80s toys - Atari. I still have
Google69490f6862051cb8
google-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlBasheer journalist sharfadi14

Basheer journalist sharfadi14.jpg6
Basheer journalist sharfadi 11 1
Maraba Da Zuwa Wannan
Shafi Mai Al-barka 1

☀ Zabi inda kake son shiga ☀
Menunks
→Home
→Akidojin Ahlussunnah
→Addinin musulunci (35)
→40 Hadith (50)
→Fadakarwa (120)
→Neman labarai (20)
→Shi'a Kafirci (50)
→Hadith (55)
→Khudubobi (24)
→Tarihin magabata (60)
→Raddi / Maida martani (99)
→Face book post (30)
→Monthly Archives (60)
→Tambaya da Amsa (20)
→Sahabban Annabi {s.aw} (50)
→Taskar maluman sunnah (25)
→Akidar Y'an Shi'a Dangane da Al'kur'ani
→Fassarar Usulussunnah (20)
→Sheik Ja'afar {Rahimahullah} (65)
→Sheik Abubakar Gumi {Rahimahullah} (30)
→Sheik Dr. Muhammad Sani R/Lemo
→Salafiyyah Network Nigeria (100)
→Adam Sani Abu-Umayrah (99)
→Salaf Ustaz (79)
→Malama Ummi Ahmad Katsina
→Malama Amina Saleh Mande
→Labarai (40)
→Nishadantarwa (10)
→Siyasar Nigeria (9)
→Vidio (33)
→Audio (66)
→Hotuna (120)
→Internet Cheat (90)
→Site Achieve
→Application (10)
→Games (8)
→About me (01)

Wannan shafin mallakarCoollogo com-1281358 3
Ne




SHAFI DON KARUWAR MUSULMI
{TA YAYA ZAKIYI WA MIJINKI BIYYAYA} ?(001)
.
Wallafar malama jamila mukhtar saleh.
.
**ABUBUWAN DA KE CIKIN LATTAFIN**,
1)GABATARWA
2)TARIHIN MAWALLAFIYAR
3)GODIYA
4)SADAUKARWA
5)MA'ANAR AURE
6)HIKIMAR AURE
7)HUKUNCIN YIN AURE
8)SIFFOFIN MATAR DAYA DA ZA'A AURA
9)MATAKAN NEMAN AURE A MUSULLUNCI
10) SHARUDDAN AURE
11)AUREN DA SHARI'A TA HARAMTA
12)WASANNI YAYI KWANCIYAR AURE
14)KWANCIYAR AURE
15)LADUBBAN JIMA'I
16)ABUBUWAN DA AKA HANA GURI SADUWA
17)WANKAN JANABA
18)SIFFAR WANKAN JANABA
19)SAKAMAKON WANKAN JANABA
20)HAKKIN MA'AURATA A JUNANSU
21) NAU'IN MATA
22) RAYUWAN MATA KAFIN MUSULUNCI
23)RAYUWAN MATA A MUSULUNCI
24) RAYUWAN "YA MACE
25) A MATSAYINKI NA "YA MACE YAKAMATA KI SIFFANTU DA WADANNAN SIFFOFIN 26)SUTURAN "YA MACE
27)TSAFTAR JIKI DANA MUHALLI DON SAMUN NATSUWAR MAZAJE
28)ABINDA KE SA NAMIJI YA FITARAN MATARSHI
29) WASU ABUBUBWA DA AKE SO NAMIJI YA DINGA YIWA MATARSHI
30)TARBIYYA
31)ZAMA DA MIJI
32)SHAWARA GA "YAN UWA MATA
33) KAMMALAWA
34) MANAZARTA.
WADANNAN ABUBUWAN SUKE CIKIN LATTAFIN ZAMU DINGA KAWU MUKU DA IZININ ALLAH DAFATAN ALLAH YATAI MAKE MU
YAKUMA AMFANAR DA YAN UWAN MU BAKI DAYA
ITA KUMA
MALAMA JAMILA MUKHTAR SALEH ALLAH YASAKA MATA DA ALHERIN SA YAKUMA KARA MATA KWARIN GWUIWA. AMEEN



