imani ba Har sai kunyi soyayya.
Shin bana shiryar daku a bisa wani Abu ba! Wanda Idan kuka aikata shi zakuyi soyayya!
'KU YADA SALLAMA A TSAKANIN KU'
(Muslim)
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Huraira (r.a) yace: Hakika Annabi (s.a.w) yace:
.
' Alamomin munafiki guda uku (3) ne:
1.Idan yayi zance se yayi karya.
2.Idan yayi Al'qawari se ya sa6a.
3.Idan aka amince masa se yayi Ha'in ci.
.
(Bukhari & Muslim).
.
Allah ka karemu daga fadawa daya daga wadannan munanan Hali.
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Huraira (r.a) yace: Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
''An qawata wuta da Abubuwan sha'awa, Sannan an qawata Al'jannah da abubuwan Ki''
.
(Bukhari & Muslim)
.
Note:
Ma'ana : Ita wuta an ka wata ta da abubuwan da zuciya take so take sha'awa Irin su kida da sauran kayan shaidan ci. Ita kuma Al'jannah An qawata ta da Abubuwa na Al'khairi wanda Ita zuciya take qin su.
.
Ya Allah ka karemu da sharrin son zuciya.
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Huraira (r.a) yace: Hakika Annabi (s.a.w) yace:
.
''Wanda ya halarci Jana'iza yana da Kiradun guda (1) Wanda kuma ya halarce ta Har aka binne ta dashi (ya raka ta) yana da Kiradani guda (2) '
.
Sai Aka ce da Annabi (S.a.w) Menene Qiradaaa ni??
.
Sai Annabi (s.a.w) yace:- 'Misalin duwatsu biyu masu girma'
.
(Bukhari & Muslim).
.
Wannan gara6asa ce da kuma Falala ta zuwa Jana'iza ya Yan uwa se mu daura Himma domin samun wannan gara6asa.
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Huraira (r.a) yace:
.
''Hakkin musulmi akan (dan uwansa) musulmi guda biyar ne:
.
1.Mayar masa da Sallama.
2.Duba shi Idan bashi da lafiya.
3.Zuwa masa Jana'iza.
4.Ka amsa masa gayyatar sa.
5.Kayi masa Addu'a Idan yayi Atishawa.
.
(Bukhari & Muslim).
.
Fatan zamu kiyaye.
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Huraira (r.a) Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
' Na haneku da yin zato domin Hakika zato shine mafi karyar zance'
.
(Bukhari & Muslim)
.
.
Wannan Wasiyya ce da Annabin mu yayi mana fatan zamu kiyaye.
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Huraira (r.a) yace:-
.
''Wani mutum yazo wajen Annabi (s.a.w) yace:-
.
'Ya Ma'aikin Allah!
.
Wane mutum ne yafi Can-Canta da na Kyautata masa???
.
Sa Annabi (s.a.w) yace:-
.
'Mahaifiyarka'
.
Sai mutumin yace Sannan wa??
.
Sai Annabi (s.a.w) yace: 'Mahaifiyarka'
.
Sai mutumin yace: Sannan wa??
.
Sai Annabi (s,a.w) yace: 'Mahaifiyarka'
.
Sai mutumin yace sannan wa??
.
Sai Annabi (s.a.w) yace: ' Sannan Mahaifin ka'
.
.
(Bukhari & Muslim)
.
Wannan Hadisin yana nuna mana yin biyayya ga Iyaye da kuma daraja Irin ta Mahaifiya wadda Annabi (s.a.w) ya mai-maita sau uku akan mahaifiya wannan ta sanya mu Yan Izala muka fi kowa biyayya ga Iyayen mu domin muna kwadaitar da su ga bin Allah Amman bama durqusa musu domin bama son su sa6awa Allah. A'a mu se dai Sunnah Sak babu sakin layi.

Note:-
Ba zan Tsawaita ba:
' Masu durquso sukan ce ai iyaye ne girma masu ake yi. Wannan gaskiya ne Amman fa ku tuna Allah ya fada a cikin suratun Nisa'i:- WA'IZA HUYYITUM BI TAHIYYATUN FA HAYYU BI'AH SANA MINHA AU RUDDUHA'
.
Ma'ana:
'Idan An gaisheku da gaisuwa to ku mayar da mafi kyawunta ko kuyi makamanciyarta'
.
To Idan ka durqusawa mahaifinka don gai suwa shi kuma yaya zeyi tunda an ce in anyi gaisuwa a maida Fiye da ita ko dai-dai da ita??
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Huraira (r.a) Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
''Kalmomi Guda Biyu masu sauqi a bisa Harshe. Masu nauyi a ma'auni Masu Soyuwa ga mai rahama (Ubangiji) ' Kalmomin Sune:-

'SUBHANALLAHI WA BIHAMDIHI .
'SUBHANALLAHIL AZIM'
.
.
(Bukhari & Muslim)
.
.
Kunji Anbaton Allah bisa koyarwar Annabin sa ba bisa koyar war.....

