Ring ring
Google69490f6862051cb8
google-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlBasheer journalist sharfadi14

Basheer journalist sharfadi14.jpg6
Basheer journalist sharfadi 11 1
Maraba Da Zuwa Wannan
Shafi Mai Al-barka 1

☀ Zabi inda kake son shiga ☀
Menunks
→Home
→Akidojin Ahlussunnah
→Addinin musulunci (35)
→40 Hadith (50)
→Fadakarwa (120)
→Neman labarai (20)
→Shi'a Kafirci (50)
→Hadith (55)
→Khudubobi (24)
→Tarihin magabata (60)
→Raddi / Maida martani (99)
→Face book post (30)
→Monthly Archives (60)
→Tambaya da Amsa (20)
→Sahabban Annabi {s.aw} (50)
→Taskar maluman sunnah (25)
→Akidar Y'an Shi'a Dangane da Al'kur'ani
→Fassarar Usulussunnah (20)
→Sheik Ja'afar {Rahimahullah} (65)
→Sheik Abubakar Gumi {Rahimahullah} (30)
→Sheik Dr. Muhammad Sani R/Lemo
→Salafiyyah Network Nigeria (100)
→Adam Sani Abu-Umayrah (99)
→Salaf Ustaz (79)
→Malama Ummi Ahmad Katsina
→Malama Amina Saleh Mande
→Labarai (40)
→Nishadantarwa (10)
→Siyasar Nigeria (9)
→Vidio (33)
→Audio (66)
→Hotuna (120)
→Internet Cheat (90)
→Site Achieve
→Application (10)
→Games (8)
→About me (01)

Wannan shafin mallakarCoollogo com-1281358 3
Ne




SHAFI DON KARUWAR MUSULMI
AZUMIN SITTU-SHAWWAL ))
"
"
'YAN-UWA-
Ga wani Saqo Mai Cike da Tarin- Alkairai masu
yawa
"
"
DON ALLAH-
Idan kuka Karanta, ku Tunatar da Wanda ya
manta da Wadannan azumin, kwanaki shidda (6)
Na cikin Wannan Watan, mai Suna kamar haka <
(( SHAWWAL ))>
"
"
'YAN-UWA-
{ IMAM MUSLIM } ...
ya fitar da hadisi Ingantacce, daga- ( Abu ayyuba
Al-ansariy ) (r.a) yace......
"
"
MANZON ALLAH (s.a.w) yace:
duk wanda ya azumci Ramadan / Sannan yabi shi
da Azumi guda Shidda (6) a Cikin watan-
Shawwal/ Zai kasance kamar Wanda ya Azumci
Shekara a Wurin Samun Lada......
"
"
'YAN-UWA,
Azumin Kwana shidda (6) Na Watan- ( Sallah )
wato watan Shawwal / { MUSTA,HABBI NE }..
"
WANNAN SHINE-
Zantuttukan mafiya yawa daga Cikin Malamai....
"
"
WASU KUMA SUKA CE-
{ MAKARUHI NE } / sabo da jin tsoron kada
Mutane su Dauka Cewa Shima Wajibi ne, Kamar
yadda na Ramadan yake Wajibi
"
"
FA'IDAN AZUMIN SHAWWAL
"
NA FARKO-
yin azumi Shidda (6) Na Shawwal / yana Cika
Ladan Azumin Shekara daya (1)
"
"
NA BIYU
Azumin- Shawwal, yana Ciki wani Gurbi na
Ibadar- mutum
( Tawayayya )
"
"
YADDA AKE YIN AZUMIN
Malamai sunyi Zantuttuka Guda biyu (2) Kamar
haka......
"
"
ZANCE NA FARKO
Malamai suka ce- yin azumin guda Shidda (6)
ajere Shi akafi so
"
"
ZANCE NA BIYU
Wasu malaman kuma, sunce-
Babu wani Lokaci da aka Qayyade yin Azumin
( Sittu-Shawwal ) a Cikin watan....
SUKA QARA DA CEWA-
yin azumin ajere, ko a Rarrabe, Duka daya ne
akowani Lokaci/ Amma acikin Watan- SHAWWAL
"
"
'YAN-UWA
WANNAN SHINE SAQON DA NIKE SO IN ISAR
AGAREKU
".
"~Ina maku fatan alheri


****DOKA**** (jibwis Social Media Nigeria)

Sako zuwa ga mambobin social media a fadin tarayyar Najeriya,

Allah yana fada a cikin alkur'ani mai girma cewa :
" Hakika Allah yana umartarku da ku maida amanoni zuwa ga ahlinta......."
Karkashin wannan ayar shugaban kwamitin Jibwis social media na kasa ya fitar da doka kan dukkan dan social media da ya dauko rubutun da bashi yayi ba wajibi yayi ishara zuwa ga asalin me rubutun.
Misali : Via merubutu, ko a karshe yace daga : me rubutu. Ko wani abu daze bayyana ba shine asalin me rubutun ba ga asalin me rubutun.

Alh Adamu Attahir
Sec. Gen. National Jibwis social media


HANTSI..... SHIRIN FITSARA NA RAI DANGIN GORO

Shirin 'RAI DANGIN GORO' hmmmm . . . !!!

Idan malamanmu na addini baza su yunkura ba wajen
samun wani malami zakakuri, mai zalaka da zai dinga
karanto 'SIRAH' ko dai wani littafin na daban mai dauke da
tarihin rayuwar Annabi (saw), iyalansa, sahabbansa da
yakokin da akayi don daukaka addinin Allah, domin maye
gurbin ko janye tunanin al'ummarmu daga wancan layin
na gangan, shirin da kullum yake gafalantar, shashantar,
dakilar, gurbatar da tunanin iyaye mata (musamman
matasan iyaye 'yan wajejen 25. . .30 . . .40 . . . haka).
Hakika shirin ya damfaru da zukatan al'ummar da a
matakin shekaru yakamata ace sun mai da kai tare da
bada himmarsu kacokan kan kalubalen da yake tunkararsu
kuma yake zame musu barazana a rayuwa wato samun
'SAHIHIYAR KO INGATACCIYAR TARBIYYAR
MUSULUNCHI da YAKIN NEMAN ILIMIN ADDINI DANA
BOKO domin aiki dashi ba don aikatau dashi ba (ina fatan
an gane bambancin aiki da aikatau).
Wasu lokutan baya Mal. Aminu Ibrahim Daurawa yayi wani
shirin tarihin sahabbai a Freedom FM, shirin ya samu
karbuwa sosai, akwai shirin Mal. Saminu Yakasai na 'AIKI
DA LURA' koda yake shirin yafi armashi da samun dimbin
masu sauraro lokacin da yake RAHAMA FM, kafin ya
sauya wajen aiki zuwa Wazobia FM. Ire-iren wadannan
malamai masu zalakar harshe da iya sarrafa shi irin na
wancan ISA mai shirin RAI DANGIN GORO, su yakamata su
kara yunkurowa da dimbin shirye-shiryen addini masu
kayatarwa don dasa tarbiyya da yad'a ilimi ga miliyoyin
al'ummar da shirin RAI DANGIN GORO ya d'amfaru kuma
yake kara cigaba da samun tasiri a zukatansu, gaskiya
al'umma sun jefar da GASKE sun rungumi GAN-GAN. Kada
kuso kuga yadda shirin ke sanya matasa rawar jiki da
dauki a kowacce safiya.
Duk mai sanya idanu akan iyalansa da mai sanya kunnuwa
ga hirarrakin da matan gidajenmu da yaranmu matasa
mazansu da matansu, zaiji yadda suke haddace sidira
bayan sidira, shafi bayan shafi na littafin GAN-GAN da ake
karantowa a shirin RAI DANGIN GORO na karfe 9:30 -
10:00 na kowacce safiya a wata kafar watsa labarai dake
zangon FM.
HATTARA DAI MAGIDANTA, AIKACE-AIKACEN GIDA SUNA
SAMUN TAZGARO A WANNAN LOKACIN.
Kuma wani abin takaici shine, akwai shirin addinin
musulunchi na Dr. Aliyu Isa Fantami da yake biyo bayan
shi wancan watsattsen shiri na RAI DANGIN GORO da
misalin 10:00, wato da zarar 10:00 tayi dai-dai da fara
sauraron Dr. Fantami sai kaga gayyar sauraron RAI
DANGIN GORO ta watse, wasu kuma kashe radio ma suke
kwata-kwata.
KAI CO ! KAI CO !! KAI CO !!!


DAN SOCIAL MEDIA TAMBAYI KANKA 001!!!(Jibwis Kaltungo)
.
ya kamata duk wani dan social media ya tambayi kanshi
cewa: wane gudumawa nake bawa musulunci a social
media wanda bayan rayuwata musulunci zatayi kuka
saboda rashi na.
.
ya kamata kowa ya tambaya kanshi, a matsayinka na dan
social media Musulmi kuma Ahlussunnah ya kamata ace ka
tanadar da wani abu a social media wanda ko bayan
rayuwarka # LADA zaiyita samunka(sadakatuj jariya), kama
daga kirkirar Accounts, Groups, pages e. t. c. a facebook,
whatsapp, twitter, e. t. c.
.
ya kamata tun da sauran Rai a jikin mutum yayiwa kanshi
wannan tanadi kafin ace bayanan.
.
ko shakka babu akwai wasu mutane da suka bada
gudumawa sosai a social media wanda ko bayan ransu za'a
tuno su ayi musu addu'ar alkhairi, misali: Ustaz Ibrahim
Baba Suleiman wannan bawan Allah muna mishi
kyakkyawan zato bisa aiki da yake gudanarwa a social
media, ganin cewa shike jagorantar Committee na Social
Media na # Nigeria baki daya na Kungiyar # IZALA .
.
kuma ba lallai ne sai ka kirkiri groups da pages ba, Account
dinka kawai idan ka kiyaye ta ka yada ilimi ka cida
musulunci gaba, ba shakka akwai wadanda zasuyi maka
addu'ar alkhairi.
.
Muna rokon Allah ya karba mana kyakkyawan ayyukanmu,
wadanda mukayi kuskure kuma ya gafarta mana, ya kuma
bamu ikon kiyaye # Alkalaminmu wajen rubutu.
.
daga naku:
# Abu_Abdirrahman_Kaltungo
25/July/2015


SAKON JUMMA'A NA WANNAN SATI.

Yaku bayin Allah! Haqiqa Ma’aikin Allah (ﷺ) ya kasance yana cin moriyar ranar Juma’a ta hanyar aikata ayyuka na qwarai, ya kasance daga aikina shiriyarsa (ﷺ), girmama wannan rana da darajta ta, da kebantarta da wasu abubuwa na musamman, kamar karanta Surar (Alif lam mim Assajdat) da (Hal ata alal insani) a sallar Alfijir dinsa, saboda sun qunshi abin da ya kasance da abin da zai kasance a yininta.

Kuma yan daga cikin abubuwan da ta kebanta da su: an so yawaita salati ga Annabi (ﷺ) a daranta.

Imam Ibn Alqaiyim Allah ya jiqansa yana cewa:

"Manzo Allah shi ne shugaban halitta, kuma yinin Juma’a shi ne shugaban ranaku, don haka yin salati a gare shi a wannan rana yana da falala wadda babu irinta.

Tare da wata hikimar wadda ita ce: Kasancewar duk wani alheri da al’ummarsa ta samu a duniya da lahira ta same shi ne ta hannunsa.

Sai Allah ya tarawa al’ummarsa tsakanin alherin duniya da lahira, don haka mafi girman girmamawa za su samu za su same ta ne ranar Juma’a. Domin a ran nan ne za a tashe su zuwa gidaddajinsu da fadojinsu a cikin Aljanna. Kuma ranar Idi ce a gare su a duniya. Yinin da a cikinsa Allah Ta’ala yake taimakonsu da amsa addu’o’insu da buqatunsu. Kuma ba ya mai da hannun mai roqo fayau a cikinsu . Duk wannan kuwa sun san shi ne, kuma ya same su ne saboda shi, kuma ta hanyarsa. Don haka yana daga cikin biyan kadan daga cikin haqqinsa, mu yawaita salati a gare shi a wannan yini da darensa”
. Kuma ga shi Allah Ta’ala ya ce,
(56) [: 56]

“Haqiqa Allah da mala’ikunsa suna salati ga Annabi, ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati da sallama mai yawa a gare shi.”

Daga cikin akwai karanta sororin (juma’a) da (almunafiqun) ko (Sabbih) da (Algashiyah) daga ciki; akwai cewa mai tafiya zuwa gareta yana da ladan aiki na shekara, duk taku daya da yayi, duka da aminta, da tsayuwara daranta.

Daga ciki akwai cewa yana kankare zunubai.

Ya ku bayin Allah! Haqiqa yana daga ababuwan da shari’a ta kebanci wannan yini dashi cewa, a cikinta akwai wata sa’a da babu wani bawa musulmi da zai yi dace da ita, yana roqon Allah daga alherin duniya da lahira, face Allah ya amsa masa addu’arsa.

#Domin an ruwaito daga Abu Huraira (R.A) ya ce: Manzo Allah ya ce

“Haqiqa a cikin Juma’a akwai wata sa’a babu wani musulmi da zai yi dace da ita yana tsaye yana yin sallah, yana roqon Allah wani alheri, face sai ya ba shi”.

Ya yi haka da hannunsa yana alamta qarancinta (ma’ana ita sa’ar). Muslim ne ya rawaito shi.

Lallai wannan ta isa kyauta mai girma, kuma dama babba, baiwa gwaggwaba, wadda Allah yake buda qofofinsa ga bayinsa, don su roqe shi da ita.

#Hasararre shi ne wanda aka hana shi fallalr wannan yini da albarkar wannan sa’ar mai dinbin albarka, wadda take maimaituwa a gare mu a kowane sati. Kuma mafi rinjayen maganganu wajen tantance lokacinta shi ne, daga tsakanin La’asar zuwa faduwar rana.

#Domin An karbo daga Jabir (R.A) ya ce, Manzon Allah ya ce:

“Ranar juma’a sha biyu ce”: yana nufin sa’o’i, babu wani musulmi da za a samu yana roqon Allah mai girma da daukaka wani abu face Allah ya ba shi, don haka ku neme ta a qarshen lokaci bayan La’asar”.

Ya ku musulmi! Ku yi gasa a kan wannan alheri mai girma, wanda Allah ya sanya shi cikin ranar Juma’a ga wanda ya sunnanta da sunnan Annabi a cikin wannan, ku tsaftacce jukkunanku, ku sanya mafi kyawun tufafin ku, ku yi asuwaki, ku sanya turare, ku yi sammako don ku tafi sallar Juma’a, ku lazimci ladubban Annabi (ﷺ), da tsari na Muhammadiyya. Ku kasance daga masu rigaye zuwa alherai, masu rabauta da mafiya daukakar darajoji, (Wannan falala ce ta Allah da yake ba da ita ga wanda yaso, kuma Allah shi ne ma’abocin falala mai girma).

#Na ja kunnenku a kan qin halartar wannan alheri, da sakaci da wadannana sunnoni, domin ya zo a cikin sahihin hadisi:

"Wasu mutane ba su gushe ba suna jinkirta ta har sai Allah Ya jinkirta su”.

Ina neman tsari da Allah daga shadani abin la'annane.

Allah ka datar damu da dacewa daga Wannan Sa'a.

Abu Muh'd
27/03/2015


SAKON JUMMA'A NA WANNAN MAKO!!!

An karbo daga Anas ya ce,

"An bijiro da sallar Juma'a ga Manzon Allah (ﷺ). Mala'ika Jibrilu ne ya zo masa da ita a tafinsa kamar farin madubi, a tsakiyarsa akwai wani baqin digo, sai ya ce:

"Menene wannan ya jibrilu?"

Ya ce masa, "Wannan ita ce Juma'a Ubangijinka yake bijiro da ita a gare ka; domin ta kasance idi a gareka da alummarka a bayanka, kuma ku kuna da alheri a cikinta, wanda kai ne za ka zama na farkon samunsa, kuma yahuduwa da nasara su zama a bayanka.

#Kuma a cikinta akwai wata sa'a babu wani bawa da zai yi addu'a a cikinta ta alheri da yake rabonsa ne, face an ba shi, ko ya nemi tsari daga sharri face an ije masa mafi girma daga abin da ya nema,

kuma mu a sama muna ambatonsa ranar qari...".

Dabarani ne ya rawaito shi a cikin Al-Ausat da isnadi mai kyau .

Jumma'at Khareem...

Abu Muh'd
10/04/2015


SAKON JUMMA'AH NA WANNAN SATIN!!!

Bukhari da Muslim suka rawaito shi daga Abu Hurairata Allah ya qara yarda a gare shi cewa, Manzan Allah ya ce:

(Duk wanda ya yi wanka ranar Juma'a irin wankan janaba, sannan ya tafi a sa'a ta farko to kamar ya gabatar da rakuma ne (sadaka) har qarshan hadisin.
Kuma Hakim ya rawaito kuma ya inganta shi, daga Samrah dan Jundubi (R.A.) cewa, Annabin Allah ya ce:

"Ku halarto sallar Juma'a, kuma matso kusa da liman, domin mutum ba zai gushe ba yana nesa, har sai Allah ya jinkirta shi a cikin aljanna ko da ya shige ta".