TA YAYA ZAKI WA MIJIN KI BIYAYYA ? (002)
.
Wallafar jamila mukhtar saleh,
.
:):D:) GABATARWA :):):)
.
Dukkan yabo da godiyasun tabbata ga Allah (swt).
Tsira da amincin Allah su kara tabbata ga Annabi Muhammadu (saw) da sahabbansa, da duk wanda suka bisu da kyautatawa har zuwa ranar tashin Alkiyamah.
**** MANUFAH ****
HAkika wannan littafi na rubuta shine don ya amfanar da Al'ummar yan" uwanmu musulmai.
Wannan littafi in bai amfanar ba to ba zai cutar ba, ni dai manufata Alkhairi ga yan" uwa musulmai, don warware matsalolin ma'aurata, da kuma samun nasarar zaman aure; domin auri-saki yayi yawa; ko Allah zai kawu saukin hakan a kasarmu najeriya
Allah(swt) yayi gaskiya inda yake cewa :
"ya ku waadanda kukayi imani, ku kare kanku da na iyalan ku daga shiga wuta wadda makamashinta mutane ne da duwatsu. Akanta akwai mala'iku masu karfi, basu sabama Allah abinda ya umurce su,kuma suna aikata abinda ya umurce su."
muna rokon Allah (swt) ya yafe mana kura-kuranmu da mukeyi dare da rana, yabamu ikon cikawa da imani, amin.
Daga yar" uwarku maison cigaban Addinin musulunci.
JAMILA MUKHTAR SALEH KOFAR BAI, KATSINA
GSM NO 080 68540221.
NA fara rubuta littafin nan a shekara ta 2011, kuma na kammala shi 20/91433h. Wanda yayi daidai da 08/08/2012:



TA YAYA ZAKI WA MIJINKI BIYAYYA (003)
.
Wallafar jamila muktar saleh.
.
** TARIHIN MAWALLAFIYAR **
.
JAMILA MUKHTAR SALEH an haife ni a unguwar kafar bai a shekara 1989. An sanyani makarantar firamare ta kayalwa watau ( Ahamdu comassie modal science primary school) kadan daga cikin malaman mu sune malama bailkisu, malama Rukayya muhammad da sauransu, Allah yasakanya masu da aljannah firdausi, Ameen.
.
A shekara ta 2002 na samu nasarar shiga makarantar kwalejin yan mata dake katsina watau GOVT.GIRLS, COLLAGE KATSINA ( GGCK).
Kadan daga cikin malaman mu na wannan makaranta a wannan lokaci sune; mal. Jamilu, mal. Babangida, da sunransu Allah yasakama masu da Aljannah firdausi Ameen.
.
Nasamu wucewa zuwa kwalejin koyon harshen larabci da ilimin Addinin musulunci watau (ATC) a shekara 2006. Kadan daga cikin malaman mu na wannan makaranta sune; mal. Ashiru Bala yandaki,mal. Masa'udu, da sauransu.
.
Allah (SWT) yasaka masu da Aljannah firdausi Ameen.
.
Bayan kammala wannan makaranta ATC sai na samu aikin koyarwa a wata makarantar islamiyya mai suna TARBIYYATUL AULAD dake kofar bai a shekarar 2007. Kasantuwar makaranta ce mai son cigaban Addinin musulunci, kuma sunada kyawawan manufofi, kadan daga cikin irin manufofin wannan makarantar na cigaban Addinin musulunci sune;
.
1) Tarbiyyantar da dalibai a karkashin jagorancin AL'QUR'ANI DA HADISAN ANNABI SAW.
2) isar da sakon Allah kuma umurni da kyawanan ayyuka da kuma hani da munanan ayyuka, DAs.
A shekara 2011 nafara kokarin wallafa wani littafi dan takaitacce; domin isar da sako ko umurni Annabi (saw) da yake cewa
.
" BALLIGU ANNI WALAU AYA"
.
ma'ana (ku isar sakona ko da aya dayane ).
.
Na fara buga wannan littafi ne mai suna;
.
TA YAYA ZAKI WA MIJINKI BIYAYYA? na hausa da fatan zai amfani al'ummar musulmi baki daya.
.
In an samu kuskure a gyara mani manufa shine alkhairi, Allah yake shiryar da wanda ya so.