Allah ka tabbatar damu Bisa Sunnar Annabin ka.
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Hurairah (r.) yace: Annabi (s.a.w) yace:-
,
''Idan dayan ku ya farka daga baccin sa , ya face Hancinsa sau uku 3 Domin Hakika Shaidan yana yawo abisa Hancin''
.
(Bukhariy 23295, Muslim 238),
.
.
Wannan Hadisin Annabi (s.a.w) yana koya mana riga kafi da kuma tsafta,
.
.
Ya Allah don son da muke wa Annabin ka Da Iyalan Gidan sa ka bamu iko cikin biyayya ga Annabinka,
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Hurairah (r.a) Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
''Da badan kada na matsawa Al'ummata ba da na umarce su da yin asuwaki a kowance Al'wala''
.
(Ahmad 2460, Nasa'i 1/68, Ibn Khuzaimah 140,)
.
.
Ya Allah ka bamu Ikon riko da sunnar Annabin mu,
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abiy Hurairah (r.a) yace:- Annabi (s.a.w) yace:-
.
''Idan Kuda ya fada cikin abin shanku Ku dimiya shi sannan ku ciro shi, Hakika A cikin daya daga fuka-fukan sa akwai Cuta A dayan (Fika-fikin kuma akwai Waraka)''
.
A riwayar Abu Dawud ya kara da cewa ''Hakika Shi yana Fadawa ne da Fika-fikin da yake da cuta a cikin sa''
.
(Bukhari 3320,)
.
.
Annabin mu Likitan likitoci Ya Allah ka bamu Ikon koyi Da Annabin mu,
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi katada (r.a) Hakika Annabi (s.a.w) ya fada game da mage:-
.
''Hakika Ita ba najasa bace HAKIKA ita tana daga masu Kekkewayawa A gareku''
.
(Abu Dawud 75, Tirmidhiy 92, Nasa'iy 1/55, Ibn majah 367, ibn khuzaimah 104,)
.
Wannan a takaice yana nufin mage ba najasa bace ita,
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Hurairah (r.a) yace : Annabi (s.a.w) yace:-
.
''Tsarkin Kwaryar (Abin al'wla) dayan ku Idan kare yayi lallage a cikin sa shine ya wanke shi sau ba kwai na Farkon su da kasa''
.
(Muslim 636)
.
A wata riwayar ta Tirmidhiy '' Na Farkon su dana Karshen su '' (Za'a wanke da kasa),
.
(Tirmidhiy 91),
.
Wannan ka'ida haka take har yau Amman wadan su maluman suna ganin amadadin kasa ka iya saka sabulu ko Omo da sauransu,
.
Amman abinda yafi don kariya shine kasa Kasar Domin ko da a yanxu binciken Likitoci na wannan Zamani sun tabbatar da Idan kare yasa baki To babu abinda ke iya kawar da kwayar cutarsa se kasar nan da Annabi (s.a.w),
.
Allahu Akbar kaji likitan likitoci, su se yanxu suka fahimta amman mu musulmai tuni Mun ringa munji kuma munyi Imani daga Annabin mu, Ya Allah kai salatin ga Annabin ka,
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi huraira (r.a) yace :- Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
''Me abin hawa yayi sallama ga me tafiya a kafa me tafiya a kafa yayi sallama ga na tsaye (wadanda ba tafiya suke ba) marasa yawa su yiwa masu yawa ''
A wata riwayar ta Bukhari kuma:-
''Karami yayi ga babba'' (6231)
.
.
(Bukhari 216, Muslim 6232)
.
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi huraira (r.a) yace:- Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
''Idan kunji kukan zakara! Ku roki Allah daga falalar sa. Domin hakika mala'ika ya gani,
Idan kukaji kukan jaki! Ku nemi tsarin Ubangiji daga shaidan domin hakika shaidan ya gani''
.
.
(Bukhari 3303, Muslim 2729)
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi huraira (r.a) yace :- Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
''A cikin ranar jumu'a akwai wani lokaci musulim ba zai dace da ita ba shi yana tsaye yana sallah , Ya tambayi Allah Al-khairi Har sai Allah ya Kar6a masa''
.
(Bukhari 6300, Muslim 852)
.
.
Ya Allah ka bamu dacen wannan lokaci,
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi Huraira (r.a) yace:- Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
''Hakika Allah yayi rangwame (Afuwa) ga Al-ummata Abinda ta zantar a cikin ranta ma tukar bata aikata ba ko ta zantar da shi''
.
.
(Bukhari 127, Muslim 5269)
.
.
Tunasarwa;
''''''''''''''''''''''''''''''''''''''''''''''''''''
Wannan hadisi yana nuna Allah yayi Afuwa / Yafiya ga mutane a dangane da Abinda suka raya a zuciyar su ba tare da sun aikata wannan Abinba ko sun xantar da shi to Allah baxe kama su da laifin sa ba,
''''''''''''''''''''''''''''''''''''''''''''''''''''
Ya Allah muna rokon ka kada ka kama mu da kura-kuran mu Allah ka gafarta mana laifukanmu don son mu da Annabinka na Hakika.
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi huraira (r.a) yace:- Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
''Allah (s.w.a) yace:- Dan Adam yana cutar dani yana zagin zamani Nine zamani Al-Amari yana hannuna Ina jujjuya dare da yini''
.
.
(Bukhari 7491, Muslim 2246)
.
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi huraira (r.a) yace:- Hakika manzon Allah (s.a.w) yace:-
.
''Ubangijina mai girma da daukaka yana sakkowa izuwa saman duniya ko wane dare yana cewa:-
'Wa ze rokeni na Amsa masa??
'Wa ze tambayeni na bashi??
'Wa ze nemi gafarata na gafarta masa??''
.
.
(Bukhari 1145, Muslim 758,)
.
Yan uwa kunji gara6asa da bonus daga ubangijin mu ya Allah kabamu ikon neman gafarar ka da rokonka a koda yaushe.
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
An kar6o daga Abi huraira (r.a) yace :- Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
.
''Wanda yayi Imani da Allah da ranar lahira kada ya cutar da da makocin sa ,
Wanda ya kasance yayi Imani da Allah da ranar lahira ya girmama bakonsa.
Wanda ya kasance yayi Imani da Allah da Ranar lahira Ya fadi Al-khairi ko yayo shiru''
.
.
(Bukhari 6136, Muslim 47)
.
.
Ya Allah kabamu ikon Aiki da sunnar Annabin mu,
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