Idan ya halarta ya shagala da ibada da bin ubangiji na daga sallah da zikiri da karatun Alqur'ani, har liman ya fito.

#Yayin da liman ya fito sai ya kasa kunne ya saurari huduba, sannan ya yi sallar da tsoron Allah da nutsuwa, da tuntuntuni a kan abin da ake karantawa a cikinta na zancan Allah mai buwaya da daukaka, yayin da ya idar da sallahr farillar sai ya shagala da zikiran da aka shar'anta bayan sallah.

#Kuma an sunnanta nafila mai raka'a hudu a cikin masallaci, ko kuma mai raka'o'i biyu a gidan sa, amma jinkirtata zuwa gida shi ya fi falala domin haka Annabi (ﷺ) ya yi. kamar yadda ya tabbata a cikin Bukhari da Muslimu.

Duk wanda ya kwadaitar bisa aikata haka kuma ya aiwatar da shi da ikhlasi, to ya cancanci ya sami falalar wannan rana mai albarka, kuma ya sami ladansa mai girma daga mai ni'ima mai karamci, domin haqiqa Annabi (ﷺ) ya ce:

“Wanda ya yi alwala kuma ya kyautata alwalar, sannan ya zo sallar Juma'a, sannan ya ji kuma ya saurara, za a gafarta masa abin da ke tsakaninsa, da wata Juma'ar (mai zuwa) har da qarin kwana uku.” Muslim ne ya rawaito shi a cikin Sahihinsa .

Abu Muh'd
01/05/2015


SAKON JUMMA'AH NA WANNAN SATI!!

Ya ku bayin Allah! Haqiqa shari'a ta yi hani bisa wasu al'amura da suke hana ladan Juma'a, ko tawayar ladanta,

#kamar jinkiri wajan tafiya zuwa gareta, har sai liman ya fito, da shagaltar da masu sallah ta hanyar tsatsallaka su, domin Annabi (ﷺ) ya ga wani mutum – lokacin da yake huduba- yana tsattsallaka mutane sai ya ce masa yana masa inkari,

"Ka zauna haqiqa ka cutar kuma ka wahalar". Kuma haqiqa ana jiye wa wanda ke aikata haka tsoron kada ya shiga dungumin fadin Allah, mabuwayi da daukaka:
(58) [: 58]

(Kuma wadannan da suke cutar da muminai maza da muminai mata ba tare da wani abu da (su muminan) suka aikata ba, to haqiqa sun dauki nauyin qire da laifi mai girma).

#Daga ciki: akwai uzurrawa bayin Allah ta hanyar daga murya da zikiri ko karatun Alqur’ani, haqiqa Manzon Allah (ﷺ) ya hana hakan, da fadinsa ga sahabbai yayin da suka daga muryarsu da qira'a:

"Kada sashinku ya baiyana karatun Alqur'ani a bisa sashi" .

#Mafi muni daga haka, idan wannan uzurrawar ta zamo da zance ne a kan lamarin duniya kurum, musamman ma ana cikin huduba, domin yana daga cikin hanawa mutum (dacewa), da qarancin basira mutum ya shagala ga barin huduba da zance, ko wasa, ko waninsa, har ladan Juma'a da falalarta su kubuce masa.

Haqiqa Annabi (ﷺ) ya fada wajan yin gargadi a kan haka: “Duk wanda ya shafi qasa a yayin huduba to ya yi wasa”. Muslim ne ya rawaito shi.

Kuma an rawaito daga Abu Hurairata (R.A.) cewa Manzon Allah (ﷺ) ya ce:

“Idan ka ce da sahibinka: yi shiru, ranar Juma'a alhali liman yana huduba to ka yi yasasshiyar magagana”.

Kuma Imam Ahmad ya rawaito daga Ali ya ce: Manzon Allah (ﷺ) ya ce:

"Duk wanda ya ce ga sahibinsa yayin da liman yake huduba: yi shiru to haqiqa ya yi yasasshiyar magna. Duk kuwa wanda ya yi yasasshiyar magana, to ba shi da ladan Juma'a".

Allah ka Tsaremu daga Asarar Ladan jumma'a.

Abu Muh'd
08/05/2015


SAKON JUMMA'A NA WANNAN SATI.

Ya ku bayin Allah! Haqiqa Manzon Allah ya tsananta wajan gargadi game da qin halartar sallar Juma'a ba tare da wani uzuri na shari'a ba, yana mai bayyana cewa, wanda ya aikata haka haqiqa ya bijirar da kansa ga kamuwa da cutar gafala ta barin Allah, da yin rufi a kan zuciyar sa, duk kuwa wanda Allah ya yi rufi a kan zuciyarsa to basirarsa za ta makance, kuma makomarsa ta munana, Muslim ya rawaito cewa, #Manzon Allah ya ce:

“Lallai mutane su daina qin halartar sallar Juma'a, ko kuwa lalle Ubangiji zai rufe zukatansu, sannan su kasance daga gafalallu”.

Kuma imam Ahmad ya rawaito da Isnadi kyakkyawa, da kuma Hakim, a cikin Sahihinsa daga Abi Qatadata (R.A) cewa, Manzon Allah (ﷺ) ya ce: “Wanda ya bar Juma’a sau uku ba tare da wata lalura ba, Allah zai yi zab'i a kan zuciyarsa”.

To ku ji tsoron Allah, ya ku bayin Allah, kuma ku san irin falala da rahamar da Allah ya yi a kanku, ku tsaya a kan umarninsa ku bar abubuwan da ya hana, ko kwa rabauta da aljannatansa, a ranar gamuwa da shi.

Abu Muh'd
15/05/2015


A TABBATARMA ALLAH SUNAYENSA DA SIFFOFINSA BA TAREDA YIN ILHADI ACIKINSU BA (Canzawa ko kamantawa ko korewa ko juyarwa).

Musulmi yana bada gaskiya da abinda Allah tabaraka Wata'ala ya siffanta kansa dashi ko ManzonSa (SAW) ya siffantashi dashi na Sunaye da Siffofi ba tare da canza ma'anarsu ba ko koresu ko kamatasu da na wani abin halitta kasashe-she gajiyayye, sannan kuma yana korema Allah ta'ala dukkan abinda ya korema kansa ko Manzonsa (SAW) ya kore masa na dukkan na'u'in tawaya ko nakasa ko gajiyawa a jumlace sannan kuma a ke'bance; saboda dalilai daga Littafin Allah da Sunnar Manzonsa (SAW).

Allah ta'ala ya bamu Labari acikin Littafinsa (Al-Qur'an) game da kansa, ya bayyana mana yana da sunaye da kuma siffofianta kamar haka:

"Kuma Allah yana da sunaye mafiya kyawu, ku kirayeshi/ro'keshi dasu, kuma ka rabu da wad'an da suke yin Ilhadi (canzasu, koresu ko juyar dasu daga ha'ki'kanin ma'anarsu), da sannu za'a sakanka masu da irin abinda suka kasance suna aikatawa."

{A'araaf aya ta 180}

Yana kuma fad'i a wani wuri daba:

"Kuce Allah ko kuce Ar-Rahmaan (mai Rahama) duk wandama dai kuka kira, to ha'ki'ka shi (Allah) yana da sunaye mafiya kyawu."

{Isra'i aya ta 110}

Daga cikin abinda ya siffanta kansa dashi tabaraka Wata'ala akwai fad'insa shi mai:
Ji ne, mai gani, masani, mai hikima, mai 'karfi, mad'aukaki, mabuwayi, mai tausasawa, mai godiya, mai ha'kuri, mai gafara, mai Rahama....

Sannan ya bamu Labari cewa yayi magana da Musa (AS), ya kuma dai-daita akan Al'arshinsa (daidaita irin wadda shi kad'ai ya barma kansa sani), ya kuma halitta Adam (AS) da hannunsa, kuma shi yana son masu kyautatawa (acikin bauta da Mu'amalarsu), ya kuma bamu labarin cewa ya yarda da Muminai, da makamantan wad'annan na siffofinsa na zati da kuma na aiki, kamar sakkowarsa zuwa saman duniya yayin da d'aya bisa ukun dare ya shud'e (1/3) dukkan wad'annan suna cikin Al-Qur'ani da ingantattun Hadisai.

Zamu d'ora idan Allah ya nufa......
16/9/1435AH.


Watarana Anje YAQIN UHUD Sai Ake Cewa Sahabbai An Kashe
ANNABI (S.A.W)

Sai Wata mata Mai Suna 'UMMU KALLABI' TaJi Labarin Sai Ta Zare Takobinta Ta Hau Kan Ingarman Dokinta Ta Zo Filin Yakin Tana mai Cewa:

"Ina ANNABI (S.A.W) ???"

Sai Aka Ce Mata:

"KUTILA ABUUKI"

Wato An Kashe Babanki.

Sai Ta Ce:

"LAN AS'ALAKA ABI ABIN"

Wato Ban Tambayeku Baba Na Ba.

Sai Suka Sake Cewa Ai Bayan Babanki Ma:

"Zaujiki Fulanun Kad Kutila"

Sai Ta Ce:

"Ban Tambayeku Miji Naba"

Ina Tambayarku Ina ANNABI (S.A.W) ???

Sai Suka Sake Ce Mata:

"ABUUKI FULAMIN KATKUTILA"

Sai Ta Ce:

"LAN AS'ALUKA ABI ABIN WA AN ZAUJI WA AN AKHI WALAKIN AS'ALAKA AN RASULULLAH (S.A.W)"

Sai Suka Ce Mata:

"Idan Zaki Iya Kije Can Ga ANNABI (S.A.W) An Kewaye Shi An Sassare Shi".

A Hakan UMMU-KALLABI Ta Tafi Kafin Ta Isa Wurin Da ANNABI (S.A.W) Yake Sai Da AkaYi Mata Sara Da Suka Sau 12 a Jikinta.

Da Zuwanta Wurin Da ANNABI (S.A.W) Yake Sai Ta Ce:

"KULLU MUSIBATIN JA'ABADAKA JALALU"

MA'ANA:-

"Duk Wani Bala'i Idan Zai Zo In Dai Bai Taba Min Kai Ba To Mai Sauqi Ne a Waje Na".

SALLALLAHU ALAIHI WA SALLAAM!
YA ALLAH KABAMU IKON JAJIRCEWA DA JURE DUK WATA WAHALA AKAN SOYAYYAR SAYYIDUNA MUHAMMAD RASULULLAH (S.A.W).


Wata rana wani munafikin musulmi sukayi rigima da wani kafiri, har abin yakaisu ga shari'ah a wajen manzon Allah (s.a.w).

Ya tambayi kowannensu, kunsan Annabinmu akwaishi da Adalchi, daya gane kafirinnan shine yakeda gaskiya sai yabashi gaskiyarsa ya sallamesu.

Suna tafiya sai munafikinnan yace bai yarda da shari'ar nan da Annabi yayi musuba, aje wajen sayyadina Umar (R.A).

Suna isa gidan Umar Dan Khaddabi suka fada masa batun shari'arsu.

Saishi wannan kafirin yacewa Umar.

Munje wajen manzon Allah yabani gaskiya amma yace bai yarda ba azo wajenka.

Amirul Muminina yace su jirashi yana zuwa yana shiga gida yadauko takobi yasare kan wannan munafiki dabai yarda da shari'ar Manzon Allah ba.

Allahu Akbar !

Kaji magabata abin koyi.

Allah kaqara yarda a gareshi.

Ya Allah ka rabamu da munafunci, ka tsarkake zukatanmu.


SHIN KASAN CEWA SAYYIDUNA MU,AWUYYA DAN ALJANNA NE ?.

KASHI NA DAYA

ﻭﺻﻼﺓ ﻭﺳﻠﻢ ﻋﻠﻰ ﺭﺳﻮﻝ ﻟﻠﻪ .

HAQIQA SAYYIDUNA MU,AWUYYA DAN GIDAN ABU SUFIYAN DA GA S.HINDU <RD> DAN ALJANNA NE .

KUMA BISA DALILI NA AYA DA HADISI.

KAFIN IN,FARA ZANYI WANI DAN TANBIHI AKAN WANGA KALMA

ﺍﻟﺼﺤﺎﺑﻲ

SABODA NAGA WASU BASU SAN MAI AKE NUFI DA ITA BA.

TO HAQIQA MALAMIN MUSULUNCI ALITTAFINSA YA BAMUBAYANI

ﻫﻮ ﻣﻦ ﻟﻘﻲ ﺍﻟﻨﺒﻲ >ﺹ <ﻣﺆﻣﻨﺎﺑﻪ
ﻭﻣﺎﺕ ﻋﻠﻰ ﺍﻹﺳﻼﻡ . } ﺍﻹﺻﺎﺑﺔ 1/10 }

KAGA KENAN S.MU,AWUYYA YANA CIKI.TO BARI MUJI MAI ALLAH YACE AKAN SU MU,AWUYYA <SAHABBAI>

ﻓﻲ ﺳﻮﺭﺓ ﺍﻟﺘﻮﺑﺔ٨٩، ٨٨

ﻟﻜﻦ ﺍﻟﺮﺳﻮﻝ ﻭﺍﻟﺬﻳﻦ ﺀﺍﻣﻨﻮﺍ ﻣﻌﻪ ﺟﻬﺪﻭﺑﺄﻣﻮﺍﻟﻬﻢ ﻭﺃﻧﻔﺴﻬﻢ ﻭﺃﻭﻟﺌﻚ ﻟﻬﻢ ﺍﻟﺨﻴﺮﺍﺕ ﻭﺍﻭ ﻟﺌﻚ ﻫﻢ ﺍﻟﻤﻔﻠﺤﻮﻥ .

ﺍﻋﺪﺍﻟﻞﻩ ﻟﻬﻢ ﺟﻨﺖ ﺗﺠﺮﻱ ﻣﻦ ﺗﺤﺘﺤﺎ ﺍﻷﻧﻬﺮ ﺧﻠﺪﻳﻦ ﻓﻴﺤﺎ ﺫﻟﻚ ﺍﻟﻔﻮﺯﺍﻟﻌﻈﻴﻢ .

TO ALLAH YANACEWA SAI DAI CEWAR
MANZONSA TARE DAWADAN DA SUKAYI IMANI DA SHI KUMA SUKAYI JIHADI DA DUKIYOYINSU DA KAWUNANSU TO HAQIQA SUNA DA
ALKHAIRI KUMA HAQIQA SUNE MASU RABAUTA KUMA ALLAH YAYI MUSU TANADI NA ALJANNAH WACCE QORAMAI KE GUDANA ACIKINTA KUMA SUNA MASU DAWWAMA
ACIKINTA WANNAN SHINE RABO MAI GIRMA.

TO TABBASA SAYYIDUNA MU,AWUYYA YANA DAYA DAGA CIKIN WADANNAN MUTANE. KAGA KENAN DAN ALJANNA NE DA FADIN ALLAH <S.W.A> KUMA GA SHI MA,AIKI YANA FADA CIKIN

ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ٢٩٢ ﻭﺍﻟﺒﺪﺍﻳﺔ ٥ /٦٢٩

ﻗﺎﻝ > ﺹ < ﺃﻭﻝ ﺟﻴﺶ ﻣﻦ ﺃﻣﺘﻲ ﻳﻐﺰﻭﻥ ﺍﻟﺒﺤﺮ ﻗﺪ ﺍﻭ ﺟﺒﻮﺍ ﻭﺍﻭﻝ ﺟﻴﺶ ﻣﻦ ﺍﻣﺘﻲ ﻳﻐﺰﻭﻥ ﻣﺪﻳﻨﺔ ﻗﻴﺼﺮ ﻣﻐﻔﻮﺭﻟﻬﻢ .

ﻗﺎﻝ ﺍﺑﻦ ﺍﻟﺤﺠﺮ : ﺍ ﻗﺪ ﺍﻭﺟﺒﻮ ﺍﻱ ﻓﻌﻠﻮﺍ ﻓﻌﻼ ﻭﺟﺒﺖ ﻟﻬﻢ ﺑﻪ ﺍﻟﺠﻨﺔ .١٠٣

MA,AIKI YACE FARKON RUNDUNAR DAZATA FARA YAQI TACIKIN KOGI TO HAQIQA TAWAJABA AGARE SU < ALJANNAH > KUMA FARKON RUNDUNAR DATA YAQI GARIN
QAISARA TO ANGAFARTA MUSU.

TO KUMA WADANNAN YAQIN HARDA
MU,AWUYYA ZAKA IYA KOMAWA
FATAHULBARIY KAGANI.

SHIN KASAN ANNABI YASAN ZASUYI RIKICI SHI DA SU SAYYIDUNA ALIYU DA SAYYIDUNA AMMAR AMMA KUMA
YACE ZASU SHIGA ALJANNAH KUMA KOMAI ZASUYI ANGAFARTA MUSU ?

TO SHIN BAKA BIYAYYANE GA MA,AIKI ?

TO HAR,INDAI KANA BIYAYYA TO CENE MUSU YAN,ALJANNA KUMA WADANDA AKA GAFARTAWA.

IDAN KUMA KAKARANTA TARIHI NE KO WANI ABU KAGA LAIFIN WANI TO KATUNAFA ANGA FARTAMUSU.

KO KUMA KAKAME BAKIN KA KAMARYAN DA YAYI UMARNI.
ZAMUCI GABA


SHIN KASANCEWA SAYYIDUNA MU,AWUYYA DAN ALJANNANE ??.