TA YAYA ZAKI WA MIJIN KI BIYAYYA ? (006)
.
Wallafar malama Jamila muktar sale.
.
3) HUKUNCIN YIN AURE
Aure muhimmin abu ne acikin shari'ar musulunci, musamman idan mukayi duba da cewar Addinin musulunci yayi tafiyan daidai da yadda Allah ya hallici dan adam, kuma shi dan adam mun sani yana bukatar saduwa tsakanin mace da namiji.
Hakika, malamai sun dabi'antar da dan adam a bisa halayensa zuwa ma'aunai guda hudu (4) abisa hukuncin aure;
a) halal;- aure yana zama halal idan bashi da sha'awa, baya bukatan haihuwa, amma zai iya biyama matarsa hakkinta.
b) wajibi;-aure yana zama wajibi ga mutumin da yasan yanada karfin sha'awa, wanda idan baiyi shi ba zai iya fadawa cikin zinace-zinace. Sannan zai iya daukar nauyin matan.
c) mustahabbi;- aure yana zama mustahabbi ga mutumin da yasan zai iya danne sha'awar sa ba zai yi zina ba, ko kuma ya zamanto zai iya yin aure da biyawa matarsa bukatar ta, da riketa ko kuma ya zamto sha'awa bata dame shiba amma yana son matar, domin Annabi yace "kuyi aure don ku hayayyafa don inyi alfahari da yawan al'ummata ranar alkiyamah" Ahmad ibn hambal ya ruwaito shi.
d) haramun;- aure yana zama haramun ne ga wanda baya iya biyawa matarsa bukatar ta.
Bukata ta kasu kashi biyu (2); akwai bukata ta sha'awar saduwa da bukata ta ciyarwa, tufatarwa, da muhalli, saboda fadar manzon Allah saw "ya ku taron matasa, wanda yasami iko acikin ku yayi aure; domin shi zai kiyaye ganin sa kuma ya kiyaye kansa daga zina". Bukhari da muslim suka ruwaito wannan hadith.
Sahabin Annabi, Abdullahi dan masa'ud yace " koda za 'ace kwana goma (10) ne suka rage mani arayuwata, sai na so yin aure don gudun kada in hadu da ubangijina ina gwauro (marar aure) "