***HADISIN MU NA YAU***
.
.
AN kar6o daga Abi huraira (r.a) yace:- ''An tambayi manzon Allah (s.a.w) 'Wane Aikine mafifi ci ?? Sa Annabi (s.a.w) yace:-
.
''Imani da Allah da manzon sa''
Sai Akace Sannan me? Sai yace:-
''Yin Jihadi saboda Allah''
Sai Akace sannan me? Sai yace:-
''Aikin hajji kar6a66e''
.
(Bukhari 26, Muslim 83)
.
.
Shiga wannan koren rubutun kayi like na wannan shafin mai Al-barka
@[656168224503950:0]



•••HADISIN MU NA YAU•••
.
Ankar6o Daga Abi huraira (r.a) yace:
.
''Idan Dayan ku yayi Tahiyya ya nemi tsari da Abu hudu yace:
.
''ALLAHUMMA INNAI A UZU BIKA MIN AZABI JAHANNAM WAMIN AZABIL KABR WAMIN FITNATIL MAHYA WAL MAMATI WAMIN SHARRI FITNATIL MASIHID DAJJAL''
.
(musulim 577)
.
.
Allah ka tabbatar damu kan sunnar Annabin ka da yin riko da ita takalmin kaza



•••HADISIN MU NA YAU•••
.
Ankar6o Daga Abi huraira (r.a) yace:
.
''Mafi Al-khairin ranar da rana take 6ullowa ranar jumu'a , Acikinta aka Halicci Annabi Adam Acikinta aka shigar dashi Al-jannah A cikinta ya fita daga cikinta''
.
(Muslim 854)
.
Fatan za'ayi jumu'a lafiya



•••HADISIN MU NA YAU•••
.
Ankar6o Daga Abi huraira (r.a) yace:
.
''Wanda ya tuba kafin rana ta fito daga mafadarta , Allah ze kar6i tubansa''
.
(Muslim 2703)
.
Ya Allah ka kar6i tubanmu ka gafartama kura-kuran mu



•••HADISIN MU NA YAU•••
.
Ankar6 Daga Abi huraira (r.a) yace:
.
''Hakika Annabi (s.a.w) yace:
.
''Allah s.w.a yace: Dukkan Ayyukan dan Adam na gare shi Sai dai azumi hakika shi nawane ni xan bada ladanshi Warin bakin me azumi yafi dadi awajen Allah fiye da kanshin Al-miski''
.
(Bukhari 5927. Muslim 1101)
.



***HADISIN MU NA YAU***
.
Ankar6o Daga Abi huraira (r.a) yace:
.
''Hakika Annabi (s.a.w) yace:
.
''Allah yace: Ka ciyar ya dan Adam Zan ciyar agareka''
.
(Bukhari 5352. Muslim 993)
.
Allah kabamu iko da damar ciyarwa domin mu samu ciyarwar Allah madaukakin sarki



***HADISIN MU NA YAU***
.
Ankar6o Daga Abi huraira (r.a) yace:
.
''Hakika Annabi (s.a.w) yace:
.
''Allah ba ze dube shi ba ranar Al-kiyama wanda ya take tufafin sa da girman kai''
.
(Bukhari 2087, Muslim 5788)
.
.
Allah ya karemu daga wuce iayaka irin na yan bidi'a