KASHI NA BIYU.

ﻭﺻﻼﺓ ﻭﺳﻠﻢ ﻋﻠﻰ ﺧﻴﺮﺧﻠﻖ > ﻣﺤﻤﺪ ﺹ < ﻭﻋﻠﻰ ﺍﻟﻪ ﻭﺃﺻﺤﺒﻪ ﺍﺟﻤﻌﻴﻦ .

ACIGABAN KARATUN MU WANDA KE NUNI DA KASANTUWAR SAYYIDUNA MU,AWUYYA DAN GIDAN S.HINDU DAGA S.ABU SUFIYAN {RD}.

KASHI NA BIYU.

YAU ZAMU DORA BADAN KOMAI BA.

SAI DAN NASIHA GA YAN UWA MASU ILIMI DA HANKALI WAJEN SUGUJI FADAWA IRIN WANGA MASIFA TA ZAGIN MASU HIDIMA GA MA,AIKI { S.A.W } SHAIDA TAFARKO DAGA MANZON ALLAH S.A.W. YANA CEWA.

ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻋﻠﻢ ﻣﻌﺎﻭﻳﺔ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺤﺴﺎﺏ ﻭﻗﻪ ﺍﻟﻌﺬﺍﺏ . >

ﺍﺣﻤﺪ ٤ /١٢٧ ﻭ ﻓﻀﺎﺋﻞ ﺍﻟﺼﺤﺎﺑﺔ ١٧٤٨ ﻭﺍﻟﻄﺒﺮﺍﻧﻲ ﻓﻲ
ﺍﻟﻜﺒﻴﺮ ١٨ /٦٢٨ ﻭﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ﻓﻲ ﺗﺎﺭﻳﺨﻪ ٧ /٣٢٦ ﻭﺍﺑﻦ ﺧﺰﻳﻤﺔ
١٩٣٨ ﻭﺍﻟﻬﻴﺜﻤﻲ ٩ /٣٥٦ ﻭﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ ﺹ ٣٢٢٧ .

TO MA,AIKI GASHI DAKANSA YANA NEMAN ALLAH DA YASANAR DA SAYYIDUNA MU,AWUYYA ILIMIN
ALQUR,ANI DA KUMA IYA LISSAFI.

KUMA YATSARESHI AZABAR WUTA.

KAGA KUMA WALLAHI ALLAH YA,ANSHI WANGA ROQO NA MA,AIKI.

KAGA INMUKAJIKA KANACEWA SAYYIDUNA MU,AWUYYA DAN WUTANE TO BADAMU KAKEJAYAYYA BA DA MA,AIKI KAKE.

INKA KASANCE MAI QAUNA GA MA,AIKI TO KAME ABIN SALATINKA .

TO GAKUMA WATA SHEDAR DAGA WAJEN ALLAH.

ﻓﻲ ﺳﻮﺭﺓ ﺍﻟﺤﺪﻳﺪ ﺍﻳﺔ ١٠ -

ﻻﻳﺴﺘﻮﻱ ﻣﻨﻜﻢ ﻣﻦ ﺍﻧﻔﻖ ﻣﻦ ﻗﺒﻞ ﺍﻟﻔﺘﺢ ﻭﻗﺘﻞ ﺍﻭﻟﺌﻚ ﺍﻋﻈﻢ ﺩﺭﺟﺔ ﻣﻦ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﺍﻧﻔﻘﻮﺍ ﻣﻦ ﺑﻌﺪ ﻭﻗﺘﻠﻮ ﻭﻛﻼ ﻭﻋﺪﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺤﺴﻨﻰ ....

ALLAH YANA GAYAWA SAHABBAI CEWAR BAZASU TABA ZAMA DAIDAI BA DAWADANDA SUKACIYAR KAFIN FATAHU MAKKAH KUMA SUKAYI JIHADI ,WADANCHAN SUNE MAFI
DARAJA AKAN WADANDA SAI BAYAN FATAHU MAKKAH SUKAYI JIHADI DA KUMA CIYARWA, TO AMMA DUKKANSU ALLAH YAYIMUSU
TANADI MAI KYAU <ALJANNAH>

ﻭﻗﺎﻝ ﻣﺠﺎﻫﺪ ﻭﻗﺘﺎﺩﺓ >ﺍﻟﺤﺴﻨﻰ .:ﺍﻟﺠﻨﺔ <. ﺗﻔﺴﻴﺮ ﺍﺑﻦ
ﺟﺮﻳﺮ ٢٧ /١٢٨ ﻭﺍﺳﺘﺪﻝ ﺍﺑﻦ ﺣﺰﻡ ﻣﻦ ﻫﺬﻩ ﺍﻻﻳﺔ ﺑﺎﻟﻘﻄﻊ
ﺑﺄﻥ ﺍﻟﺼﺤﺎﺑﺔ ﺟﻤﻴﻌﺎ ﻣﻦ ﺍﻫﻞ ﺍﻟﺠﻨﺔ }ﺍﻟﻔﺼﻞ ٤ /١٤٨ - ١٤٩ }

MALAN MUJAHID DA QATADA DA IBN HAZIM DUKANSU SUNKAFA HUJJA DA WANGA AYAR AMATSAYIN DALILI AKANCEWAR DUKKAN SAHABBAI YAN ALJANNA NE..

TO KUMA YATABBATA SAYYIDUNA MU,AWUYYA YABAYYANA MUSULUNCINSA NE A ASHEKARAR BUDE MAKKAH

{ ﺗﺎﺭﻳﺦ ﺍﻹﺳﻼﻡ ﻟﻠﺬﻫﺒﻲ _ﻋﻬﺪ ﻣﻌﺎﻭﻳﺔ
٣٠٨ }

TO KAGA KENAN YANA DAYA DAGA CIKIN WADANDA ALLAH YAYI MUSU TANADI NA ALJANNAH.

KUMA MASUCEWA SAYYIDUNA MU,AWUYYA KAFIRI NE KO MUNAFUKI NE KO FASIQINE TO DA ALLAH SUKE RIGIMA.

DAN ALLAH YANA FADA CIKIN.

ﺳﻮﺭﺓ ﺍﻟﺤﺠﺮﺓ ﺍﻳﺔ ٧ .

ﻭﻟﻜﻦ ﺍﻟﻠﻪ ﺣﺒﺐ ﺇﻟﻴﻜﻢ ﺍﻷﻳﻤﻦ ﻭﺯﻳﻨﻪ ﻓﻲ ﻗﻠﻮ ﺑﻜﻢ ﻭﻛﺮﻩ ﺇﻟﻴﻜﻢ ﺍﻟﻜﻔﺮ ﻭﺍﻟﻔﺴﻮﻕ ﻭﺍﻟﻌﺼﻴﺎﻥ ﺍﻭ ﻟﺌﻚ ﻫﻢ ﺍﻟﺮﺍﺷﺪﻭﻥ .

KAGA ALLAH YANACEWA YASANYA MUSU QAUNAR IMANI KUMA YAQAWATA MUSUSHI AZUKATANSU YAKUMA SANYA MUSU QIN KAFIRCI DA FASIQANCI DA SABAMASA .KUMA
YACE SUNE SHIRYAYU.

KAI KUMA KANA BAHAKA BA TO DA SHI KAKE RIGIMA.

ZAMU CIGA BA.


SHIN KOKASAN CEWA SAYYIDAUNA MU,AWUYYA DAN ALJANNA NE ???

KASHI NA UKU.

ﺍﻟﺤﻤﺪﻟﻠﻪ ﻭﺻﻼﺓ ﻭﺳﻠﻢ ﻋﻠﻰ ﺭﺳﻮﻝ ﻟﻠﻪ .

ACIGABAN KAWO DALILAI NA,AYOYI DA KUMA HADISAI DAKE NUNI DA KASANTUWAR ZAMOWAR S. MU,AWUYYA .RD. A GIDAN
ALJANNAH.

TO YAU ZAMU CIGABA.

DAGA INDA MUKA TSAYA.

ﻋﻦ ﻳﺰﻳﺪ ﺑﻦ ﺍﻟﻌﺴﻢ ﻗﺎﻝ .:ﺳﺌﻞ ﻋﻠﻲ ﺑﻦ ﺍﺑﻲ ﻃﺎﻟﺐ > ﺭ < ﻋﻦ ﻗﺘﻠﻰ ﺻﻔﻴﻦ . ﻓﻘﺎﻝ ﻗﺘﻼﻥ ﻭﻗﺘﻼﻫﻢ ﻓﻲ ﺍﻟﺠﻨﺔ ﻭﻳﺴﻴﺮ ﺍﻷﻣﺮ ﺇﻟﻲ ﻭﺍﻟﻰ ﻣﻌﺎﻭﻳﺔ .

>ﺍﺑﻦ ﺍﺑﻲ ﺷﻴﺐ ٣٩٠٣٥ >

ANTANBAYI S.ALIYU DANGANE DA YAQIN DA YAFARU A SUFYIN TSAKANINSA DA DAN UWANSA S. MU,AWUYYA NAGAME DA WADANDA
AKAKASHE ACIKIN YAQIN SAI S. ALIYU YAKE CEWA WADANDA AKAKASHE DAGA CIKIN MU DA WADANDA AKA KASHE DAGA CIKIN SU S. MU,AWUYYA DUKA YAN ALJANNA NE.

KUMA HAKA WANNAN YAKE AWAJEN S. MU,AWUYYA <SHIMA RA,AYINSA KENAN.> TO KAI DAN UWA KAJI ABINDA S. ALIYU YAKE FADI SHI AGURI NAI BAIKALLON SU S. MU,AWUYYA AMATSAYIN DAKAKE DAUKARSA NA <kafirci ko fasiqanci >DANNASAN DAI BAKAFI S. ALIYU SANIN NASSI BA TO SHI BAIYI IRIN WANCHAN FAHIMTA DA KAYI BA SHI
YAFAHIMCI DUKKANSU IJTUHADI NE KUMA YASAN DUKKAN ABINDA SUKA AIKATA ALLAH YAYAFEMUSU TUNDA ANNABI YANEMA MUSU GAFARA KAMAR HAKA.

ﺳﻮﺭﺓ ﺍﻝ ﻋﻤﺮﺍﻥ ٧ :-

ﻭﻟﻮ ﻛﻨﺖ ﻓﻈﺎ ﻏﻠﻴﻆ ﺍﻟﻘﻠﺐ ﻻﻧﻔﻀﻮﺍ ﻣﻦ ﺣﻮﻟﻚ ﻓﺎﻋﻒ ﻋﻨﻬﻢ ﻭﺍﺳﺘﻐﻔﺮﻟﻬﻢ ﻭﺷﺎﻭﺭﻫﻢ ﻓﻲ ﺍﻷﻣﺮ .

DAKA KASANCE MAI KAUSHIN HALI <ANNABI S.A.W.> DA SUN WATSE
<SUNRABU DAKAI > TO KAIYI MUSU AFUWA KUMA KANEMA MUSU GAFARA KUMA KANEMI SHAWARARSU ACIKIN AL,AMURA.

TO KAI KAJI ABINDA ALLAH DAKAI NAI YAKE FADI YANA UMARTAR MA,AIKI DA YAYIMUSU AFUWA KUMA YADINGA NEMA MUSU GAFARA AKAN LAIHUKANSU DASUNKA AIKATA TO KAI KANAJIN ALLAH BAI YAFEMUSU KOMAI SUNKA AIKATA ?

KUMA YACI YADINGA NEMAN SHAWAR AGURINSU, TO KAI KANAJIN ALLAH ZAICE MA,AIKI YADINGA NEMAN SHAWARAR ARNA KO KAFIRAI FASIQAI ?

TO WALLAHI SU SAYYIDUNA MU,AMUYYA MUTANAN KIRKI
NE TUNDA ALLAH YAGAFARTA MUSU. KUMA YAYI MUSU ALQAWARI NA ALJANNAH KAMARHAKA.

ﺳﻮﺭﺓ ﺍﻟﻔﺘﺢ ٢٩ :-

ﻭﻋﺪﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﺀﺍﻣﻨﻮ ﺍ ﻭﻋﻤﻠﻮ ﺍ ﻟﺼﻠﺤﺖ ﻣﻨﻬﻢ ﻣﻐﻔﺮﺓ ﻭﺃﺟﺮﺍ ﻋﻈﻴﻤﺎ .

TO ALLAH YAYI WA SU S.MU,AWUYYA
ALQAWARIN ALJANNA SABODA SUNYI IMANI KUMA SUNYI AIKI NAQWARAI KUMA YAYI MUSU GAFARA DA KUMA TANADI NA LADA MAIYAWA.

TO KAI KANA CEWA FASUQAINE SU.

KAGA KENAN DA ALLAH KAKE RIGIMA.

SABODA SU S. MU,AWUYYA ALLAH YACE MUSU MUMINAI NE SU MA,AIKI MA YACE MUSULMAINE KUMA MANYAMA ACIN MUSULMAN. KAGA .

ﺳﻮﺭﺓ ﺍﻟﺤﺠﺮﺍﺕ ٩ :-

ﻭﺇﻥ ﻃﺎ ﺋﻔﺘﺎﻥ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﺆﻣﻨﻴﻦ ﺍﻗﺘﺘﻠﻮﺍ ﻓﺄﺻﻠﺤﻮﺍ ﺑﻴﻨﻬﻤﺎ ...

TO KAJI DAI ALLAH YANA BAMU LABARIN YAQIN DA,AKAYI TSAKANIN SAYYIDUNA ALIYU DA DAN UWANSA SAYYIDUNA MU,AWUYA YANACEWA IDAN RUNDUNAR MUMINAI GUDA BIYU SUNA YAQI TO KUDAI DAITA TSAKANINSU.

A BAKU DINGA TSINEWA DAYAN BARIN BA A,KUCE ALLAH YAQARAMUSU YARDARSA
DAKUMA GAFARARSA WADAYA YACE ZAI MUSU.

TO ALLAH YAQARA YARDA DA SU GABADAYA.

ZAMUCI GABA.


SHIN KASANCEWAR SAYYIDUNA MU,AWUYYA DAN ALJANNA NE ?

KASHI NA HUDU

SHIN ZAKA IYA YIMUSU HUKUNCI ?

ﺍﻟﺤﻤﺪﻟﻠﻪ ﻭﺻﻼﺓ ﻋﻠﻰ ﺭﺳﻮﻝ ﻟﻠﻪ .

HAQIQA ACIGABADA KAWO DALILAI NA ALQUR,ANY DA KUMA INGANTACIYAR SUNNAR MA,AIKI AKAN KASANTUWAR ZAMANTOWAR
S.MU,AWUYYA DAYA DAGA CIKIN YAN
ALJANNAH TO YAU ZAMU KAWO WANI DALILI DA ZAMU NEMI WANDA ZAI IYA
WARWAREMANA SHI.

MUTUQAR ZAKA ZARGI S.MU,AWUYYA TO ZAKA ZARGI S.ALI <R.A.>.

HAQIQA DUKKAN WANDA YAKASANCE MAI QAUNAR MA,AIKI TO YAYARDA DA MAGANAR MA,AIKI INDA YAKECEWA .

ﻭﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﻣﻮﺳﻰ . ﺭ . ﻋﻦ ﺍﻟﺤﺴﻦ .ﺭ . ﺃﻥ ﺍﺑﺎﺑﻜﺮﺓ . ﺭ . ﻗﺎﻝ ﺳﻤﻌﺖ ﺍﻟﻨﺒﻲ . ﺹ . ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻤﻨﺒﺮ ﻭﺍﻟﺤﺴﻦ ﺇﻟﻰ ﺟﻨﺒﻪ ﻳﻘﻮﻝ ﺇﺑﻨﻲ ﻫﺬﺍ ﺳﻴﺪ ﻭﻟﻌﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﺃﻥ ﻳﺼﻠﺢ ﺑﻪ ﺑﻴﻦ ﻓﺌﺘﻴﻦ ﻋﻈﻴﻤﺘﻴﻨﻲ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﺴﻠﻤﻴﻦ .

> ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ٣٧٤ >.

TO TABBAS MA,AIKI .S.A.W. YACE WANNAN DAN NAWA SHUGABANE MAIYUWUWA ALLAH YASANYA YAZAMA WANDA ZAI SULHUNTA
TSAKANIN MANYA MANYAN BANGARORIN MUSULMAI GUDA 2.

TO HAQIQA KUMA HAKANTAFARU S.HASSAN YAZAMA SANADI NA SULHUNTA, JAMA,AR S.MU,AWUYYA DA S.ALIYU WANDA AKAYI YAQIN
SAFIN DA SU.

HAKAN KENUNA CEWAR SAYYIDUNA MU,AWUYYA YANA DAYA DAGA CIKIN MANYA MANYAN MUSULMAI YANGABA ACIKINSA DAFADAR MANZON ALLAH .S.A.W. KAGA CEWAR KACE MASA KAFIRI KO WANI ABU MAI KAMA DA HAKA TO RIGIMACE DA MA,AIKI.

KU MA ALLAH YAYI MASA DA SHI DA
DAN,UWANSA S.ALIYU SHAIDA DA CEWAR SU MUMINAI NE.

KAMAR.