TA YAYA ZAKI YI WA MIJINKI BIYAYYA?(007)
.
Wallafar malama Jamila muktar sale.
.
SIFFOFIN MATAR DA ZA'A AURA.
.
1) Mace mai son Addini da kamun kai, kuma mai kunya.
2) yar gidan mutunci, mai kyakkyawan dabi'a, saboda faden manzon Allah saw " Ana auren mace don abubuwa guda hudu 4:- kyawunta, dukiyanta, nasabanta, da addininta," sai yace "kuzabi ma'abuciyar addinin."
.
Bukhari da muslim suka ruwaito shi.
.
MATAKAN NEMAN AURE A MUSULUNCI
.
1) YA halarta namiji yaga matar da zai nemi aurenta.
2) sa'annan yanemi izinin yimata magana daga wurin iyayenta; domin su fahimci juna.
3) bayan iyaye sunyi bincike akansa sai su bashi lokaci da wurin da zasu rinka zaunawa domin fahintar junansu.
4) ya halarta su iyayen mace ko namiji su nema wa "ya"yansu wanda ya dace dasu idan bukatar hakan ta taso.
5) mace zata iya nuna wata alama ga wanda ta ke so ko ta furta masa cewa tana sonsa musamman ga (bazawara).
6) wani ko wasu suna iya ganin wata yarinya da ta dace da wani mutumin kirki su bashi shawarar ya neme ta.
7) ko kuma shi namijin yayi wa macen da yake so jirwaye mai kamar wanka, idan tana idda ko takaba, kamar yace, "ba mata irinki ke rasa mazajen aure ba", ko kuma yace " idan kin kammala iddah karki fara sanar da kowa sai ni".
.
SHADUDDAN AURE
.
Hakika aure baya kulluwa har sai ancika sharudda kamar haka:-
.
1- waliyi:- wannan shine majibinci al'amarin daya daga cikin ma'aurata watau (macen da za'a aura). Shine wanda zai iya zama mahaifi ko dan uwan mahaifi ko wanda akayiwa wasicci da shi, ko shugaba na musulunci da sauransu.
2- sadaki:- shina abinda ake bayarwa domin ya halatta wa ma'aurata kawunan su da zaman tare a rayuwansu, kuma sadaki zai iya zamowa daga kudi, ko wasu kaya, ko aikin kwadago a gona ko karatun Al'kur'ani zuwa wani zangon karatun. Zai iya zama dukiya mai yawa ko dan kadan; amma karancin sadaki yafi albarka kamar yanda yazo a hadisin Annabi swa.
3- siga:- shine furucin da manemin aure zaiyi na neman abashi auren "wance" sannan mahaifi ko waliyin matar ya furta mashi kalmomi da cewa ya yadda ya bayar da auren "yar sa mai suna "wance" ga "wane" sai shedu su shaida.
4- auna jini:- don a tabbatar da ba'a dauke da wata cutar zamani ko makamanci yan haka.



TA YAYA ZA KIYI WA MIJINKI BIYAYYA? (008)

7) AUREN DA SHARI'AH TA HARAMTA :-

1- AUREN MUTU'A :- shi ne auren wucin gadi na sati 1, ko wata guda 1, ko shekara daya 1 da sauransu.
Wannan nau'in aure, Annabi s.a.w ya hana yin shi, ma'ana ya haramta shi har sau uku 3, tun a yakin khaibar inda yace " huwa haramun !" huwa haramun!!" huwa haramun!!! Ila yaumil kiyamah"watau haramun ne shi, haramun ne shi, haramun ne shi, (auren mutu'a) har ranar alkiyamah saboda haka yanzu duniyar musulunci tayi ittifaki cewa " babu masu dabbaka wannan aure sai mabiya akidar SHI'A (Addinin mutanen farisa ).

2-AUREN SHIGARI::-
shi ne auren musanyen "ya "ya batare da sadaki ba, kamar kabani "yar ka in aura, ni kuma in baka "ya ta ka aura. Ba wani sadaki kawai

3- AUREN MUSHIRIKI KO MUSHIRIKA:-
wannan hadisai da Alkur'ani da ijima'in malaman sunnah sun haramta shi. Saboda fadan Allah s.w.a a inda yake cewa
" kar ku aura mushirika har sai ta musulunta"
sai kuma yace
" kar ku aura ma mushuriki har sai ya musulunta"
suratul bakara aya 220.

4- AUREN KARUWA:-
Har sai idan ta tuba daga karuwancin ta, to ana iya auren ta.

5- AUREN WANDA YAI HARAMA DA AIKIN HAJJI.

6- AUREN YAN UWA MATA NA TSATSO DAYA LOKACI GUDA.

7- AUREN MATAN DA MUTUM YA SAKE TA SAKI UKU.

8- AUREN DA AKA DAURA BATARE DA WALIYYI BA.

9- AUREN MUHARRAMI KO MUHARRAMA.

10- MUHARRAMAI TA FUSKAN NASABA SU NE :-

A- uwaye
B- "ya "ya
C- yan uwa
D- "ya "yan "yar uwa.

11-MUHARRAMA TAFUSKAN SURUKUTA SU NE :-

A-"ya "yan mata (agololi )
B- matar uba
C- matar kaka
D- uwayen mata
E- kakar mata
F- matayen "ya "ya na tsatso.