An kar6o daga Abi Huraira (r,a) Hakika manzon Allah (s.a.w) yace;-
.
''Idan dayanku ya kyautata musuluncinsa dukkan kyakykyawan aikin da ya aikata xa'a rubuta masa kwatankwacinta guda goma Izuwa ninki Dari bakwai dukkan mummunan aikin daya aikata xa'a rubuta masa misalinta guda daya''
,
(Bukhari 129, Muslim 42)
.
Y'an uwa kunji yadda Allah yake son mu da rahamar sa se mu dage da bauta masa ba tare da miss ba
.
Ya Allah muna rokon ka ninninka mana Hasanat din mu



An kar6o daga Abi Huraira (r.a) Hakika manzon Allah (s.a.w) yace:-
.
''Shaidan yana zuwa ga dayan ku se yace : Waye ya halicci kaza! Waye ya halicci kaza!! (har sai yace) waye ya halicci ubangijin ka!!! Idan kaji haka Ka nemi tsari daga ubangiji''
.
(Muslim3276, Muslim 134)
.
.
Ya Allah ka karemu daga sharrin shaidan da mabiyansa



***{HADISIN MU NA YAU}***
.
An karbo daga Abu Huraira Abdur-rahman dan Sakhrin (R.A) yace:
.
Naji manzon Allah (S.A.W) yana cewa:
.
"Duk abin dana haneku toku nisance (ku bar aikatashi) abin dana umarceku dashi to kuzo dashi gwargwadon iko.
Hakika yana daga abinda ya hallakar da mutanen dake gabanku shine yawan tambayoyinsu da sabawarsu ga
Annabawansu.
.
(Bukhari 7288) da (Muslim 1337).
------------------------------
Annabi (s,a,w) yahana sahabbansa yawan tambayoyi domin kada su takurawa kansu, akan abin da Allah bai dora musuba.
.
Ya Allah kaqara mana biyayya ga annabi Muhammad (s.a.w)



•••HADISIN MU NA YAU•••
.
An kar6o daga salim daga mahaifin sa (r.a) yace
.
"Haqiqa manzon ‪#Allah‬(s.a.w) yace"
.
""Babu hassada se ga abu guda 2 mutumin da #Allah ya bashi Al-qur ani yana bitarsa dare da rana
mutumin da #Allah ya bawa dukiya yake ciyar da ita (ta hanyar Allah) dare da rana""
.
(Bukhari da muslim)
.
#Allah ka kare mu daga hassadar da ba ta shari'a ba



¤¤¤ {HADISIN MU NA YAU} ¤¤¤
.
¤¤An kar6o daga Abi huraira (R.A) Hakika manzon ‪#‎ Allah‬(s.a.w) yace'
.
¤" Kada dayan ku yayi burin mutuwa im ma dai me kyautatawa (me aikin al-khairi) ne tana yiwuwa yaqara (aikin al-khairin)"¤
.
¤¤{Bukhari 7235, Muslim 2682,}¤¤
.
¤A wata riwaya ta Bukhari ya qara da cewa'
.
¤"Idan me sa6o ne tana yiwuwa ya daina"¤



{HADISIN MU NA YAU}
.
an kar6o daga Abi hurairah (R.A) yace
.
"Hakika manzon ‪#Allah‬(s.a.w) yace"
.
Wani mutum yana tafiya akan hanya se yaga wata kaya (me cutarwa) se ya kawar da ita (ya dauketa daga kan hanya) se Allah ya gode masa kuma ya gafar ta masa
.
(bukhari 654) & (muslim 1914)
.
A wani hadisin me Alaqa da wannan manzon rahama (s.a.w) yace kawar da qazanta daga kan hanya sada qa ce
---------------------------------------
Ya #Allah ka sanya mu cikin masu samun rahamar ka a wannan wata me Al-barka



••• ¤{HADISIN MU NA YAU}¤ •••
.
An kar6o daga Abi musa (r.a) yace;
.
Annabi (s.a.w) yace:
.
••• "Hakika ‪#Allah ‬mai girma da daukaka yana shimfida hannunsa da daddare (na qudura) domin kar6ar tuban masu sa6o da rana sannan yana shimfida hannunsa da rana domin kar6ar tuban masu sa6o da daddare har sai rana ta fito daga mahudarta" •••
.
••(muslim 2759)••
••A wata ayar kuma Allah (s.w.a) yace"
.
••"ku nemu gafarar ubangijin ku haqiqa shi me gafara ne"••
.
(suratu nuh 10)
.
Haqiqa #Allah yana qaunar bayinsa ya #Allah ka gafartamana zunuban mu



█(HADISIN MU NA YAU) █
.
█An kar6o daga Anas dan malik (R.A) yace:
.
█:manzon Allah (s.a.w) yace:
.
█"Kuyi sahoor domin cewa acikin sahoor akwai Al-barka"█
.
(Bukhari & Muslim)
.
█A wani hadisin kuma daga Anas dan malik da zaid bin sabit (R.A) sukace:
.
█:Munyi sahoor da manzon Allah (s.a.w) sannan muka tashi izuwa sallah.
.
Anas yace" sai nace wa zaidu :
.
'Nawane tsakanin kiran sallah da sahoor??
.
Sai zaidu yace" gwargwadon karanta aya 50
.
(Bukhari & Muslim)
.
saboda haka anso jinkirta sahoor sannan a gaggauta buda baki
.
Ya ‪#Allah‬muna roqon ka kasamu daga cikin bayinka da kake yan tawa a cikin wannan wata mai al-barka