ﻭﺇﻥ ﻃﺎﺋﻔﺘﺎﻥ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﺆﻣﻨﻴﻦ ﺍﻗﺘﺘﻠﻮﺍ ... >ﺍﻟﺤﺠﺮﺍﺕ ٩ >

KAGA KENAN DOLE KA SALLAMA .

IDAN KAQI TO YI MANA HUKUNCI ANAN...

MA,AIKI DAIYA CE.

ﺇﺫﺍ ﺍﻟﺘﻘﻰ ﺍﻟﻤﺴﻠﻤﺎﻥ ﺑﺴﻴﻔﻴﻬﻤﺎ ﻓﺎﻟﻘﺎﺗﻞ ﻭﺍﻟﻤﻘﺘﻮﻝ ﻓﻰ ﺍﻟﻨﺎﺭ .

> ﻣﺴﻠﻢ ﻭﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ ﻭﺍﺣﻤﺪ >

TO MANZON ALLAH {S.A.W} YACE IDAN MUSULMAI GUDA BIYU SUKA HADU DATAKUBBANSU <sukayaqi juna > DA WANDA AKA KASHE DA MAI KISAN TO DUKKANSU YAN WUTANE.

TO YARAGE GAREKA.

KOWA YASAN YANDA TAFARU.

DOLE KATSAYA KAMAR YANDA MAI YAFADA.

ﺍﻟﻐﻨﻴﺔ . ﺹ .١١٢ >

ﻗﺎﻝ >ﺹ < ﺇﺫﺍ ﺫﻛﺮ ﺃﺻﺤﺎﺑﻲ ﻓﺄﻣﺴﻜﻮﺍ .
ﻭﻓﻲ ﻟﻔﻆ ﻭﺇﻳﺎﻛﻢ ﻭﻣﺎﺷﺠﺮ ﺑﻴﻦ ﺃﺻﺤﺎﺑﻲ ...

TO KAJI SHAWARAR MA,AIKI DA JILANY YAHAKAI TO MANA.

KAWAI MUKAME BAKU NAN MU MUBI UMARNIN ALLAH SANNAN DA NA MA,AIKI.

ﻭﺍﻟﺬﻳﻦ ﺟﺎﺀﻭﺍ ﻣﻦ ﺑﻌﺪﻫﻢ ﻳﻘﻮﻟﻮﻥ ﺭﺑﻨﺎ ﺍﻏﻔﺮﻟﻨﺎ
ﻭﻹﺧﻮﺍﻟﻨﻨﺎﺍﻟﺬﻳﻦ ﺳﺒﻘﻮﻧﺎ ﺑﺎﻹﻳﻤﺎﻥ >.... ﺍﻝﺣﺸﺮ ١٠ >

TO KAI KAJI FA A CEWA ZAKAYI ALLAH YAGA FARTAMUSU.

INKAFADI KOMA BAYAN HAKA TORIGIMA KAKE DANASSI.

DAN HAKA KAKIYAYI KANKA DA CIN MUTUNCIN KAWUN MUMINAI *{ SAYYADUNA MU,AWUYYA DAN ABOU SUFIYAN DA GA SAYYADATUNA
HINDU R.A.}*


SHIN KASANCEWA SAYYIDUNA MU,AWUYA DAN ALJANNA NE ????

KASHI NA BIYAR.

الحمد لله رب العالمين. و الصلاة والسلام على سيد محمد وعلى آله و أصحبه اجمعين.

ACIGA BA DA KAWO DALILAI NA ALQUR,ANI DA KUMA HADISAN MA,AIKI <S.A.W.> DA MAGANGANU NA MAGABATA NA QWARAI AKAN KASANTUWAR ZAMANTOWAR S.MU,AWUYA <R.A.> DAN ALJANNA NE YAU ZAMU DORA A,INDA MUKA KWANA.

ALALHAQIQA HADISI YAGWADAMANA FALALA MAI GIRMA GAWANDA YAYI YAQI DAN DAUKAKA KALMAR ALLAH HAR MA,AIKI YAKE YIMASA BUSHARA DA CEWA

وعن ابي عبس عبدالرحمن بن جبر <ر> قال.قال رسول الله <ص> ما اغبرت قدما عبد في سبيل الله فتمسه النار. <البخاري >

TO LALAI MA,AIKIN ALLAH YANA CEWA QAFAR BAWA <DUGADUGAN >BAZASUYI QURABA AKAN TAFARKIN ALLAH <JIHADI> KUMA WUTA TA SHAFESHI.

ALLAHU AKHBAR, TO INDAI KUWA HAKANE TO S.MU,AWUYA KO QANSHIN WUTA MA BAZAI JIBA DOMIN SHI NE WANDA YAHADA RUNDUNA TA YAQI DOMIN AJE AKAI SAQON ALLAH HARGARIN مدينة قيصر. KUMA MA,AIKI DAMAN YAFADA WADANDA ZASUYI WANGA AIKI TO مغفورلهم ANGAFARTA MUSU KO MA CIKIN فتح الباري /٦/١٢٠
KASHA QARIN BAYANI KO البداية والنهاية ٥/٦٢٩،٦٣٠

TO KAGA KENAN MA,AIKI YABASHI SHAIDA TA CEWAR YAFI QARFIN WUTA TA SHAFESHI. bani na fada ba ANNABI NE <S.A.W.> YADADA .

TO KAGA KENAN TSINEMASA KO ZAGIN SA KO KAFIRTA SHI KUSKURE NE MAI GIRMA. KO MAI WANI ZAIFADA MA AKAN SA TO KADAI JI MAGANAR MA,AIKI AKAN SA.

KAI DAN UWA HARMA FA MAHAIFINSA YASHIGA CIKI WUTA BAZATA SHAFESHI BA DAN SHIMA YAJE YAQI ALOKACIN MA,AIKI HAR,AKAYI MASA RAUNI <CIWO> AKAN DAUKAKA KALMAR ALLAH . WATO S.ABOU~SUFIYYAN <R.A.> DOMIN MALAN NASURU KABARA <R> YABADA LABARIN WANNAN QADIYYA CIKIN ألفية السيرة .ص.. ٧١
YAKECEWA

وفقئت عين أبي سفيانا ~صخر بن حرب ولقد أتانا ~ ان فقئت اخراه باليرموك ~ سعدك يا نفس إذا رضوك ~ في جنة تسوى له عينان....

M.NASURU KABARA YA YANACEWA HAQIQA IDANUN S.ABOU SUFIYAN <R> ANCIRETA NE AYAQIN DA,IFA DAYAN NABIYUN A YARMUKA AKA CIRE SHI YAKE CEWA JINDADIN KI YAKE RAI TA <ABOU SUFIYAN MAHAIFIN SAYYIDUNA MU,AWUYA <R.A.> LOKACIN DA ZA,ADAWO MUKI DA SU ABIKIN ALJANNA.

TO KAGA KENAN MALAN YA DUBA NUSUS NA NASSI INGANTATTU SHI YASA YAYI WANGA IRIN FURUCI.

KUMA ASHAFI NA 113 YAKE CEWA WANNAN SHI NE MAZAHABIN SHEHU ABDULQADIR JILANY <R> KAGA KENAN SABAWA WADANNAN DALILAI SABAWA ALLAH NE DA KUMA MA,AIKI <S.A.W.> KAGA KENAN DAN UWA YIN SHIRU AKAN ABINDA YAFARU AJUNANSU <SAHABBAI> SHI NE TSIRA ADUNIYA DA KUMA LAHIRA.



KU ISAR MIN DA SAKONA KO DA AYA GUDA CE"

*TSARABATA GAREKU*

Ibn Qayyumul Jauziy ya fada cewa

ABU 4 SUNA CUTAR DA JIKI

1- yawan magana
2- yawan barci
3- yawan jima'i
4- yawan cin abinci

ABU 4 YANA RUGUZA JIKI

1- bakin ciki
2- bacin rai
3- rashin barci
4- yunwa

ABU 4 YANA JANYO ARZIKI

1- yawan istigfari
2- tsayuwar dare
3- yawan sadaka
4- Zikirin safiya da yammaci

ABU 4 YANA HANA ARZIKI

1- baccin asuba
2- karancin sallah
3- kasala
4- Ha'inci

ABU 4 YANA BUSAR DA FUSKA DA TAFIYAR DA HASKENTA

1- karya
2- bushewar zuciya
3- yawan tambaya ba akan ilimi ba
4- yawaita fajirci

ABU 4 YANA KARA HASKEN FUSKA

1- tsoron Allah
2- cika alkawari
3- yawan kyauta
4- kame kai

Allah ya sa mu lura kuma mu yi aiki da shi. Ameen thumma ameen.

Basheer Journalist Sharfadi
09/04/2015,



FADAKARWA GA MASU SHIGA FACE BOOK . (Mal.Aminu Ibrahim Daurawa)

Face book wata hanya ce ta gani, da saurare, da karantawa, da rubutawa, da yadawa.

Ka tabbatar, da jinka da ganin ka, da rubutunka, da karantawarka, da abinda ka yada, Allah zai tambayeka ranar Alkiyama,

Wasu suna ganin tunda su kadai, suke kamar babu, mai ganin su sai suyi abinda suka ga dama, alhalin Alllah yana ganin su.

Ga shawarwari domin amfanuwar mu:

1, Mu kiyaye idanuwanmu daga kallon batsa,

2, Umarni da kyawawan aiyuka da hani da munana.

3, Duk abin zamu rubuta mu tabbatar da muna da cikkakiyar hujja ta ilmi.

4, Mu daina yawan bayar da labarin abinda ya shafemu, na yau da kullum, kamar yanzu na tashi, yanzu ina cin abinci yanzu kaza da kaza, duk wannan bai dace ba.

5,Mu kula da Kulla abota da mutumin da bakasan ko waye ba,

6, Yada jita jita, da kanzan kurege, da kage da sharri, da wani ko wasu,

7, Kiyaye isgili da baa ga wata kabila ko wani yare, domin bakasan yadda wannan mutunen sukeji ba.

8, Kula da lokaci, domin wasu suna wace gona da iri amfani da face book.

9, Masu kawo wani labari mara kan gado, kuma su zagi, ko tsinewa wanda yaki taya su, abin, kamar duk wanda baice kaza ba Allh ya yi masa kaza .

10, Yada kalaman batsa, da hotunan batsa, da maza masu shigowa da hotunan mata, da kuma mata masu shigowa da hotunan mata, da masu daukan haton mace batare da sanin ta ba su yada a face book .

Duk wadannan abubuwa suna faruwa da fatan zamu kiyaye,



***YADDA AKEYIN WANKAN JANABA***
.
Da farko Idan Mutum yashiga Ban-'daki (bathroom) Zai farane da wanke Najasar dake tare dashi.
.
Ma'ana, Zai Fara wanke Al'aurarsa, da kuma duk wuraren da Maniyyi (ko jinin) ya taba ajikinsa.
.
(Misali tun daga Cibiyarsa har zuwa cinyoyinsa).
.
* Kuma Zai Qulla niyyah ne yayin da yake wanke Al'aurarsa.
* Sannan saiya wanke dukkanin Gabobinsa na Alwala.
Amma sau dai-dai ko 2 ko 3 duk wanda mutum yayi daidaine.
* Idan kaga dama zaka bar Qafafunka, Sai akarshen wankan.
* Sannan Saika wanke Kanka Sau Uku.
(tare da wuyanka da fuskarka gaba dayanta).
* Saika wanke tsagin Jikinka na Dama, har zuwa Kafarka ta dama.
* Sai kuma tsaginka na Haggu, kahada har Qafarkata haggu din.
* Ya zama wajibi kacire zobe daga hannayenka (Idan ya matseka) kuma dole ka Tsetsefe dukkan yatsunka na hannu dana Qafa.
* Ka chuda Kafarka sosai.
Musamman idan inhar kanada kaushi.
* idan kazo wanke kowanne tsagi, ka tabbatar da cewa kana Chutchuda Bayanka sosai.
* Idan kuma hannunka baya iya kaiwa, sai kasamo wani Tsumma ko Kyalle mai tsafta, KaJiqa-shi, Sannan ka Chutchuda dashi.
* dole ne ka chutchuda Ko ina ajikinka.
Musamman ma idan kana da Qiba.
* Dolene Ka wanke Duburarka sosai tun farko.
Kada kayi la'akari da cewar"Ai bakayi bahaya ba".
A'a. Ai nan dinma jikinka ne.
Idan baka wanke taba, to wankanka bai yiwu ba.
* Ka kula da Ramin cibiyarka.
Ka tabbatar cewa Ruwa yashiga har nan.
* Ya zama dole'yan uwa mata su tabbatar cewa Ruwan ya ratsa har cikin Kitsonsu yayin wankan.
* Namiji idan yanada gemu, to lallai ne ka tabbatar cewa ka Tsetsefe shi komai Kaurinsa da duhunsa.
~~ ~~ ~~ ~~ ~~ ~~ ~
.
NOTE: Zaka iya amfani da wannan alwalar wacce kayi yayin wankanka.
Indai har baka sake ta'ba al'aurarka ba bayan kayi alwalar.
HAKA AKE YIN WANKAN JANABA, HAILA, NIFASI, DA KUMA WANKAN SHIGA MUSULUNCI.
.
Wallahu A'alam.



BABU HADI!! YIN ASUWAKI SHINE GABA DA MAULUDI
.
.
.
.
Hadisi ya tabbata daga Abi Hurairah (r.a) yace:
.
'Hakika Annabi (s.a.w) yace:-
''Ba dan kada na matsawa Al'ummata ba dana umarce su dayin Aswaki akan a yayin ko wacce Al'wala''
.
{Imam Malik A Muwadda 1/66/115, Nasa'i 1/68, Imam Ahmad 2/46, Ibn Khuzaimah 140,}
.
.
A suwaki dai sunnah ce saboda tabbatar sa daga Annabi (s.a.w) Amman kash se dai Yan Dariku da Yan shi'a suna fifita mauludi akan sa Amman yan uwa in muka duba xamuga Shi son Annabi shina biyayya cikin abinda yayi umarni dashi, Gasgata shi cikin abinda ya bada labari dashi, Nisantar duk abinda yayi hani.....
.
.
To amman se ga yan ta mauludi sun ki bin Abinda Annabi yace mman sun dauka na Christochi saboda su sun raba hanya da,
.
''LAKAD KANA LAKUM FI RASULULLAHI USWATUN HASANATUN LIMAN ..........'
.
.
Ya Dan uwa hakika An saukar da aya cewa:
.
''AL'YAUMA AKMALTU LAKUM DINAKUM''
.
Sannan Imam Muslim Ya rawaito Hadisi Annabi (s.a.w) yace:
.
''Babu wani Annabi da Allah ya aiko Face ya kasance hakki a gareshi ya shiryar da Al'ummarsa Al'khairin da ya sani Sannan ya tsoratar da su sharrin daya sani garesu''
.
.
To amman abin mamaki yan tamauludi sun rike gam sunce :-
.
'Aaaaaaaaa Shi wanga mauludi shike nuna son Annabi A ranar mauludi a na samun.... Ana.... Ana...Kuma kunga In mun fito titi kunga yawan mu Kusan muke da gaskiya sbd in mauludin ga ba gaskiya ba ba xamuyi wannan yawan ba ''
.
.
Hmmm Allah (s.w.a) kuma yace:-
.
''WA'IN TUDI'I AKSARA MAN FIL ARDI YUDILLUKA AN SABILILLAH''
(an'am 116),
.
.
Dan Allah ina son a taimaka min a matsayina na dalibin Ilmi a kawo min hadisi guda daya tak ko aya da inda Hadisin yake sannan yaku yan uwa yan Son xuciya masu koyi da su .......... Dan Allah in kun kawo aya ku kawo Tafsser din da kuka samo fahimtar da kuka kawo,
.
HADISI DAYA IDAN BABU MUKUMA ZAMU KAWO NA HARAMTAWA,
.
Duk wani Al-khairi munyi Imani Annabi (s.a.w) ya sanar damu,
.
'YA AYYUHAR RASULU BALLIG MA.......'
.
A musulunci Hatta kashi yanada Hadisai Amman ba'a samu na maulud ba To yaya Abin yake??
.
.
Duk wanda ya tuhumi Annabi(s.a.w) da rashin isar da sko kafirine!!
.
.
Da sannu zamuzo da fashin baki akan mauludin nan domin mun san duk abinda ake sbd an dan dana kafin Allah ya ganar damu mu tuba mu nemi gafara,
.
Basheer Journalist Sharfadi
29/Dec/2014
www.sunnahsak.mywapblog.com