12-AUREN CIKIN IDDAH.



Koma saman shafi

→Labarai

HASSADA MUGUN CIWO, ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA,(Imam Aliyu Indabawa)

HASSADA MUGUN CIWO, ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA,(Imam Aliyu Indabawa)
.
Wannan da kuke gani shine Dr kalifa qaribullah nasiru kabara, wanda ya kasance shine halifan dariqar qadiriyya, kuma muna girmama shi saboda halayensa na kawaici da sanin ya kamata, sai Allah ya jarrabe shi da wani taqadarin kani wanda ya addabe shi da hassada kullum cikin zaginsa yakeyi yana kushe shi yana aibata shi,
.
Asali abinda yasa yake masa wannan hassadar shine saboda halifa qaribullahi Allah yayi masa ni'imomi da baiwarwaki wanda shi kanin nasa bashi dasu, yafi shi duk wani abu da ake so, ta bangaren daukaka, da Ilmi da 'yaya da kudi da magoya baya da manyan mutane Sarakuna, uwa uba kuma yana da hankali wanda shi kanin nasa yayi rashinsa,
.
Sannan ga mukamin Halifa da yake rike dashi wanda shine yafi komai kona masa zuciya da motsa masa hassada, saboda shi a tunaninsa ai shine yafi cancanta daya gaji mahaifinsa ya zama halifan qadiriya saboda tunaninsa wai yafi Qaribu Ilmi shine yasa ya dade yana zagin Halifa karibu yana cutar da shi ta ko'ina yana nuna hassadarsa gare shi, dayake dama hassada ga mai rabo taki ce, shi kuma halifa Qaribu kullum sai kara gaba yakeyi har wasu kashashen ma suna bashi lambar yabo ta girmamawa amman duk da haka har yanzu Abdun jabberun yaki ya gane,
.
Ku duba Ko A haife qaribu ya haifi Audujanbiri amman saboda tantiranci da rashin tarbiya babu irin zagin da bayayi masa akwai Lokacin Audu janbiri yace,"qaribu wai babarsa da cikinsa ta shigo gidan malam wai qaribu ba dan malam bane wai shege ne kuma a duba dashi qaribun dashi Audu janbirin waye yake kama da malam kabara, kuma wai a cikin taron daruruwan mutane yayi wannan maganar, ba wannan kadai ba da dai sauran maganganu masu muni wanda shi kuma qaribun dayake yasan kanin nasa yana da ragaggen hankali baya biye ta tashi kullum hakuri yake dashi, lokacin da magoya bayan qaribu suka ga abin nasa fa ya wuce tunani ya koma tsantsar iskanci da rashin mutunci sai sukace suma dai dai suke da dan iska, inda duk lokacin da yazo wani taro ko maukibi sai suki su barshi ya shiga idan ma ya shigo sai su jefe shaidani, haka suka dinga yiwa dan banza daga karshe dayaga uwar bari da kansa yaje ya bawa halifa Qaribu hakuri akayi salhu tun daga lokacin abu ya danyi shiru,
.
Sai yanzu ya tsiro da wani iskancin, yana zagin Halifa qaribullah, dama tun asali kasancewarsa mutum mai neman Suna kota halin qaqa, amman hakan yaki samuwa yasa yake cin zarafi da cin mutuncin mutane sai kaji shi yana zagin babban malami wanda ya haife ya haife shi,
.
haka ya koma ta6o 'yan siyasa wanda duk gomnatin da take kai to sai yayi ta zaginta kenan har sai an bashi wani abun, misali lokacin mulkin kwankwaso na farko haka ya dinga bi yana zagin kwankwaso har sai da kwankwaso ya bashi fili a gwale filin mushe, wanda yanzu haka a cikin filin yayi gidansa yayi masallacin juma'a filin ma hakkin mutane, lokacin da kwankwaso ya tafi shekarau yazo sai ya koma 6angaren shekarau yana masa jagaliya da yaga shekarau baya bukatar tafiya da 'yan jagaliya irinsu sai ya dinga zagin shekarau har yake cewa idan yabi shekarau to shi dan zina ne, ana nan sai malam shekarau yayi masa wani babban Alkhairi wanda ya fito yace duk duniya ibrahim masu girma guda uku ne, da Annabi