¤{HADISIN MU NA YAU}¤
.
An kar6o daga Mu'awiyya (R.A} yace;
.
Annabi(s.a.w) yace;
.
"WANDA allah yake son shi da Al-khairi se ya sanar dashi Addini"
.
(Bukhari, 7312; Muslim, 1037)
.
Ya Allah ka sanar damu Addinin ka kuma bamu ikon aiki dashi­



{HADISIN MU NA YAU}
_____________________________
An kar6o daga Uqbatu bin Amir yace;
.
'Annabi (s.a.w) yace:
.
" Wanda yayi Al-wala sannan yace:
.
" Na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai bashi da abokin tarayya sannan ya shaida Annabi muhammad (s.a.w) bawan (Allah) ne kuma manzon sane,
.
Za'a bude kofofin Al-jannah guda 7 a gareshi ya shiga ta inda yaga dama"
____________________________
¤[Muslim, 234]¤
.
Fadin wannan kalma ba wai ta tsaya ne ga furuci kawai ba se ka qudurce a zuci kuma kai biyayya ga Allah da manzon sa,
.
Allah ka kar6i ibadun mu a wannan watan



*** ¤{HADISIN MU NA YAU}¤ ***
.
¤An kar6o daga Abi sa'eedul khudri (R.A) yace:
.
Annabi(s.a.w) yace:
.
¤" Wanda ya yarda da Allah shine ubangiji ya yarda da Addinin musulunci Da kuma Annabi muhammad (s.a.w) Al-jannah ta wajaba a gare shi"¤
.
(Abu dawud 1529)
.
¤"An kar6o daga Anas (r.a) yace :
.
Annabi (s.a.w) yace:
.
¤" Babu dayan ku da ze shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma Annabi muhammad (s.a.w) manzonsa ne yana mai gasgatawa a cikin zuciyarsa face sai Allah ya haramta wuta a gareshi"¤
.
(Bukhari 128, Muslim 32)
.
Imani da Allah da manxon sa baya taqaita ga furici kawai face se kayi aiki da shi don haka ba wai kace a baki ka yarda da Allah ba kuma kana yin Abinda ya sa6a da koyarwarsa dole se kabi abinda yaxo da shi shine kai imani dashi,
.
Allah yasa mu dace



{HADISIN MU NA YAU}
.
An kar6o daga Abi Hurairah (r.a) yace
.
"Hakika manzon Allah (s.a.w) yace"
.
"" A cikin rana jumu@ a kwai wani lokaci mu sulmi ba ze dace da shi ba yana mai addu'a face idan ya roqi ‪#Allah ‬Al-khairi ze bashi (za'a amsa addu arsa)
.
(bukhari 6400) & (muslim 802)
.
Ya #Allah ka sa mu yi gaman katar da wannan lokaci don haka ake son ka zama cikin bauta da roqon uban gijin ka a dukkan ranar jumu@n gaba daya-
-------------------------------------HAPPYJumu@MUBAR@K



***An kar6o daga Abi hurara {r.a} yace:-
.
Annabi {s.a.w} yace:-
.
''Bawa {mutum} ba ze suturta bawa ba har sai Allah ya suturtashi a ranar lahira''
.
{muslim}
.
Allah ka samu cikin wadanda Allah ze suturta
.
A wani hadisin na Abu huraira yace:- Annabi {s.a.w} yace:-
.
''Duniya kurkukun mumini ce kuma Al-jannar kafiri''
.
{muslim}
.
A wani hadisin na Abi hurairah yace:-
.
'Badade na {yana nufin Annabi s.a.w} yayi min wasiyya da Abu guda uku
.
1.Azumin kwana uku a kowane wata
.
2.Sallah duha {walaha}
.
3. Nayi wuturi kafin nai barci
.
{Bukhari & muslim}
.
Ya ‪#‎ Allah‬ka bamu ikon riko da sunnar Annabin mu garam gam

*************************

→Labarai

HASSADA MUGUN CIWO, ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA,(Imam Aliyu Indabawa)