MAULUDI BAYA NUNA SON MANZON ALLAH. HASALI MA TSABA MASA NE.
.
Manzon Allah(saw) yace:
.
‘dayanku baya zama mai imani har sai na zama mafi soyuwa gareshi fiye da mahaifinsa, da dansa, da duk sauran mutane baki daya…
.
Sannan Allah(swt) yace:
.
ﻗﻞ ﺇﻥ ﻛﺎﻥ ﺁﺑﺎﺅﻛﻢ ﻭﺃﺑﻨﺎﺅﻛﻢ ﻭﺇﺧﻮﺍﻧﻜﻢ
ﻭﺃﺯﻭﺍﺟﻜﻢ ﻭﻋﺸﻴﺮﺗﻜﻢ ﻭﺃﻣﻮﺍﻝ ﺍﻗﺘﺮﻓﺘﻤﻮﻫﺎ
ﻭﺗﺠﺎﺭﺓ ﺗﺨﺸﻮﻥ ﻛﺴﺎﺩﻫﺎ ﻭﻣﺴﺎﻛﻦ ﺗﺮﺿﻮﻧﻬﺎ
ﺃﺣﺐ ﺇﻟﻴﻜﻢ ﻣﻦ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ ﻭﺟﻬﺎﺩ ﻓﻲ ﺳﺒﻴﻠﻪ
ﻓﺘﺮﺑﺼﻮﺍ ﺣﺘﻰ ﻳﺄﺗﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﺑﺄﻣﺮﻩ ﻭﺍﻟﻠﻪ ﻟﺎ ﻳﻬﺪﻱ
ﺍﻟﻘﻮﻡ ﺍﻟﻔﺎﺳﻘﻴﻦ.
.
Ka ce: “Idan ubanninku da
ɗiyanku da ´yan´uwanku da
mãtanku da danginku da
dũkiyõyi, waɗanda kuka yi
tsiwirwirinsu, da fatauci wanda
kuke tsõron tasgaronsa, da
gidaje waɗanda kuke yarda da
su, sun kasance mafiya sõyuwa
a gare ku daga Allah da
ManzonSa, da yin jihãdi ga
hanyarSa, to, ku yi jira har Allah
Ya zo da umurninSa! Kuma
Allah bã Ya shiryar da mutãne
fãsiƙai.
.
‘Yan’uwa ku sani duk musulmi mai amsa sunar musulunci ya zama wajibi ya fifita soyayyarsa ga annabi(saw) fiye da kowa…
.
Sannan soyayya da akeyiwa annabi soyayyace ta biyayya da kauna. Ba soyayyah bace kaman ta tsakanin samari da budurwa…
yadda za’a gane mutum na son Annabi bawai kawai fada a baki ake ganewa ba, A’a a aikace ake ganeshi, kayi imani dashi sannan kabi umarninsa, ka fifitashi akan kowa.
.
In kuka duba zaku samu a rayuwar baffan Annabi abu daalib. Babu wadda yafiso fiye da manzon Allah(saw) amma da yake baiyi imani da annabi ba ya tabbata Annabi yace shine wadda za’ayi masa azaba mafi sauki a gidan wuta, lokacin mutuwarsa Annabi(saw) ya masa tallan kalman shahada amma Allah bai azurtashi da karba ba,
.
kunga inda kawai soyayya ba tare da imani da Annabi da yi masa biyayya ba tana tserar da mutum da abu dalib ya tsira…
.
Toh saboda haka ya dace ku tantance soyayya da kukeyi wa Annabi(saw) kada kuyi masa soyayya irinta Abu dalib domin bazata tserar daku ba…
.
Yana daga cikin soyayya ga Annabi girmama sakon da yazo dashi da kuma yada ta,
.
yana daga cikin soyayyar Annabi girmama iyalan gidansa da kaunarsu.
.
Yana daga cikin son Annabi son sahabbansa da girmamasu, duk wanda ya tabbata cewa shi sahabi ne ko ahlulbaiti toh ya zama wajibi wa masoya Annabi mu soshi kuma su girmamashi,
.
Sannan su kyamaci duk wanda ya kyamace shi….
.
Ya zama wajibi ga duk masoyin Annabi ya zama da’iman yana bibiyar ayyukan Annabi, ya zama duk ibadoji ko mu’amaloli da zaiyi ya zama yana koyine da Annabi(saw).. Iya gwargwado.
.
‘Yan’uwa kubi Annabi(saw) ku soshi zaku sami tsira….
.
Allah(swt) yace:
.
ﻗﻞ ﺇﻥ ﻛﻨﺘﻢ ﺗﺤﺒﻮﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﺎﺗﺒﻌﻮﻧﻲ ﻳﺤﺒﺒﻜﻢ ﺍﻟﻠﻪ
ﻭﻳﻐﻔﺮ ﻟﻜﻢ ﺫﻧﻮﺑﻜﻢ ﻭﺍﻟﻠﻪ ﻏﻔﻮﺭ ﺭﺣﻴﻢ.
.
Ka ce: “Idan kun kasance kunã
son Allah to, ku bĩ ni, Allah Ya
sõ ku, kuma Ya gãfarta muku
zunubanku. Kuma Allah Mai
gãfara ne, Mai jin ƙai.
.
Ga misali mai Alaka da wannan… Ya tabbata cikin sunnar Annabi(saw) azumtar ranar alhamis da litinin…
.
Toh anan ake gane cikakkken masoya Annabi(saw) ga lissafin kalandar musulunci an kusa sha biyu ga watar rabi’ul awwal ne, ko sha daya…
.
Toh kaman yadda muka sani ne akwai da yawa daga cikin musulmai anan Nigeria da ma waje. wadda sha biyu ga wata suke fita suna zaga cikin gari suna buga ganga suna rawa, suna fita da anko kala kala. Kuma suna fita manyansu da yaransu, domin a cewarsu sunayin haka ne don murnar haihuwar annabi(saw).. .
.
Toh kaga anan abinda nakeso ince shine su masu aikata wannan abu su sani ba da Annabi(saw) suke koyi ba, kuma wannan abinda sukeyi shaidan ne kawai yake kawata musu shi su daukeshi a matsayin addini.
.
Babu inda ya tabbata cikin addinin musulunci cewa Annabi ya tara al’ummar musulmai suna gudu acikin gari saboda murnar haihuwansa..
.
Haka aikin sahabbai bai nuna haka ba, haka tabi’ai da tabi’ittaabi’een..
.
Toh indai yin haka nuna wa Annabi soyayyane shin su masuyin wannan abu sunfi duk wa’innan son Annabi ne?
.
‘Yan’uwa ya dace mu natsu musan me mukeyi kada shaidan ya wautar da hankulanmu ya janyo mana sanadiyyar halaka…
.
Duk masoyin Annabi(saw) abinda zaiyi Ranar Litinin shine ya tashi da azumi, domin abinda ya tabbata Annabi yakeyi kenan….
.
Sannan masu daukar wannan rana a matsayin ranan murna ya dace su fahimta cewa a wannan ranan annabi(saw) ya bar duniya,
.
sannan kuma bayaanin cewa an haifeshi a wannan ranar akwai rauni, domin akwai ruwayoyi da suke nuna cewa ba’a sha biyu ga watan rabi’ul awwal aka haifeshi ba…
.
Saboda haka bai dace mu dauki wannan ranar a matsayin ranar murnar haihuwansa ba kawai….
.
Sannan aima bai dace ace wai musulmi sai kawai cikin rana daya ne kawai zai nuna murnarsa ga haihuwar annabi(saw) ba.
.
Wannan gafala ce… Ta Y'an Bidi'a
.
Saboda haka ‘yan’uwa wannan abu duk ba nuna soyayya bace ga Annabi(saw) nuna soyayya ga Annabi shine kabi umarninsa, kada kayi abinda bai saka kayi ba.
.
Muna fatan Allah ya nuna mana gaskiya ya bamu daman binta ya kuma nuna mana karya ya bamu daman kauce mata….
.
Basheer Journalist Sharfadi
29/Dec/2014

TaMaulude


KACIKA ZUCIYARKA DA AMBATON ALLAH A KODA YAUSHE DOMIN SHINE BAYA MANTAWA DA KOWA.
.
Manzon Allah (s.a.w) yace:
.
''Ayyuka nagartattu masu wanzuwa a wajen Allah (S.W.T) sune fadin:
"SUBHANA LILLAHI, WAL HAMDU LILLAHI, WALA ILAHA ILLALLAHU, WALLAHU AKBAR"
.
A wani hadisin kuma abu huraira Allah ya yarda dashi yana cewa:
Manzon Allah (s.a.w) yace:
Mutum yace:
"SUBHANA LILLAHI, WAL HAMDU LILLAHI, WALA ILAHA ILLALLAHU, WALLAHU AKBAR"
Shiyafi soyuwa a gurin Allah fiye da dukkan abinda rana ta hudo akansa.
.
Sahihu Musleem 4 hadisi mai lamba: 2073.
.
'Yan uwana kuji wannan irin romon lada da Allah yake rabawa a garemu, badan komai yakeyi mana hakan ba sai domin yanason mushiga Al-jannah.
Ya UBANGIJI kashigar damu Al-jannah firdausi madaukakiya.



Idan kana so kaga duniya bayan rasuwarka ka dubeta bayan rasuwar waninka.
.
Idan kadubi yadda masoya suke mantawa da masoyansu.
Wannan na nuna maka cewa wata rana kai ma za'a manta dakai bayan rasuwarka.
Ko duniya ta shagaltar dasu su manta dakai.
.
Dan uwa Ka sanya rayuwarka (tazama ta Allah baki dayanta).
Domin shine baya mantuwa kuma shine dauwamamme.
.
Ya Allah madaukakin sarki ka karbi rayuwarmu muna masu yimaka da'a kuma ka kyautata karshenmu.



HADIN KAI BAYA HANA WA’AZI DA FADIN GASKIYA!
.
(Sheik Muhammad Rabi’u Rijiyar Lemo)
.
Hadin kan musulmi da
dunkulewarsu su zama abu daya,
wani abu ne da Allah da Manzonsa
suka yi umarni da shi, kuma suke
son shi, Allah Madaukakin Sarki a
cikin lintafinsa mai girma a wurare
da dama ya hana bayinsa
musulmai rarrabuwa. Haka nan
Manzon Allah (S.A.W) ya hana
rarrabuwa, ya yi umarni da haduwa
da lazimtar Jama’a a wurare da
dama a cikin hadisansa ingantattu.
A gefe guda kuma tarin ayoyi masu
yawa sun zo akan yin wa’azi da
umarni da kyakkyawan aiki da
hana mummuna, kamar yadda
Manzon Allah (S.A.W) ya yi umarni
da isar da sakonsa koda kalma
daya ce mutum ya sani, don haka
hadin kai baya nufin ka kyale dan
uwanka akan barnar da yake ba,
shi ma ya kyale ka akan barnar da
kake kai ba, kada kowa ya fadi
abin da dan uwansa yake yi ba
daidai ba, wannan ba shi ne irin
hadin kan da Allah da Manzonsa
suke so ba, kuma ba shi ne aka yi
umarni da shi a cikin Alqur’ani da
hadisai ingantantu ba, Saboda
haka ba karamin kuskuren fahimta
ba ne, wani ya ce an raba kan
musulmi don ana yi musu wa’azi
akan su bar bidi’a da shirka, don
kuwa Allah Madaukakin Sarki a
cikin Suratul Ali-Imran inda ya yi
magana akan hadin kai da rashin
rarrabuwa sai da ya ratso da
maganar wa’azi da umarni da
kyakkyawan aiki da hani da
mummuna.
Magana ta gaskiya hadin kai na
gaskiya shi ne wanda aka gina shi
akan Alqur’ani da Hadisai
ingantattu akan fahimtar magabata
na kwarai, aka yadda da yiwa juna
nasiha da fadin gaskiya, amma
matukar zamu kawar da kanmu
daga kuraran juna, da bidi’o’i da
shirka da zagin sahabbai da
sauran miyagun akidu, mu daina
wa’azi a kansu, mu ja bakinmu mu
yi gum, wai da sunan hadin kai, to
babu ko shakka wannan ba hadin
kai ba ne, kuma babu yadda
zukatanmu za su hadu, kuma ba
shi ne Allah da Manzonsa suke so
ba. Allah ya yi mana gamonkatar.



Adalci wa Ahlussunnah
.
(Sheik Muhammad Rabi’u Rijiyar Lemo)
.
Wannan Batu Haka Yake
Masu hikimar zance sukan ce
.
“Mutum makiyin abin da bai sani
ba ne”. Babu ko shakka duk wanda ya kalli mafi yawan masu fada da Ahlissunnah, zaka gansu suna fadan ne akan jahiltar hakikanin tsarin (wato manhajin)
Ahlissunnah, wanda aka gina shi
akan ilimi gaskiya da adalci, mafi
yawansu suna dogara ne akan
abin da munanan malami suka
fada musu, ko kuma a kan wasu
dabi’u da ta’adu na jahilan
Ahlissunnah.
.
Alal misali idan mutum ya dauki
bajimin malamin nan na sunnah,
shahararre mai dimbin sani,
.
shehun musulunci Ibnu Taimiyyah,
.
zai ga da yawa daga cikin masu
zaginsa da kafirta shi da munana
shi, basu san komai a kan tarihinsa ba, basu karanta littattafansa ba,
kawai suna daukar abin da
makiyansa suka rubuta a kanshi na karya da taawilin maganganunsa su shiga yadawa da jayayya a kai,
amma duk wanda yake karanta
littattafansa da idon basira zai yi
mamakin irin adalci da tausasa da
fadin gaskiya na wannan bawan
Allah
.
Allah ya jikan wani malaminmu a Jami’ar Musulunci ta Madinah, ya kasance yana cewa,
.
“Mafi yawancin mutane suna
karanta littattafan Ibnu Taimiyyah
amma basa daukar ladabinsa da
halayensa”
.
Don haka dan uwa zama mai adalci wajen yin hukunci
ga wani mutum ko kungiya ko
wasu mutane, karanta abin da
suka rubuta da kansu, koma cikin
jiga-jigan littattafansu, tana nan ne zaka gane gaskiya,
.
Allah ya raba mu da son zuciya.



Mummunan Tasirin Kallon Fina Finan Tarihin Musulunci….
.
Ina kira ga ‘yan’uwa musulmai dasu kaurace wa wannan dabi’ah ta kallon fina finan tarihin musulunci wanda ake nuna sahabban Annabi(Sallallahu alaihi wasallam) aciki. Ko kuma wasu Magabata masu daraja. Hakan yana da matukar hatsari sosai. Musamman ga yara. Ka kiyaye kada ka rinka barin yaranka suna kallon wa’innan fina finai. Domin yana da matukar tasiri azukatan mutane. Wanda inhar mutum ya kalli irin wa’innan film din toh aduk lokacin da yaji sunan wani sahabi toh hoton da zai rinka zuwa zuciyarsa shine hoton da ya kalla a wannan film din. Wanda wa’innan masu shirya fina finai irin shiga da sukeyi ta tsabawa ta sahabban da kuma surarsu baki daya… Malamanmu na wannan zamani sun nuna haramcinsa . Sai mu kiyaye. Allah kiyayemu.



***MAGANAR ANNABI ZANBI BATA AUDU DAN GIDAN NASIRERE BA****
.
.
HAdisi ya inganta daga Annabi s.a.w kamar haka;-
.
An kar6i daga Abu mushar daga sa'eed bin Abdul'azeez daga rabi'ata bin yazeed daga Abdurrahman bin Ameerata ya kasance daya daga cikin sahabban Annabi s.a.w yace:-
.
'Daga Annabi s.a.w yace:-
.
''Ya ubangiji ka sanar da mu'awiyya rubutu ka tseratar dashi daga azaba''
.
{Bukhari 5/24,} {Dabarani a musnad shameen 1/190 da mu'ujmahl kabeer 18/251,} {musnad Imamu Ahmad 4/721.}
.
.
Sannna An kar6o wata riwayar makamanciyarta kamar haka:-
.
''An mu'awiyyat bin salih an yunus bin saif anil ha ris bin zayad an abi arahimus sam'e an irbadi bin sariyya R.A kala '
.'' Sami'itu rasulallahi s.a.w wa huwa yud auna ilas suhur fi shahri ramadana:
.
''Hallumu ilal giza'a mubarak'' summa sami'itahu yakulu:-
.
''ALLAHUMMA ALLIM M'AWIYYATUL KITABA WAL HISABA WAKIHIL AXAB''
.
.
(abu dawud 2/303} {nisa'i 2/79} {Ibn khuzaimah ya ingantashi 3/214 da ibnu hibban 16/191}
.
To Yan uwa ni dai Annabi aka aiko mana don haka shi zanbi babu ni ba audu halaka To anan in kunce mu'awiyya arnene to kuma Annabi yayi masa Addu'a to maganar wa zamu dauka ??
.
Ta la'anannnnneeee??
.
Nidai ta Annabi zanbi Kaipa?? Kepa??