ibrahim da ibrahim inyass da ibrahim shekarau, lokacin da kwankwaso ya dawo be tafi dashi ba sai ya koma zagin kwankwaso ko lokacin da kwankwaso ya ta6a Annabi S.A.W sai ya dinga zagin kwankwaso har yace dashi ya zama kafiri, haka ya tara mutanensa har ya dauki sulke da kwalkwali ya saka a jikinsa , ya umarci 'yan jagaliyar yaransa suka rike makamai suka fito gari suna zanga zanga, amman yadda zakasan munafiki ne sai gashi lokacin da yake wa 'yan tijjaniya raddi yana siffanta Muhammadu Rabi'u kwankwaso da mai kishin musulunci,
.
Ba 'yan siyasa kadai ba, tuntuni shine yau ya ta6o 'yan izala gobe kaji ya ta6o 'yan tijjaniyya jibi ya ta6o 'yan qadiriya ko wani malami wanda bashi da dariqa, tun mutane suna biye masa har suka gane manufarsa suka gane cewa yana fama da ta6in hankali ta yaya zasu tsaya suna rigima da mahaukaci sai duk suka kyale karen yaje yayi ta haushinsa shi kadai, daya ga haka sai ya canza dabara akan ya samu masoya wanda zai dinga damfararsu 'yan kudaden su, haka yayi ya dinga tara karatu da sunan kishin Annabi da soyayyarsa nan ko babu abinda yake koyawa sai jahilci da dure duren ashariya, Kunji AMIRUL FASIKINA HUJJATUL JAHILINA kenan,
.
Koda matasan suka fuskanci babu wata tsiya na karatu da ake karuwa da Abdun jabberun sai duk suka dinga watsewa suna karewa kamar hatsin guziri, daya fuskanci neman Sunan dayake har yanzu a kano ba'asan da wani Abdun jabberun ba, wanda ko a gwale filin mushe babu wanda yasan dashi, kuma gashi na cefane yana gagararsa sai ya tsiro da wani iskanci da zindikanci na zagin sahabban Annabi inda yaje ya kar6o kwangilar kudi wajen Iro jakin zariya L.A don ya samu magoya baya, lokacin daya fara zagin sahabbai irinsu sayyadi Mu'awiya A,S yana kawo hadisai ta karfin tuwo yana juya musu ma'ana malaman Sunnah sun zabura suna mayar masa da raddi wanda shi dama abinda yake so kenan ayi ta zancensa yayi suna a san dashi, bayan lokacin da malam Alqasim yayi buji buji dashi akan littafinsa muqaddimatul Khaziba, haka aka dinga fama dashi akan yazo a zauna ayi muqabala akan wannan mas'alar ta fi'atul bagiya, amman hakan yaki yuyuwa kullum ya zauna sai dai dure duren ashariya da tsine tsine da karya da cika baki da alfhari da ihu da kowayee, a haka yanzu zindiqancin nasa da iskancin nasa har yazo ya fara zaginsu sayyadi Abubakar yana karyatashi akan hadisin gadon Annabi, yana zagin sayyadi usman akan wai azzalumi ne a lokacin mulkinsa, yanzu da malaman Sunna suka gane cewar bamagujen dan shi'ar yanada ta6in hankali sai duk suka kyale shi, don idan banda me ta6in hankali babu wanda zai dinga zagin sahabbai yana tuhumarsu,
.
To sai rannan mai tatsinen a wani shirmen sa dayake yi wai da sunan karatu yana karanto wani soki burutsun littafinsa mai suna MUQADDIMATUL KHAZIBAH babi mai taken LA TASABBU AS'HABI sai yazo maganar akan wani Hadisi da Halifa Qaribullah ya rawaito akan Sayyadi Ali inda ya dinga ciwa halifa Qaribullah mutunci yana fada masa maganganu na 6atanci yana cewa zasu 6ata dashi akan imami, ba don komai yake haka ba wai don kawai halifa shi yana girmama sahabban Annabi baya zaginsu sannan yana fadar gaskiya a duk inda ta dace, ko a wani haukan karatun Amirul jahilina na baya naji wai har yana cewa wai qaribu yayi maja da 'yan izala yana kiransa da nasibi,
.