HASSADA MUGUN CIWO, ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA,(Imam Aliyu Indabawa)
.
Wannan da kuke gani shine Dr kalifa qaribullah nasiru kabara, wanda ya kasance shine halifan dariqar qadiriyya, kuma muna girmama shi saboda halayensa na kawaici da sanin ya kamata, sai Allah ya jarrabe shi da wani taqadarin kani wanda ya addabe shi da hassada kullum cikin zaginsa yakeyi yana kushe shi yana aibata shi,
.
Asali abinda yasa yake masa wannan hassadar shine saboda halifa qaribullahi Allah yayi masa ni'imomi da baiwarwaki wanda shi kanin nasa bashi dasu, yafi shi duk wani abu da ake so, ta bangaren daukaka, da Ilmi da 'yaya da kudi da magoya baya da manyan mutane Sarakuna, uwa uba kuma yana da hankali wanda shi kanin nasa yayi rashinsa,
.
Sannan ga mukamin Halifa da yake rike dashi wanda shine yafi komai kona masa zuciya da motsa masa hassada, saboda shi a tunaninsa ai shine yafi cancanta daya gaji mahaifinsa ya zama halifan qadiriya saboda tunaninsa wai yafi Qaribu Ilmi shine yasa ya dade yana zagin Halifa karibu yana cutar da shi ta ko'ina yana nuna hassadarsa gare shi, dayake dama hassada ga mai rabo taki ce, shi kuma halifa Qaribu kullum sai kara gaba yakeyi har wasu kashashen ma suna bashi lambar yabo ta girmamawa amman duk da haka har yanzu Abdun jabberun yaki ya gane,
.
Ku duba Ko A haife qaribu ya haifi Audujanbiri amman saboda tantiranci da rashin tarbiya babu irin zagin da bayayi masa akwai Lokacin Audu janbiri yace,"qaribu wai babarsa da cikinsa ta shigo gidan malam wai qaribu ba dan malam bane wai shege ne kuma a duba dashi qaribun dashi Audu janbirin waye yake kama da malam kabara, kuma wai a cikin taron daruruwan mutane yayi wannan maganar, ba wannan kadai ba da dai sauran maganganu masu muni wanda shi kuma qaribun dayake yasan kanin nasa yana da ragaggen hankali baya biye ta tashi kullum hakuri yake dashi, lokacin da magoya bayan qaribu suka ga abin nasa fa ya wuce tunani ya koma tsantsar iskanci da rashin mutunci sai sukace suma dai dai suke da dan iska, inda duk lokacin da yazo wani taro ko maukibi sai suki su barshi ya shiga idan ma ya shigo sai su jefe shaidani, haka suka dinga yiwa dan banza daga karshe dayaga uwar bari da kansa yaje ya bawa halifa Qaribu hakuri akayi salhu tun daga lokacin abu ya danyi shiru,
.
Sai yanzu ya tsiro da wani iskancin, yana zagin Halifa qaribullah, dama tun asali kasancewarsa mutum mai neman Suna kota halin qaqa, amman hakan yaki samuwa yasa yake cin zarafi da cin mutuncin mutane sai kaji shi yana zagin babban malami wanda ya haife ya haife shi,
.
haka ya koma ta6o 'yan siyasa wanda duk gomnatin da take kai to sai yayi ta zaginta kenan har sai an bashi wani abun, misali lokacin mulkin kwankwaso na farko haka ya dinga bi yana zagin kwankwaso har sai da kwankwaso ya bashi fili a gwale filin mushe, wanda yanzu haka a cikin filin yayi gidansa yayi masallacin juma'a filin ma hakkin mutane, lokacin da kwankwaso ya tafi shekarau yazo sai ya koma 6angaren shekarau yana masa jagaliya da yaga shekarau baya bukatar tafiya da 'yan jagaliya irinsu sai ya dinga zagin shekarau har yake cewa idan yabi shekarau to shi dan zina ne, ana nan sai malam shekarau yayi masa wani babban Alkhairi wanda ya fito yace duk duniya ibrahim masu girma guda uku ne, da Annabi ibrahim da ibrahim inyass da ibrahim shekarau, lokacin da kwankwaso ya dawo be tafi dashi ba sai ya koma zagin kwankwaso ko lokacin da kwankwaso ya ta6a Annabi S.A.W sai ya dinga zagin kwankwaso har yace dashi ya zama kafiri, haka ya tara mutanensa har ya dauki sulke da kwalkwali ya saka a jikinsa , ya umarci 'yan jagaliyar yaransa suka rike makamai suka fito gari suna zanga zanga, amman yadda zakasan munafiki ne sai gashi lokacin da yake wa 'yan tijjaniya raddi yana siffanta Muhammadu Rabi'u kwankwaso da mai kishin musulunci,
.
Ba 'yan siyasa kadai ba, tuntuni shine yau ya ta6o 'yan izala gobe kaji ya ta6o 'yan tijjaniyya jibi ya ta6o 'yan qadiriya ko wani malami wanda bashi da dariqa, tun mutane suna biye masa har suka gane manufarsa suka gane cewa yana fama da ta6in hankali ta yaya zasu tsaya suna rigima da mahaukaci sai duk suka kyale karen yaje yayi ta haushinsa shi kadai, daya ga haka sai ya canza dabara akan ya samu masoya wanda zai dinga damfararsu 'yan kudaden su, haka yayi ya dinga tara karatu da sunan kishin Annabi da soyayyarsa nan ko babu abinda yake koyawa sai jahilci da dure duren ashariya, Kunji AMIRUL FASIKINA HUJJATUL JAHILINA kenan,
.