***TATSUNIYAR RAPIDAWA GAME DA SARKIN MU'UMINAI MU'AWIYYA BIN ABI SUFYAN***
.
.
.
.
Bismillahirramanirraheeeeeem
.
Y'an uwa Assaslamu Alaikum kamar yadda mukace yau zamu fara dauko daya daga cikin tatsuniyoyin shaci fadi da y'an shi'a na fili (zakzaky) da na 6oye (Su Audu dan gidan na sirere) suke yi ga wannan bawan Allah mai dara ja to y'an uwa muna iyayin hakuri in ka xagi iyayen mu ko malumanmu Amman in ka ta6o As'habu rasuul to ba saurarawa wlh....
.
KOWA YA ZAGI UBAN WANI..............
.
.
Alhamdulillah bari mu dauko wata hikaya da suke yawo da ita ako ina suna jinginata ga Sayyidina mu'awiyya bin Abi sufyan ga yadda hikayar yake
.
Suka ce:-
.
''RAWAL BAXIRIY BI ISNADIN SAHIH AN ABDULLAHI BIN AMRI BINUL AS KA KUNTU JALISAN INDA RASULALLAH FA KALA :- YADLI'U ALAIKUM MIN HAZA L FAJR RAJULIN YAMUTU ALA GAIRA MILLATIY ' KALA WA KUNTU TARAKTU ABAHU KAD WADA A LAHU WUDU WA KUNTUKA ABISAL BAUL MAKHA KATA AN YAJ SA A KALA :- FADLI'A MU'AWIYYATA FAKALAN NABIYY HAZA HUWA''
.
Fassara
.
Su kace An rawaito daga balaziriy da sanadi ingantacce daga Abdullahi binul amr bin as yace ya kasance A zaune a gurin Annabi s.a.w sai Annabi yace ynz wani mutum zai 6ullo muku wannan mutumin ze mutu ba akan hanyata ba (shiriyata) Abdullahi bin amr bin as hankalinsa ya tashi domin ya bara mahaipinsa a gd yana Al-wala yasan idan yagama wajen Annabi ze tahoyana gudun ace mahaipin sane ana haka saiga mu'awiyya ya 6ullo sai Annabi yace 'wannan shine!
.
Wannan tatsuniyar sukan yi karya suce dabari ne ya fitar ko wadansu malaman kuma su hada lamba su bashi a cikin ko wane littafi domin dai biyan bukatar su
.
To wannan tatsuniyar tana cikin wani littaffi da y'an shi'a suke ji da shi mai suna (BIHARUL ANWAR NA AL-MAJLISI JUZ'I NA 33 SHAFI NA 67)
.

Wannan tatsuniyyar babu ita a
DABARO !
BAIHAKI !!
BUKHARI !!!
MUSLIM!!!!
ABU DAWUD!!!!!
MUSNAD NA IMAMU AHMAD
MUWADDA
NAILIL AUDAT
BULUGU
RIYADU
.
WALLAHI TALLAHI BABU WANNAN TATSUNIYYAR BABU ITA BA LABARIN TA KAI KARI WLH MA GA DAI YAN TAMBAYOYI
.
Daliban ilmi da farko
1. Akwai bukatar ku bincika waye balaxiriy rawin hadisin na farko??
Amsa:- Dan shi'a ne
.
2.Shin menene a cikin biharul anwar din da aka ciro tastuniyyar??
Amsa:- a cikin sa ne ake tuhumar nana Aisha r.a cewa itace ta kashe Annabi s.a.w ! A cikinsa ne ake tuhumar sayyadi Abubakar da cewa ya cinye gadon nana fadima R.A !! Wannan kadan kenan daga kafircin littain
.
3. Sunce duk me goyon bayan sarkin mu'uminai mu'awiyya bin abi sufyan ya halaka to Abdullahi bn amri binul as da aka ce shi ya bada labarin a bayan wa yake??
Amsa :- sayyadi mu'awiyya yake goyon baya
.
4.To idan kunce yan tawagar mu'awiyya sun halaka to ga tambaya! DALHATU BIN UBAIDILLAH yana cikin ashratul mubash-shirina bil jannah kuma mu'awiyya yake goyon baya ZUBAIR BIN AUWAM shima dan Al-jannah ne kuma mu'awiyya yake goyon baya to ya abin yake ne??
.
.
Amsa kawai... Zamu kawo falalar mu'awiyya bin Abi sufyan ingantacce nan gaba kadan insha Allahu



***Falalar Karanta Al-Qur’ani***
.
ﻋﻦ ﺍﺑﻦ ﻣﺴﻌﻮﺩ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ ﻗﺎﻝ
: ﻗﺎ
ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ :
“ﻣﻦ ﻗﺮﺃ
ﺣﺮﻓﺎ ﻣﻦ ﻛﺘﺎﺏ ﺍﻟﻠﻪ ﻓﻠﻪ ﺣﺴﻨﺔﻭﺍﻟﺤﺴﻨﺔ ﺑﻌﺸﺮ
ﺃﻣﺜﺎﻟﻬﺎ ﻻ ﺃﻗﻮﻝ: ﺃﻟﻢ ﺣﺮﻑﻭﻟﻜﻦ ﺃﻟﻒ ﺣﺮﻑ
ﻭﻻﻡ ﺣﺮﻑﻭﻣﻴﻢ ﺣﺮﻑ”
.
ﺭﺍﻭﻩ ﺍﻟﺘﺮﻣﺬﻱ ﻭﻗﺎﻝ:
ﺣﺪﻳﺚ ﺣﺴﻦ ﺻﺤﻴﺢ.
.
The Messenger of Allah (Sallallahu Alaihi wasallam ) said,
.
“Whoever recites a letter from the
Book of Allah, he will be credited
with a good deed, and a good deed
gets a ten-fold reward. I do not say
that Alif-Lam-Mim is one letter, but
Alif is a letter, Lam is a letter and
Mim is a letter.”
.
Manzon Allah(Sallallahu Alaihi wasallam) yace: ‘Duk wanda ya karanta Harafi Daga cikin littafin Allah, yana da lada, Sannan Wannan lada ta ninku zuwa Goma irinta, bance Alif laam mim harafi daya ba, A’a, alif Harafi, laam, harafi, Mim, harafi.


***SADA ZUMUNTA***
.
.
Daga Jubair ibn mud’am(Allah kara masa yarda) yace: yaji manzon Allah(tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yana cewa:
.
‘MAI YANKE ZUMUNTA BAZAI SHIGA ALJANNAH BA’.
.
Bukhari da muslim suka rawaito.
.
Wannan yana nuna mana mahimmancin sada zumunta a addinin musulunci. Wanda a wani hadisin annabi yayi nuna da sada zumunta na kara wa mutum arziki.
.
Sai muyi kokari wurin sada zumunta koda ko ga wanda suka yanke mana ita ne


***KAME BAKI DAGA MAGANGANU MARA AMFANI ***
.
.
ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﻫﺮﻳﺮﺓ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ ﻋﻦ ﺍﻟﻨﺒﻲ
ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻗﺎﻝ: “ﻣﻦ ﻛﺎﻥ ﻳﺆﻣﻦ ﺑﺎﻟﻠﻪ
ﻭﺍﻟﻴﻮﻡ ﺍﻵﺧﺮﻓﻠﻴﻘﻞ ﺧﻴﺮﺍﺃﻭ ﻟﻴﺼﻤﺖ” (ﻣﺘﻔﻖ
ﻋﻠﻴﻪ).
.
Manzon Allah (Sallallahu Alaihi wasallam) Yace:
.
‘Duk wanda yayi imani da Allah da ranar Qiyaama, toh Ya fadi alheri ko yayi shiru.
.
Takaitaccen Karin Bayani:
.
wannan Hadisi yana nuna mana Mahimmancin kame baki ga barin yin magana inhar mutum ya tabbata maganar nan Bazata kawo maslaha ba, toh kada ya furta yayi shiru shi ya fiye masa Alkhairi.


ASHARATUL MUBASHSHIRUNA BIL JANNAH.
______________
Manzon Allah (S.A.W.) yanada Sahabbai kemanin guda 120,4000.
Amma akwai wasu kebabbu, zababbu, fitattu wadanda akayi musu bishara da gidan Aljanna tun sunada Rai a wannan duniya.
Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yafada a hadisi cewa:
.
Anyi musu bishara da gidan Aljanna, wato sune:
.
ASHARATUL MUBASHSHIRUN.
.
Wadannan Sahabbai sune kamar haka:-
.
(1) Abubakar Saddiq (R.A).
.
(2) Umar Bin Khaddab (R.A).
.
(3) Usman Bin Affan (R.A).
.
(4) Aliyu Bin Abi Thalib (R.A).
.
(5) Dhalha Ibn Ubaidullah (R.A).
.
(6) Zubair Ibnul Awwam (R.A).
.
(7) Abdurrahman Bin Auf (R.A).
.
(8) Sa'ad Bin Waqqas (R.A).
.
(9) Sa'id Bin Zaid Bin Amr (R.A).
.
(10) Abu Ubaidah Bin Jarrah (R.A).
.
Allah Madaukin Sarki ya kara yarda ga wadannan bayi nasa.


KARANTA AYATUL KURSIYU BAYAN SALLAR FARILLAH
.
Annabi (s.a.w) yace:
.
"Duk wanda ya karanta Ayatul Kursiyu bayan kowacce sallar farilla, babu abinda zai hanashi shiga Aljanna, saidai mutuwa.
.
Allah ya bamu ikon karantawa.


ADDU'AR DUBA MARA LAFIYA
.
An kar6o daga Abbas (R.A) yace:
Annabi (s.a.w) yace:
.
''Babu wani mutum musulmi da zaije gaishe da wani Musulmi maraya lafiya, wanda ajalinsa baizo ba yace:
.
''AS'ALULLAHAL AZEEM RABBAL ARSHIL AZEEM AN YASHFIYAKA''
.
««fassara»»
.
Ina rokon Allah mai girma, Ubangijin Al'arshi mai girma yabaka lafiya.
.
Na rantse da Allah babu wanda zai karantawa mara lafiya wannan addu'ar face sai Allah (s.w.t) yabashi sauki saidai idan cutar ajalice


AYOYIN RUQIYYAH.
====================
.
Likitanci A Musulunci
.
WADANNAN SUNE AYOYIN DA AKE RUQIYYA DASU.
GASU KAMAR HAKA ZALLARSU:
.
1-SURATUL FATIHA.
2-SURATUL BAKRA,AYA TA 1 zuwa ta 5.
3-SURATUL BAKARA AYATA 163 zuwa ta 164.
4-SURATUL BAKRA AYA TA 255 zuwa ayata 257.
5-SURATUL BAKRA AYATA 258 zuwa aya ta 276.
6-SURATUL AALI IMRAN, AYATA 18.
7-SURATUL AARAF AYAH TA 54.
8- SURATUL MUMIN,AYATA 115 zuwa aya ta 118.
9-SURATUL SAAFAAT AYATA 1 zuwa ayata 10.
10 SURATUL HASHARI AYATA 21 zuwa ayata 24.
11-SURATUL JIN AYA TA 1 data 3 data 10.
12- SURATUL IKLAS.
13-SURATUL FALAQ.
14-SURATUL NAS.
.
To wadannan sune ayoyin ruqiyyah, amma wasu maluman sukan kara dawasu ayoyin.
Amma idan wanda za ayiwa yashafi sihiri, to sai an hada masa da ayatul fakku sihiri, ko ibdalu sihir, saboda karya wannan assihiru din.
Sannan kafin afara kuma yanada kyau ayi aduoin sosai.
Domin yinsu suma yanada taasiri, domin wani Aljanin daka karanta wadannan aduoin kafinma kafara zakaga yayi magana ko kuma kaji mara lafiyar yakama Ihu da Qarfi, kodai wani abu dake nuna yafita daga cikin hayyacinsa.