To janbiri idan ma izalar qaribu ya koma ai ya gano itace gaskiya ne, tunda gaskiya yake bi, kuma kowa yayi shaidar cewa qaribu malami ne me koyar da karatu wanda yakanyi tafsiri a gidan sarki, sannan a ranaku yakan karanta sahih muslim da Algunya da ishreniyya, ba kamar ka ba wanda babu abinda ka iya sai dai ka tara mutane kayi ta dura ashariya kana tsine tsine kana sheka karya kana hauka suna ihu kana koya musu ta'addanci kana cewa su dauki makamai suje masallacin da akai rikici a baya su kashe 'yan izala, kai saboda ci da qarfi irin na mai mai tatsine sai kaje ka rubuto hadisai da ayoyi kazo kayi ta karantasu da kyar kana kuskure a cikin ayoyin, mutumin da ko haddar simini daya bashi da ita a Qur'ani, kai ko Ayar Muhammadur rasulillah ma daya karanto akwai kusa kurai a cikinta, kai Abduljbbar wallahi jahili ne na karshe, na tabbata ko fatiha ma idan zai karanta sai an ci gyaransa, ayar suratul ma'ida IN TU AZZIBHUM FA INNAHUM IBADUK WA IN TAGFIR LAHUM FA INNAKA ANTAL AZIZUL HAKIM duk da rubuto ayar yayi amman shi jahilin sai cewa yayi FA INNAKA ANTAL GAFURUR RAHIM haka farkon raddinsa ga 'yan tijjaniya yace" ALLAZINA HUM IZA ASABATHUM sai ya sake cewa" ALLAZINA IZA ASABSATUM.. Kunji chakwakiya fa, haka a wani karatunsa yana karanta tarihin matan Annabi S.A.W wai ayar da take suratul Ahzab tana gargadi ga Matan Annabi itace" INKUNTUNNA TURIDNAL HAYATUD DUNYA WAZINATAHA FATA A LAINA UMATTI U KUNNA WA USARRIH KUNNA amman jahilin wai sai yace." FATA A LAINI UDALLIQUKUNNA WA USARRIH KUNNA, kuji jahili wanda beyi karatun Qur'ani ba, sannan ayar ta suratu Ahbaz yazo kan kissar Zainab da zaid ayar itace WAMA KANA LI MU'UMINUN WALA MU'UMINATUN IZA QADALLAHU WARA SULUHU AMRAN AY YAKUNA LAHUMUL KIYARATU MIN AM RIHIM WAYAY YA'ASILLAH WARA SULAHU FAQAD DALLA DALALAN MUBINA amman kasgin jahilin sai yace" FAQAD DALLA DALALAN BA'IDA kunji jahili wanda beyi karatun qur'ani ba. Idan nace zan dinga kawo kuskuren wannan hanfefen sai na kawo sunfi hamsin, don ko aya daya bazai iya ba ammn ya dinga wa Qur'ani Hawan qawara.
.
To wai wannan kuhungun jahilin kasgi, wai a fadar wasu wawayen shine malami kuma wai hanferen shine jagoransu, kai godiya ta tabbata ga Allah daya saka mabiya wannan zindiqin suka kasance wawaye mahaukata, tabbas kamar yadda suke fada na yarda Amirul jahilina shine mujaddadin wawaye na wannan zamani.
.
Abdun jabbarun sai dai kayi hakuri, na gaba yayi gaba na baya sai labari, halifa qaribullah yayi maka nisan da har abada bazaka ta6a kamo koda farcensa saba, sai dai ka cigaba da haukanka da zagin nasa idan bakayi wasa ba hassada itace zata sheke ka har lahira, kuma ko shi Halifa Qaribun yasan kanada matsalar kwakwalwa, wanda ya kamata yasan yadda za'ayi a kaika dawanau tun kafin haukan naka yakai ka fara zagin annabawa kana tuhumarsu, abduljabbar nidai ina maka Addu'ar Allah ya baka lafiya ya rabaka da wannan cutar ta ta6in hankali da take damunka, su kuma jahilan da suke biye maka. Allah ya ganar dasu su fara zuwa makaranta suy karatu, don babu wani mai ilmi da hankalin da zai dauki wannan galmashoran mai dure duren ashariya da zagin sahabban Annabi wai da sunan malami.
.
Tofah dama ance duk yadda akai da jaki dai yaci kara, yanzu gaskiyar nan dana fada fa sai ka samu wasu jakunan sun fara tunkuyi koh? To jakunan kogo ayi ta tunkuyi lafiya, nidai babu jakin daya isa ya tunkuye ni na juya nace zan rama, ko shi kansa babban jakin naku na kogo be isa balle wasu karnukan farauta, saboda haka 'ya'yan mutu'a. Karnukan farauta haihuwar mutu'a kuy ta haushi lafiya.
.
Har yau dai
.
Angom Fatima ne Abban Sadiq
.
I.A.I