Koda matasan suka fuskanci babu wata tsiya na karatu da ake karuwa da Abdun jabberun sai duk suka dinga watsewa suna karewa kamar hatsin guziri, daya fuskanci neman Sunan dayake har yanzu a kano ba'asan da wani Abdun jabberun ba, wanda ko a gwale filin mushe babu wanda yasan dashi, kuma gashi na cefane yana gagararsa sai ya tsiro da wani iskanci da zindikanci na zagin sahabban Annabi inda yaje ya kar6o kwangilar kudi wajen Iro jakin zariya L.A don ya samu magoya baya, lokacin daya fara zagin sahabbai irinsu sayyadi Mu'awiya A,S yana kawo hadisai ta karfin tuwo yana juya musu ma'ana malaman Sunnah sun zabura suna mayar masa da raddi wanda shi dama abinda yake so kenan ayi ta zancensa yayi suna a san dashi, bayan lokacin da malam Alqasim yayi buji buji dashi akan littafinsa muqaddimatul Khaziba, haka aka dinga fama dashi akan yazo a zauna ayi muqabala akan wannan mas'alar ta fi'atul bagiya, amman hakan yaki yuyuwa kullum ya zauna sai dai dure duren ashariya da tsine tsine da karya da cika baki da alfhari da ihu da kowayee, a haka yanzu zindiqancin nasa da iskancin nasa har yazo ya fara zaginsu sayyadi Abubakar yana karyatashi akan hadisin gadon Annabi, yana zagin sayyadi usman akan wai azzalumi ne a lokacin mulkinsa, yanzu da malaman Sunna suka gane cewar bamagujen dan shi'ar yanada ta6in hankali sai duk suka kyale shi, don idan banda me ta6in hankali babu wanda zai dinga zagin sahabbai yana tuhumarsu,
.
To sai rannan mai tatsinen a wani shirmen sa dayake yi wai da sunan karatu yana karanto wani soki burutsun littafinsa mai suna MUQADDIMATUL KHAZIBAH babi mai taken LA TASABBU AS'HABI sai yazo maganar akan wani Hadisi da Halifa Qaribullah ya rawaito akan Sayyadi Ali inda ya dinga ciwa halifa Qaribullah mutunci yana fada masa maganganu na 6atanci yana cewa zasu 6ata dashi akan imami, ba don komai yake haka ba wai don kawai halifa shi yana girmama sahabban Annabi baya zaginsu sannan yana fadar gaskiya a duk inda ta dace, ko a wani haukan karatun Amirul jahilina na baya naji wai har yana cewa wai qaribu yayi maja da 'yan izala yana kiransa da nasibi,
.
To janbiri idan ma izalar qaribu ya koma ai ya gano itace gaskiya ne, tunda gaskiya yake bi, kuma kowa yayi shaidar cewa qaribu malami ne me koyar da karatu wanda yakanyi tafsiri a gidan sarki, sannan a ranaku yakan karanta sahih muslim da Algunya da ishreniyya, ba kamar ka ba wanda babu abinda ka iya sai dai ka tara mutane kayi ta dura ashariya kana tsine tsine kana sheka karya kana hauka suna ihu kana koya musu ta'addanci kana cewa su dauki makamai suje masallacin da akai rikici a baya su kashe 'yan izala, kai saboda ci da qarfi irin na mai mai tatsine sai kaje ka rubuto hadisai da ayoyi kazo kayi ta karantasu da kyar kana kuskure a cikin ayoyin, mutumin da ko haddar simini daya bashi da ita a Qur'ani, kai ko Ayar Muhammadur rasulillah ma daya karanto akwai kusa kurai a cikinta, kai Abduljbbar wallahi jahili ne na karshe, na tabbata ko fatiha ma idan zai karanta sai an ci gyaransa, ayar suratul ma'ida IN TU AZZIBHUM FA INNAHUM IBADUK WA IN TAGFIR LAHUM FA INNAKA ANTAL AZIZUL HAKIM duk da rubuto ayar yayi amman shi jahilin sai cewa yayi FA INNAKA ANTAL GAFURUR RAHIM haka farkon raddinsa ga 'yan tijjaniya yace" ALLAZINA HUM IZA ASABATHUM sai ya sake cewa" ALLAZINA IZA ASABSATUM.. Kunji chakwakiya fa, haka a wani karatunsa yana karanta tarihin matan Annabi S.A.W wai ayar da take suratul Ahzab tana gargadi ga Matan Annabi itace" INKUNTUNNA TURIDNAL HAYATUD DUNYA WAZINATAHA FATA A LAINA UMATTI U KUNNA WA USARRIH KUNNA amman jahilin wai sai yace." FATA A LAINI UDALLIQUKUNNA WA USARRIH KUNNA, kuji jahili wanda beyi karatun Qur'ani ba, sannan ayar ta suratu Ahbaz yazo kan kissar Zainab da zaid ayar itace WAMA KANA LI MU'UMINUN WALA MU'UMINATUN IZA QADALLAHU WARA SULUHU AMRAN AY YAKUNA LAHUMUL KIYARATU MIN AM RIHIM WAYAY YA'ASILLAH WARA SULAHU FAQAD DALLA DALALAN MUBINA amman kasgin jahilin sai yace" FAQAD DALLA DALALAN BA'IDA kunji jahili wanda beyi karatun qur'ani ba. Idan nace zan dinga kawo kuskuren wannan hanfefen sai na kawo sunfi hamsin, don ko aya daya bazai iya ba ammn ya dinga wa Qur'ani Hawan qawara.
.
To wai wannan kuhungun jahilin kasgi, wai a fadar wasu wawayen shine malami kuma wai hanferen shine jagoransu, kai godiya ta tabbata ga Allah daya saka mabiya wannan zindiqin suka kasance wawaye mahaukata, tabbas kamar yadda suke fada na yarda Amirul jahilina shine mujaddadin wawaye na wannan zamani.
.
Abdun jabbarun sai dai kayi hakuri, na gaba yayi gaba na baya sai labari, halifa qaribullah yayi maka nisan da har abada bazaka ta6a kamo koda farcensa saba, sai dai ka cigaba da haukanka da zagin nasa idan bakayi wasa ba hassada itace zata sheke ka har lahira, kuma ko shi Halifa Qaribun yasan kanada matsalar kwakwalwa, wanda ya kamata yasan yadda za'ayi a kaika dawanau tun kafin haukan naka yakai ka fara zagin annabawa kana tuhumarsu, abduljabbar nidai ina maka Addu'ar Allah ya baka lafiya ya rabaka da wannan cutar ta ta6in hankali da take damunka, su kuma jahilan da suke biye maka. Allah ya ganar dasu su fara zuwa makaranta suy karatu, don babu wani mai ilmi da hankalin da zai dauki wannan galmashoran mai dure duren ashariya da zagin sahabban Annabi wai da sunan malami.
.
Tofah dama ance duk yadda akai da jaki dai yaci kara, yanzu gaskiyar nan dana fada fa sai ka samu wasu jakunan sun fara tunkuyi koh? To jakunan kogo ayi ta tunkuyi lafiya, nidai babu jakin daya isa ya tunkuye ni na juya nace zan rama, ko shi kansa babban jakin naku na kogo be isa balle wasu karnukan farauta, saboda haka 'ya'yan mutu'a. Karnukan farauta haihuwar mutu'a kuy ta haushi lafiya.
.
Har yau dai
.
Angom Fatima ne Abban Sadiq
.
I.A.I