LOKUTAN AMSA ADDU'A.
~~~~~~~~~~~~~~~~
.
Kowanne lokaci mutum yayi addu'a dai -dai ne, Allah mai iko ne ya amsa masa.
.
Sannan akwai lokutan da Manzon Allah (s.a.w) yayi bayani suna da falala, idan mutum yayi addu'a cikinsu Allah yana amsawa.
Ga lokutan kamar haka:
.
1 -DAREN LAILATUL QADRI, idan Allah yayiwa mutum muwafaka ya ganshi.
2 -Yin Addu'a bayan mutum ya idar da Sallar farilla, ko nafila
3 -Yin Addu'a tsakanin kiran Sallah da tayar da Ikama.
4 -Yin Addu'a a lokacin da ruwan sama yake sawka (anso mutum yayi sallah raka'a 2) idan akwai halin yi.
5 -kowacce awa ta ranar Juma'a domin Manxan Allah (s.a.w) yace:
Akwai wata awa a ranar Juma'a, da mutum zai dace yayi addu'a da Allah ya amsa masa
6 -Lokacin da mutum yayi SUJJADA acikin Sallah.
7 -Yin Addu'a lokacin da mutum ya sami ruwan ZAM-ZAM zai sha
8-Lokacin da mutum yatashi TSAKADDARE yayi Nafil-fuli Allah ya taimakemu duniya da lahira yakuma amsa addu'o'in mu na alkhairi.


ABU GOMA A KWANA GOMA
.
(Mal.Aminu Ibrahim Daurawa)
.
Manzon Allah saw yace;
.
Babu wasu kwanaki mafi girma a wajan
Allah, wanda yafison aikin alkhairi
a ciki, kamar wadanann kwanaki
goma, ku yawaita hailala, da
kabbara, da godiya, a kwai
abubuwa goma, a ciki
.
1- Yin Hajji da Umra
2- Yin Azumi na kwana tara, inda
hali,
3-Yawan tuba da istigfari
4- Wanda zaiyi layya kada yayi
aski ko ya yanke farce, har sai yayi
layya
5- yawaita, Nafila, kamar sallah
karatun Alkua’ani mai girma,sada
zumunta, iyaye, makota,
6- Sallar idi
7- Layya
8- Azumin Ranar Arfa
8- yawan ambaton Allah
9- Tsayuwar arfa
10- Yaumul hajji al’Akbar


** TONON SILILI DAN GANE DA SALATIL FAATIH**
(1)
.
Assalamu alaikum wr, Barkanmu da saduwa a wannan lokaci!
.
Kamar yanda kuka sani, Salatul Fatihi shine salatin da Yan tijjaaniya keyi maimakon Salatul Ibraamiy da Annabi s.a.w ya koyar! Yau da Izinin Allah, zanyi bayani akanta tundaga tushe!
.
TARIHIN SALAATUL FAATIHI:
.
Kamar yanda na taba jin Tarihin saukar wahayin Salatul Faatihi daga Bakin Malamin Tijjaniyyah a Layinmu, sunan Malamin MUHAMMADU SALLAH, yace: Muhammadul Bakari yayi tsawon lokaci a Khalwah, yana roqon Allah yabashi salaati shaa kundum, shugaban Salatai, sai A Qarshe Allah ya turo masa da Malaa'ika ya kawo masa SALAATUL FAATIH cikin takardar Haske, wacce aka rubutata da Alqalamin Qudurah! Silsilarta kenan!
To shi kuma shugaban tafiya (shehu Tijjani) sai yace: (Lallai Annabi s.a.w ya bashi labari, cewa ita -salatul fatih- ba ta cikin ta'alifin Bakariy, sai dai shi Bakariy ya fuskanci Allah lokaci mai tsawo akan yabashi salaatin Annabi, wanda ya tattaro ladan dukka salatai da sirrikansu, ya kwashe lokaci mai tsawo kan wannan buqata, sai Allah ya Amsa masa, ya aiko masa da Malaa'ika da wannan salati, wato Salaatul Faatihi, tana rubuce a wata takarda ta haske) -Jawaahirul ma'aani 1/138.
.
Haka nan, Aliyu Haraazimiy na cewa: (Amma falalar Salatul Faatihi lima Ugliqa zuwa qarshenta, haqiqa naji shehinmu -Tuijjani- yana cewa: Na kasance da ambaton Salaatul Faatihi Limaa Ugliqa sanda nake dawowa daga Hajji a hanyata ta zuwa Tilmisaan, sabida abinda na gani na falalarta -salatul Faatihi din-, falalar kuwa itace: KARANTATA SAU 1, YANA DAIDAI DA SALATI (wanda Annabi ya koyar) SAU DUBU DARI 6 (600000)!
.
Kamar yanda yake a cikin "Wardatul juyub", marubucin littafin Wardah ya Ambato cewa: Sayyadi Muhammadul Bakariy Assiddiyqiy Ya sauka a Misra yana matsayin QUDUBI, yace (shi Bakari): DUK WANDA YA KARANTATA SAI BE SHIGA ALJANNAH BA, TO YA RIQE MA'ABOCINTA -salatil Fati, wato Bakari kenan- A WURIN ALLA!!!!!
Naci gaba da karantata har saida nai tafiya daga Tilmisaan zuwa Samgon, yayinda naga salaatinda cikin yinta sau 1, daidai ne da sauke Dalaa'ili sau 70000, sai na qyale salatul Faatihi lima ugliqa, na shagaltu da ita -waccan da tafi dalaa'ilu 70000 kenan-, itace:
.
(Allahumma salli alaa sayyidnaa Muhammad wa alaa aalihi salaatan Ta'adilu jamiy'I salawaati ahli mahabbatika wa sallim salaa sayyidnaa muhammad wa alaa aalihi salaaman ya'adilu salaamuhum), sabida abinda na gani na falalarta mai yawa, sai Annabi s.a.w ya Umarceni da na koma karanta Salatul Faatihi lima ugliqa, sanda ya umarceni da komawa salatul faatih, sai na Tambayeshi s.a.w gameda Falalarta, sai ya bani labari da farko: da cewa karantata sau 1 tana daidai da Qur'ani sau 6, sai nan na biyu ya bani labari, karantata sau w, yana daidai da dukkan tasbihi da ya auku cikin halittu da dukkan zikiri, da dukkan addu'a babba ko qarama, da Qur'ani sau dubu shida 6000, domin shi yana cikin zikiri ne.........) -Jawaahirul Ma'aani: 1/94-.
.
Kunji cikin tatsuniyar tasu:
.
1: Allah ne ya Aiko Malaa'ika ya kawowa Muhammadul Bakari salatul faati.
2: salaatul Faati -wacce bakari ya kawo- tafi salatin da Annabi s.a.w sau 700000.
3: Tafi saukar Qur'ani sau 6.
4: kai Tafi saukar Qur'ani ma sau 6000.
5: Annabi s.a.w shine duk ya fadi wadannan falalolin salatul faatih din.
6: Duk wanda Ya karanta salatul Faatihi ko sau 1 ne a rayuwarsa amma kuma sai ya shiga wuta be shiga Aljannah ba, to ya shaqo Muhammadul Bakari agaban Allah!
.
Kai da dai sauran bayanai, duk wanda ya karanta rubutun sama zai sha bayanai!
.
**Da haka nake cigiyar duk wani bijimin Batijjane dan Amutu riqaqqe balagagge isashe qosashshe da ya fito ya kare wannan Qaryar da shehu Tijjani yayi!
.
Kunsan ma ABIN MAAMAKI? Wallahi wannan Salaatin Ya Girmi Tijjani da Bakari da sama da shekaru 1000**
.
Bisimillah


Abahuraira ya rawaito cewa :-

Annabi(s.a.w) yayiwa MU'AWIYYA R.A addu'a cewa
.
"Allah ka sanyashi shiriya kuma abin shiryar wa"
.
(sinani tirmixi)

imam ahmad da irbadi bin sariyya da dabarani sun rawaito
annabi (s.a.w) yayiwa mu'awiyya addu'a cewa

."''ALLAH KA SANAR DA MU'AWIYYA RUBUTU KA KUMA TSARE SHI DAGA AXABA"
.
(MUSLIM)
.
HAKA A HADISIN UMMU HARAM ANNABI YACE AN GAFAR TA WA MAYAQAN TEKU
KUMA MY'AWIYYA NE COOMANDER
KAGA KENAN ANNABI YA YABI MUA'A WIYYA

SHIN ANNABI KAKE TUHUMA AKAN YIWA MU'AWIYYA ADDU'A???

KO KUMA KA SAN GASKIYA KAWAI ABINDa AMIRULJAHILEENA YACE DA SHI KAKE AIKI???


WANENE MAI DA”AWAH ???
.
(Sheikh Muhammad Kabir Haruna Gombe)
.
Da yawan Mutane na zaton cewa; Kira zuwa ga Musulunci da Nusar da Musulmai kan Turbar Annabi, aiki ne da ya takaita ko ya rataya kan Manyan Malamai da Kuma Ustazai da wadanda ke da Ruwa da Tsaki cikin harkar Addini.
.
Aikin fadada Musulunci da Gyarawa Mutane zama a cikinsa, Nauyi ne da ya rataya kan Wuyan kowane Musulmi da Musulma, Manzon Allah yace:
.
“ Ku isar da Sako daga gareni, ko da Aya Daya ce kawai kuka sani”
Sau da yawa in Manzon Allah ya kammala zance sai yace:
“Wanda ya zo ya sanarwa Wadanda ba su sami damar zuwa ba”
.
Ashe, Duk wanda ya san Aya Daya, Nauyin kira zuwa ga Allah ya hau kansa inji Bakin da baya Karya(s.a.w).
.
Samari !! da Dattawa!! Ya zama muku Tilas ku tambayi kanku ?? Wace Gudummawa kuka bayar na Habaka wannan Tafiya?? A cikin Gidajenku ko tsakanin Abokanku?? Wajen Aikinku ko Kasuwancinku??
.
Allah zai tambayeka kan Damar da ka samu amma ba ka yi amfani da ita ba!!
.
Shin In wani zance ko Nasiha ta shige ka, Ka taba Sharing da Abokanka ??
.
Wa yace maka sai ka haddace Ayoyi da yawa?? Ko sai ka Iya Larabci?? Ko sai an nadaka liman?? Abinda ba a so shine; Ka fadi abinda baka da Masaniya a kansa?? Wannan kam in ka aikata zaka sha Azaba Ran Qiyama. Annabi(s.a.w.)yace:
.
“ Wanda ya yi min Karya da gangan ya tanadi Matsuguninsa a Wuta ranar Qiyamah”
.
Allah yasa Mu Dace.


MAICECE MU’UJIZA ?
.
(DARASI NA FARKO).
.
{Mal.Aminu Ibrahim Daurawa},
.
Abubuwan mamaki da zai iya
faruwa ta hannun dan Adam, gaba
daya kashi goma ne.
Na daya Mu’ujiza ko aya daga
Annabawa.kamar sandar Annabi
musa, ko raya matacce da warkar
da makaho da kuturu ga Annabi
isa, ko bubbugowar ruwa ta
hannun Annabi Muhammad saw.
.
Na biyu, Irhasat, abin mamaki
dake faruwa ta hannun Annabi
kafin aikoshi da manzanci, kamar
duwatsu da suke yiwa Annabi saw
sallama idan ya wuce ta gabansu
kafin aiko shi.
.
Na uku, karama, wanda take
faruwa, ta hannun waliyan Allah
kamar sayyadina Umar (ra ) ya
kirawo wani tabii mai suna sariya,
daga tsawon fiye da kilometer
1000, ya kuma jishi ba tare da
amfani da wayar sadarwa ba.
.
Na hudu Alma’una, shine wata
gudunmawa ta gaggagawa da
Allah yake yiwa wani bawansa
daya shiga wani matsatsi ko
damuwa, kamar yadda yazo a
cikin sharhin akidatul- dahawiyya
na shaik Usaimin, cewa wani
bawan Allah,tsoho ya dorawa
jakinsa kaya, sai jakin ya mutu
kafin zuwa gida sai ya roki Allah
ya rayashi domin ya isar masa da
kayansa zuwa gida, jakin ya tashi,
sai bayan sun isa gida sannan ya
mutu.
.
Na biyar tsafi wanda yake faruwa
ta hannun matsafa, kamar
matsafan lokacin Annabi musa, da
sukayi fito- na- fito dashi Allah ya
bashi nasara akan su.
.
Na shida, siddabaru ko rufa-ido,
wanda zakaga masu wasa da
miciji sukeyi, kamar kaga mutum
ya shiga cikin jaki ta jela ya fito ta
baki, ko ya zura allura ta kofar
hanci daya ,ya fito da ita ta kofa
daya.
.
Na bakwai, Ihana, (wato wulakanci
da kunyatarwa)wanda yake
faruwa ta hannun wanda yayi
daawar Annabta ta karya, kamar
Musailamul kazzab, lokacin da
yaji cewa wani mai ciwon ido yazo
wajen Manzon Allah saw yayi
masa Addu’a ya warke, shima sai
yace akawo masa mai ciwan ido
zaiyi masa Addu’a, da aka kawo
mai ciwon idon,yanayi masa tofi
sai idon ya rufe, ya dena gani
gaba daya.
.
Na takwas, istidraji, shine abin
mamaki da yake faruwa ta hannun
wanda yayi daawar uluhiyya, wato
matsayin Allantaka, kamar Dujal
wanda zaizo da abubuwan
mamaki, yace ayi ruwa ayi, yace
kasa ta tsage, yaje makabarta
yace matattu su tashi, kuma aga
sun tashi, irin wannan shi ake kira
shigo- shigo ba zurfi, ko talala, ko
jarrabawa, daga Allah domin yaga
zaa bishi, ko zaabi dujal mai ido
daya, wanda da shine Allah da
gaske yaya ya zama mai ido
daya?
.
Na tara, abubuwan mamaki ta
hanyar koyo, da kwarewa ko wata
baiwa, mutum yana iya zuwa da
abin mamaki wanda sauran
mutane za suyi mamaki, kamar
yadda muke gani, cikin shirye-
shirye na wasanni ko wata bajinta
ta hawa igiya ko nutso a ruwa, ko
kokawa ko daga wani abu mai
nauyi, da sauransu.
.
Na goma kayan kere- keren
zamani na kimiya da fasaha,
wadanda suke ta fitowa, a baya
babu su, na kayan sadarwa, da
abubuwan hawa,da sauransu, duk
abinda zaka gani daga dan Adam
na mamaki baya fita daga
wadannan abubuwa goma,
.
Wanda za muyi magana akai itace
mu’ujiza wanda kalmace ta larabci
tana nufin gajiyarwa, wato abinda
ya zama gagara koyo, ko gagara
misaltau, abinda yafi karfin wani
dan Adam wanda ba Annabi ba,
yazo dashi, don haka mu’ujiza
tana nufin wani abin mamaki da
daure kai, wanda Allah yake
gudanar dashi ta hannun Annabi
wanda zai tabbatar da cewa,
sakon da suke dauke dashi daga
wajen Allah yake, kuma ga dalili
akan haka wanda bai yarda ba
shima, yayi irin abinda sukayi ko
yazo da sheda akan haka.
.
Mu’ujiza ta kasu kashi uku, ko
tana shiga layi uku, duk wata
mu’ujiza ta Annabi, tana zama ko
nuna ilmi, ko wadata, ko iko da isa
wanda yafi karfin tunanin dan
Adam.
Dukkan mu’ujizozin da zamu kawo
na Annabi akan wannan layin
suke, ko, ilmi ko wadata, ko
kudura wato iko da isa


Ankarbo Hadisi daga Abi musa(radiyallahu anhu) yace:
.
manzon Allah(sallallahu alaihi wasallam) yace
.
: ‘Mumini da dan’uwansa mumini kaman gini ne sashe na karfafa sashi….
.
‘yan’uwa wannan hadisi yana nuna mana matsayin alaka dake tsakanin muminai, bai dacewa ka nemi wa dan’uwanka da sharri ko kaci mutuncinsa, ko ka rusa abinda ya gina. Abinda addini ya koyar damu shine mu dankule wuri daya mu taimaki juna akan gaskiya…
.
Allah taimakemu ya hadamu akan gaskiya


FADAKARWA KAN BID’AH!!!!!
.
‘YAN’UWA GA WATA SABUWA!
.
.Acikin Littafin malamin Hadisinnan Annawawi, a karkashin sharhin hadisinnan wanda ya shahara wanda yake hani da bid’ah. Hadisin ummuna Aisha(r.a) tace: manzon Allah(saw) yace:
.
‘duk wanda ya kirkiro wani abu ya sanya cikin wannan lamari namu na addini wanda baya cikinsa toh an mayar masa.’ Sai akace: ‘duk wanda ya kago wani abu ya sanya cikin addinin musulunci wanda kuma babu wannan abu aciki sannan bashi da wani asali da zai danganta wannan abu zuwa gareshi, wannan abu ya zamto abune wanda za’a mayar masa sannan bazama akoma a kalleshi ba. Sannan kuma wannan hadisi ta zama ka’ida daga cikin ka-dojin addini daukakakkiya yana zama tilas kiyayeta da kuma nuni dashi wurin bata duk wasu sababbin abubuwa da bid’oi. Haka take a rubuce kaman yanda kuka gani, ku duba riyaadussaliheen shafi na 77.
Saboda haka ‘yan’uwa
musulmai nake kira a gareku da ku zamto wayayyu a addini, ku zamto masu budaddun zukaata wurin karban gaskiya.
.
Haka kuma sanannen malaminnan wato imam malik, ga zancensa game da bid’ah…
.
Yace: ”duk wanda ya kirkiri bid’ah ya kirata kyakkyawa toh tamkar yana riya cewa annabi ya ha’ince annabtan da aka bashi ne bai isar duka ba’ sannan ya sake cewa ‘duk wani abu da bai zama addini ba lokacin annabi toh yanzu bashi yiwuwa ta zama addini’ duba al-I’tisaam kasha mamaki.
.
Sannan a aqeedah ta imam malik mai bid’ah ko sallama baza ayi masa ba. Duba A l-Ibaanah na ibn Battah,
441.
.
Toh ‘yan’uwa masu girma ku dubi irin wa’innan zantuka masu tsada… A hakikanin gaskiya akan wannan mas’ala ta bid’ah ansamu tsabani sosai tsakanin ‘yan’uwa musulmai wanda wasu suke ganin cewa akwai bid’ah mai kyau, akwai wasu kuma da suke ganin babu wata bid’ah mai kyau. Toh a hakika ‘yan’uwa in za’abi ka’ida ta addinin musulunci, babu wata bid’ah kyakkyawa. Duk wata bid’ah acikin addini batace…
.
Manzon Allah(saw) yace kullu bid’atin dalaala. Saboda haka dole mu dauki wannan ka’idar. Domin inka duba zakaga toh shin yaushe muka kammala da duk abinda annabi yazo mana dashi da har zamuyi shisshigi mu kirkiri naamu??
.
ga wata hadisi ta Manzon Allah(saw)
ﺣﺪﺛﻨﺎ ﺇﺳﻤﺎﻋﻴﻞﺣﺪﺛﻨﻲ ﻣﺎﻟﻚﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﺍﻟﺰﻧﺎﺩ
ﻋﻦ ﺍﻷﻋﺮﺝﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﻫﺮﻳﺮﺓﻋﻦ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ
ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻗﺎﻝ ” ﺩﻋﻮﻧﻲ ﻣﺎ ﺗﺮﻛﺘﻜﻢﺇﻧﻤﺎ
ﻫﻠﻚ ﻣﻦ ﻛﺎﻥ ﻗﺒﻠﻜﻢ ﺑﺴﺆﺍﻟﻬﻢ ﻭﺍﺧﺘﻼﻓﻬﻢ ﻋﻠﻰ
ﺃﻧﺒﻴﺎﺋﻬﻢﻓﺈﺫﺍ ﻧﻬﻴﺘﻜﻢ ﻋﻦ ﺷﻰﺀ ﻓﺎﺟﺘﻨﺒﻮﻩﻭﺇﺫﺍ
ﺃﻣﺮﺗﻜﻢ ﺑﺄﻣﺮ ﻓﺄﺗﻮﺍ ﻣﻨﻪ ﻣﺎ ﺍﺳﺘﻄﻌﺘﻢ.
.
Manzon Allah yace.Ku barni kan abinda nabarku akai, domin abinda ya halaka wa’inda suke gabaaninku tambayoyinsu, da kuma tsabawa annabawansu. Duk abinda na hanaku ku gujeshi, abinda kuma nayi muku umarni ku kawoshi dai dai gwargwado.
.