Back to posts
Comments:
[2016-02-24 12:46:57] Moh'd B. Ussaini :

To Maza Kaje Ka Tuba Domin Kayi Karya Gami Da Hahilci Bataimiye

[2016-07-01 13:33:04] ANAS AMEEN :

ALLAH YA SAWAKE AMEEN.

[2016-05-12 10:18:42] ummu aisha :

SLM

[2016-07-24 11:41:23] Aminu Rabiu Garun Gudinya Babura :

Ya Allah kaganar damu gaskiya katseratar da diga diganmu daga saba maka amin

[2016-07-30 09:45:55] MHD SANI :

Allah yasaka wa abduljabbar anyi masa kage kuma baze yafeba

[2016-09-16 20:21:32] ibrahimaliyusumaila@gmail.com :

kai arasa wanda za aiwa sharri sai abduljabbar

[2016-08-28 13:57:17] Shamsuddeen lawal anchau :

Tofa!

[2018-02-07 06:24:04] Zaharaddeen m.abubakar deen :

to allah yaimana jagora amin mudai sunnah sak.


UNDER MAINTENANCE

Share|

Kaima shiga a tattauna da kai
* No boards.

Online: Guests: 1


→Ra'ayin jama'a game damu

 IDAN KANA BUKATAR A TALLATA MAKA HAJAR KA A WANNAN SHAFIN DA SAURAN SHAFUKAN MU KANA IYA TUNTUBAR MU TA WADANNAN HANYOYIN KAMAR HAKA:


Email: bjournalist55@hotmail.com

Phone No: 09035830253

Facebook: Basheer Journalist Sharfadi

Address: Ittihad Computer Centre,  No 92 Daneji Kano


MAI TALLA SHI KE DA RIBA


*Bayanan ka*
Browser din da ka hawo Mozilla

Kasar da kake United States

Adadin Maziyarta 726669

Adadin Wadanda Sukayi Comment 65691

A Wadanda Suka Shiga Tattaunawar Mu 54


Follow @bjournalist55
→Yi Adding Dina Ta Facebook
→Yi Like Na Dakarun Sunnah Page
→Yi Like Dina Ta Facebook

*Shafuka Masu Alaka Da Mu*

→Basheer Sharfadi wordpress
Basheer Sharfadi Blog Spot
UP
→Home

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah)
ISLAMIC DATE
  • phpimg2.php?it&ic=yellow



  • Click to Sms
    Click to Call


    Basheer journalist sharfadi3
    Coollogo com-1281358