Back to posts
Comments:
[2016-02-24 21:46:57] Moh'd B. Ussaini :

To Maza Kaje Ka Tuba Domin Kayi Karya Gami Da Hahilci Bataimiye

[2016-07-01 22:33:04] ANAS AMEEN :

ALLAH YA SAWAKE AMEEN.

[2016-05-12 19:18:42] ummu aisha :

SLM

[2016-07-24 20:41:23] Aminu Rabiu Garun Gudinya Babura :

Ya Allah kaganar damu gaskiya katseratar da diga diganmu daga saba maka amin

[2016-07-30 18:45:55] MHD SANI :

Allah yasaka wa abduljabbar anyi masa kage kuma baze yafeba

[2016-09-17 05:21:32] ibrahimaliyusumaila@gmail.com :

kai arasa wanda za aiwa sharri sai abduljabbar

[2016-08-28 22:57:17] Shamsuddeen lawal anchau :

Tofa!

[2018-02-07 15:24:04] Zaharaddeen m.abubakar deen :

to allah yaimana jagora amin mudai sunnah sak.


UNDER MAINTENANCE

Share|

Kaima shiga a tattauna da kai
* No boards.

Online: Guests: 1


→Ra'ayin jama'a game damu

 IDAN KANA BUKATAR A TALLATA MAKA HAJAR KA A WANNAN SHAFIN DA SAURAN SHAFUKAN MU KANA IYA TUNTUBAR MU TA WADANNAN HANYOYIN KAMAR HAKA:


Email: bjournalist55@hotmail.com

Phone No: 09035830253

Facebook: Basheer Journalist Sharfadi

Address: Ittihad Computer Centre,  No 92 Daneji Kano


MAI TALLA SHI KE DA RIBA


*Bayanan ka*
Browser din da ka hawo Mozilla

Kasar da kake

Adadin Maziyarta 272548

Adadin Wadanda Sukayi Comment 65691

A Wadanda Suka Shiga Tattaunawar Mu 54


Follow @bjournalist55
→Yi Adding Dina Ta Facebook
→Yi Like Na Dakarun Sunnah Page
→Yi Like Dina Ta Facebook

*Shafuka Masu Alaka Da Mu*

→Basheer Sharfadi wordpress
Basheer Sharfadi Blog Spot
UP
→Home

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah)
ISLAMIC DATE
  • phpimg2.php?it&ic=yellow



  • Click to Sms
    Click to Call


    Basheer journalist sharfadi3
    Coollogo com-1281358