To ku duba fa ku gani ‘yan’uwa annabi yace babu wata bid’ah mai kyau kai kaazo kace akwai, kaga ka tsabawa annabi. Sanan kuma acikin ayah Allah yake cewa:
.
ﻭﻣﻦ ﻳﺸﺎﻗﻖ ﭐﻟﺮﺳﻮﻝ ﻣﻦ ﺑﻌﺪ ﻣﺎ ﺗﺒﻴﻦ ﻟﻪ ﭐﻟﻬﺪﻯ
ﻭﻳﺘﺒﻊ ﻏﻴﺮ ﺳﺒﻴﻞ ﭐﻟﻤﺆﻣﻨﻴﻦ ﻧﻮﻟﻪﻣﺎ ﺗﻮﻟﻰ
ﻭﻧﺼﻠﻪﺟﻬﻨﻢ ﻭﺳﺎﺀﺕ ﻣﺼﻴﺮﺍ.
.
Allah(s.w.t) yace: ”Duk wanda ya tsabawa manzon Allah(s.a.w) bayan shiriya ta bayyana a gareshi ya kuma bi tafarkin da ba na muminai ba, zamu jibinta masa abinda ya jawo wa kansa, sannan mu shigar dashi jahannama, makoma tayi muni”.
.
Toh ya dace ‘yan’uwa musulmai mu kula mudinga bin abu bisa ka’ida kada wani ya rudamu…
Sannan akwai wasu masu bin son zuciya, inkace musu duk bid’ah batane toh sai suyi ta kawo maka tawilce tawilce wanda bashi da asali, ko suce maka toh ai kaima kana bid’ah. Toh shikenan don inayin bid’ah ta zama maka hujjah kaima kayi? Ko kuma ka samu wasu suna kawo wani
zance wanda irin wannan zancen kawoshi ma jahilci ne, misali wa’inda basu ma fahimci ainihin me ake nufi da bid’ah ba. Sai su rika cewa… Toh kana shiga jirgi kaje makkah, kana yin visa kaje makka kuma duka annabi baiyi ba. Ko suce shiga mota ko amfani da waya da dai sauran shirme da suke kawowa. Toh irin wannan sai mu basu uzurin jahilci. Domin in akace bid’ah babu kyau toh ana zancen bid’ah cikin addini ne ba ta duniyarmu ba.. Abinda ya shafi duniyarmu annabi ya bamu cin gashin kai yace
.
‘ku kukafi sani game da lammurar duniyarku,
.
saboda haka wani yazo ya lissafo bid’ar duniya cikin jerin munanan bid’ah wannan jahilci ne. Ko kuma su kawo maka karshen nassin hadisin umar(r.a) da yace ni’imatil bid’ati haazihi sai su tsaya anan. Kaga duk wanda ya kawo irin wannan zance a bisa dalili na kirkirar bid’ah toh ya cancanci hukunci…ga nassini hadisin cikakke da suke boyewa

Allah yasa mudaace zan tsaya anan. Domin khairul kalaam ma qalla wa dalla walam yadul fa yumil…
.
Amma. Daga karshe inaso inja hankalin ‘yan’uwa masu karanta irin wannan post din da dun Allah akiyaye jawo husuma tsakaanin al’ummah. Inkakaranta baka gane ba sai ka nemi karin bayaani,
.
inkuma ka gamsu dun Allah banda tawili. Wassalaamu alaikum. Allah ya kara wa annabi yarda.


HUDUBAR ANNABI S.A.W
.
ANNABI (SAW)YA FARA DACEWA:
.
“Ya ku mutane ku bani hankalinku, domin mai Yiwuwa bazan sake kasancewa da ku bayan wannan shekaran ba,
.
saboda haka ku saurari abinda nake gaya maku da kyau, kuma (ku isar da abinda zan gaya maku) ga wadanda basa wannan wuri a yau.
.
Ya ku mutane kamar yadda kuka riki wannan wata, (na hajji) da wannan rana (ta arfa) da kuma wannan gari (na Makka) da girma kuma abin tsarewa, to, haka kuma ku riki Ran Musulmi da kuma Dukiyoyinsu da girma abin kuma karewa, ku maida wa Mutane kayan da suka baku Amana. Kar ku cuci kowa, saboda kar wasu su cuce ku, ku tuna fa, hakika ALLAH zai yi sakayya akan ayukakanku, ALLAH (SWT) ya hana cin riba,(wato kudin ruwa) saboda haka, duk abin da aka kulla ta kudin ruwa sai a warware shi. Ku yi hattara da shaidan, domin kiyaye Addininku. Yanzu kan ya fidda ran batar da ku akan manyan abubuwa (na sabo) saboda haka ku guji binshi akan kanana.
.
Ya ku jama'a hakika kuna da hakki bisa matayenku, amma suma suna da hakki bisa kanku, to hakkin su ne akanku da kuciyar dasu, Kuma ku tufatar dasu akan jin kai. ku bi dasu kyakkyawan biyarwa, ku kuma tausasa musu domin su majibintan al amurrankune,kuma mataimakan ku, Hakki ne akansu da kar su yi abota da duk wanda ba kwa so, kuma su nisanci zina.
.
Ya ku jama’a kuyi kyakkyawan bauta ga ALLAH (SWT) ku tsaida salloli biyar(5) na farilla, Ku Azumci Watan Ramadan ku Kuma bada zakka. Ku aikata aikin hajji in har kun sami daman yi. KU SANI FA, ko wane musulmi dan uwan musulmi ne. Dukkan ku dai dai kuke. Ba wanda yake da fifiko saman wani sai ta tsoron ALLAH, da aikata kyawawan ayyukka. Ku tuna fa(ya ku jama’a) wata rana za ku tsaya gaban ubangijinku, domin sakamakon ayyukanku,
.
saboda haka ku yi hattara kada ku yi sake da hanya madaidaiciya bayan na kau.
.
Ya ku jama’a ba wani annabi ko manzo da zai zo bayana kuma babu wani addini da zai zo (bayan addinin musulunci), saboda haka kuyi tunani sosai akan wannan magana dana gaya maku, kuma ku fahimce ta (sosai). Zan bar maku abubuwa guda biyu(2);
ga (alkur ani)
ga kuma (sunnah) ta.
.
In kun bi wannan ba za ku ta ba bata ba .
.
Allah yasa mudace,Wassalamu Alaikum.


BOKO HARAM SUN BAYYANA MANUFOFINSU A FILI:
=============>
Ana sanin Mutum ne ta hanyar me yake aikatawa ba me yake faɗi ba!
___ Shin me hakan ke nufi ne:
"A duk lokacin da aka dasa Bom kuma suka yi nasara ya tashi, sai Jaridu su rawaito cewar 'Ƙungiyar yan ta da ƙayar baya ne na Musulmai{Boko Haram}! Amman kuma idan masu dasa Bom ɗin suka yi rashin sa'a aka kama su, sai kuma a ga ai ba ma Musulmai bane Arna ne!"
Mu lura:
.
* Idan suka yi nasara Bom ɗin ya tashi,' Sai ace Boko Haram. Idan kuma suka yi rashin sa'a aka kamasu sai aga ba ma Musulmai ba ne!
Kenan su wanene Boko Haram ɗin?
"Shin wanda yake so ya yaɗa addinin Musulunci ta Jahar Borno ko Maiduguri zai faro ko kuwa zai faro ne daga Kudancin maso gabashin Nigeria? Mu dai mun tabbatar da cewar 99% na mutanen Mai duguri da Yobe Musulmai ne! Ke nan kalmar shahadar su ce ba ta karɓu ba ko ya-ya?"
"Duk wanda yake so ya kafa daular Musulunci, daga jihohin Maiduguri da Yobe zai faro kokuwa dai zai faro ne daga Abuja {Aso rock}? Kuma da Hukumar tsaron Nigeria zai yi ko da talakawan ƙasa waɗanda ko Constitution ɗin ma basu taɓa gani ba balle su yarda da shi?"
"Duk wanda yake so ya kafa shari'ar Musulunci a gari, shin zai kafawa jama'ar gari ne ko kuwa zai kashe mutanen garin ne gaba ɗayansu ya kuma ƙone garin sa'annan ya kafa tuta wai da sunan ya kafa shari'ar Musulunci? Kenan Zallar ƙasa ya kafama shari'ar?"
* Ta ina Boko Haram suke samun tallafi?
* kuma ta ina ake turo musu da kuɗaɗen: {ta Bankuna ko ta ina}?
* Ta ina suke shigo da Makamai: {ina Customs}?
* Daga wace ƙasa suke sayo wa: {ina Emigration}?
* Kuma a ina suke ajiye makaman idan sun sayo: {ina Security}?
* A ina suke samun Tankokin yaƙi irin na Nigeria alhali an daɗe da daina ƙera irin waɗan nan Tankokin a duniya {0ld technology or 0ld Modern technology}?
* A ina ƴan Boko Haram suke samun Sojojin yaƙi,' Daga Jahar Borno da Yobe? Kenan hakan na nufin "Ƴa_ƴa ne suke kashe iyayen su da ƙannensu, da matansu, da abokansu?" ko a zamanin Jahiliyya ba a taɓa samun haka ba!
* Shin an taɓa samu a tarihi cewar Ƴantawaye sun fi ƙarfin gawamnatin ƙasa ba tare da samun tallafi daga gwamnatin cikin gida ba ko ta waje:
a, An kifar da Gwamnatin Egypt ne ta hanyar samun goyon bayan Sojojin Egypt.
b, An kifar da Gwamnatin Libya ne ta hanyar samun goyon bayan NATO, Italy ma ta taimaka da makamai!
c, An kifar da Bagbo shugaban ƙasar {Cot, divour} ta hanyar samun tallafin Sojojin Afirka {E.U}!
e, An kifar da Sadam Husain ne ta hanyar amfani da Sojin Amurka!
f, An hamɓare Hittler ne ta hanyar amfani da Sojojin duniya!
g, An kifar da Ƙisra, Rom, Farisa ne da Sojojin Khalifa Umar {r.a}.
h, Duk wani juyin mulkin da aka taɓa yi a duniya, to an yi sa ne da haɗin bakin Sojoji!
Don me za ace ƴan ta da ƙayar baya sun fi ƙarfin Gwamnatin Ƙasa? Ina rumbunan makaman Nigeria (babu komai ne a ciki sai Ak 47)?
Allah ya taimaki bayinsa.


***{IMANI DA MANZON ALLAH}***
.
.
.
.
An kar6o daga Abdullahi bin Amri binil asi {r.a} yace:-
,
Annabi {s.a.w} yace:-
.
''Da yanku baze yi imani ba Har sai zuciyarsa ta kasance me biyayya ce ga Abinda nazo da shi''
.
{Hakeem 163, Khadeeb 368,}
.
Allah {s.w.a} yana cewa:-
.
''Ina rantsuwa da ubangijinka ba zasuyi imani ba SAI sun yarda da hukuncin ka ga abinda ya sa6a a tsakanin su''
.
{Nisa'i 65}
,
.
Ya dan uwa kaji fa yin imani da manzon Allah to shin kayi imani da shi kuma kana aikata
.
1,bidia?
2,shirka?
.
Anya kuwa?? Kenan zuciyarka tana biyayya ga Abinda Annabi {s.a.w} yazo da shi??
.
Wallahi karya ne ta yaya kace kai masoyin manzo ne Amma baka koyi dashi??
.
Duk sunnonin sa ka sake su kana musu izgilanci!
.
.
Ya kai dan Bidi'a Ta'alau ila kalimatin sawa'im bainana wa bai nakum .....................
.
Kul in kuntum tuhibbunallaha fattabi uni yuhbib kumullahu wa.......


Kunga YANDA waliyai suke na gaskya ba nakaryaba masu da awar karama
.
.
ANNABI s,a,w yabada labarin wani waliyi maisuna sa'id annabi yace da sayyadina umar ko bayan ba raina idan kahadu da wannan bawan ALLAH sa'id kace yaimaka addu a domin idan yaima addu'a za amsa bayan annabi yayi wafati da shekara 15 sannan umar yahadu da wannan bawan ALLAH saiumar yace kaine sa,id? Yace eh nine umar yakaremar kallo yaga yacika suffofin da annabi yafadamar saboda harda wani tabo da annabi yace akwai abayan wannan bawan allah umar yagani sai umar yace bawan allah karokarmin allah yagafar tamin yace to yaiwa umar addu,a sai labari yacika gari kowa yagane cewa sa'idu waliyine sai akai tazuwa kowa yace kaimin addu,a saiyaga cewa ankama girmamashi ana bashi girma saboda haka saifa yahada kayansa yabar garin yaringa buya dan kar agane inda yake tunda yagudu yabar garin har yanzu danake magana daku bawanda yataba jin labarin inda yake har gobe YASALAM! KUNJI SA'IDU waliyi nagasky mai karama ta kirki amma yanzu saikaga mutum da dogon carbi da uban rawani waishi waliyine mai karama kuma shine yake neman mutane suzo su sallamamar kaji mutum yana cewa waishi jikan annabine ma ana kunji ashe waliyan gaskya buya suke basaso asani amma yanzu fa dan uwa kunjifa yar uwa kinjifa dan haka wani kazami da rawani yadaina raina wayanku karya yake ba wali bane asalima waliyi shinma baya sanin yanada waliyantakar


*** HANYAR SHIGA AL-JANNAH ****
.
.
¤¤NEMAN ILMI¤¤
.
.
Allah {s.w.a} yana cewa:-
.
''ALLAH YANA DAUKAKA WADANDA SUKAYI IMANI DAGA CIKINKU WADANDA AKA BAIWA ILMI WASU DARAJOJI''
{mujadala 11,}
.
.
Yazo A cikin in gantaccen hadisin manzon Allah {s.a.w} cewa:-
.
.
''MAN SALAKA DARIKAN YALTAMISU FIHI ILMAN SAHHALALLAHU LAHU DARIKAN ILAL JANNAH''
.
.
Annabi {s.a.w} yace:-
.
'Wanda yabi wata hanya don neman ilmi to Allah ze saukake masa hanya izuwa Al-jannah'
.
{muslim}
.
.
Haka kuma Annabi {s.a.w} yace:-
.
''Man yuridullahu bihi khairan yufaqqihuhu fiddeen''
.
{bukhari & muslim}
.
.
Allahu Akbar ya ku Ahlussunnah ku tashi mu nemi ilmi domin da Ilmi ne ake bam-bam ce
.
1, karya da gaskiya
2, musulunci da kafirci
3,bidi'a da sunnah
.
Kai!! Da ilmin nan Ake! Ake!! Ake!!
.
.
Ya Allah ka bamu ilmi mai Amfani Kuma Allah kasa ya zama sanadin shigarmu Al-jannah


@@@ALLAHU AKBAR@@@
.
.
wato in kabi Abinda Annabi yazo dashi babu Abinda ze hanaka shiga Aljannah.
.
.
Hadisi ya tabbata Annabi {s.a.w} yace;-
.
''WATA SURA A CIKIN AL-KUR'ANI TANADA AYOYI 30 XATA XO DA MA'ABOCINTA HAR SAITA SHIGAR DASHI AL-JANNAH ITACE TABARAKA {suratul mulk}''
.
{sahihul jami' 3643}
.
.
ALLAHU AKBAR
.
Yazo a wani hadisin Annabi {s.a.w} yace;-
.
''SURATU TABARAKA TANA KARIYA GA AZABAR KABARI''
.
{sahihul jami' 3643}
.
.
Ya Allah ka tabbatar damu bisa kan sunnar Annabinka da yin riko da ita da fikoki kuma Allah kasa mu mutu akanta


***LAFAZIN SHEIK JA'AFAR***
.
.
.
IDAN BAKA SHIRYA KA MUTU BA...
.
.
Marigayi Malam Ja'afar a wata Lakcar sa ya na cewa:O
,
"Idan kai kana ganin cewa ba ka shirya ka MUTU ba, kana da inda zakai don kar ka mutu, to don Allah idan ina karatu ko ina huduba kadaina zuwa sahun gaba, don idan an harbeni kar jini ya vata ma shaddarka da kake ado da ita.
Don Allah idan ina karatu kadaina zuwa sahun gaba, idan ina huduba kadaina zuwa sahun gaba, dan idan an harbeni kar jini ya fallatsarmaka ya vata ma shaddarka da kake ado da ita"
.
.
.
Allahu akbar! Haka kuwan akai, cikin ikon Allah asubahin wata juma'a a masallacin sa dake dorayi, wasu Y'an ta'adda la'anannu y'an jahannama suka harbe Malam har lahira. Inda muryarsa ta dinga daukaka tana cewa
.
.
"INNA LILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN LA ILA HA ILLALLAH MUHAMMADUR RASULULLAH"
.
.
Duk jama'a Makota masallaci da wadanda suke nesa da Masallaci suna jinta cikin amsa kuwar Masallacin.
.
.
Allah sarki Malam Katafi amma har a yanzu kana raye,
.
.
Allah ya jikan Malam ya gafarta Musu shi da dan uwansa Malam Albani Zariya.
Da ma sauran Al'ummar Musulmi baki daya
Jaafar ks 1

WANNAN SUNAYE DADI GARE SU IDAN KUKA KIRANI DA SU YAN DARIQA DA YAN SHI'A
.
¤BAWAHABIYE INA JINDADISUNA SABODA SUNA ALLAH NE AL-WAHAB
.
¤DAN IZALA INAJINDADI WANNAN SUNA SABODA IZALA MA'ANARTA GUSARWA NE KUMA TANA GUSAR DA BIDI,A TA TSARDA SUNNAH
.
¤BASALAFE INAJINDADI SUNA SABODA SALAF AI SAHABBAI MANZON ALLAH (SAW) SUNE MASU WANNAN SUNA
.
.
Wannan duk sunaye ne masu kyau nikan bana bakin cikin idan aka kirani da su basan ko ku yan uwana Ahalusunnah ko kuna so ba
.
Nakega duk musulmi kirki bazai ki wandanna sunaye ba duk a cikin su babu suna banza.
.
Allah ya kara tsarda mun akan Sunnah amen


***FALALA DAGA ANNABIN RAHAMA***
.
.
.
.
KAI ALLAH AKBAR DUK AN CIKE DUNIYA DA KARYAR CEWA WAI MU Y'AN IZALA/SALAFIYYA BAMA SON FALALA SABODA MUNKI KAR6AR FALALAR WALIYAN SHEDAN
.
.
TO ALHAMDULILLAH MU CEWA MUKAYI DOLE NE SE DAI FALALAR TA ZAMO DAGA MANZON ALLAH (S.A.W) AMMAN IN BA DAGA NAN TAXO BA TO ACI DADI LAPIYA TUNDA WITH OUT PERMISSION FROM OUR PROPHET SO IT'S REJECTED NI KAM BASHEER NA ANNABI NAKE SO KAI FA???
.
.
BARI KUJI ME ABUL KASSIM YAKE CEWA;-
''Annabi (s.a.w) yace:-
.
.
''Wanda ya shiga kasuwa sannan ya ce :-
.
''LA'ILAHA'ILLALLAHU WAHDAHU LA SHARIKALAK LAHUL MULKU WA LAHUL HAMD YUHYI WA YUMEET WA HUWA HAYYUN LA YAMUT BIYADIHIL KHAIR WA HUWA ALA KULLI SHAI'IN KADEER''
.
.
Annabi (s.a.w) yace wanda ya karanta wannan ze shiga kasuwa to za'a rubuta masa kyakykyawa (lada) dubu sau dubu sannan a goge masa zunubi dubu sau dubu sannan akara masa daraja da ita sau dubu sau dubu sannan a gina masa gida A Al-jannah''
.
.
(sahihul jami' 6231)
.
.
Kai Allahu Akbar Yanxu me yafi wannan falala??
.
.
To ya y'an uwana y'an IZALA ynx ga falalar da Annabi ya bayar sannan kuma kace muyi taka??
.
.
To ya kai dan bidi'a damu da kai waye ya canki me cin??
.
.
Ya Allah ka tabbatar da mu akan sunnar Annabinka mu samu shahada a kanta


¤¤¤ KANA SON SHIGA AL-JANNA?? ¤¤¤
.
.
.
.
A wani hadisi Annbi {s.a.w} yace:-
''Hakika naga wani mutum yana jujjuyawa a cikin Al-jannah saboda wata bishiya da ya sareta a kan hanya saboda ta kasance tana cutar da mutane''
.......{muslim}
To y'an uwa kunga yadda wannan hadisin ya nuna mana hanyar shiga Al-jannah ta hanyar kawar da kaxanta daga kan hanya
Y'an uwa se ayi gaggawa cikin dukkan aikin Alkhairi kamar yadda Allah yace:-
''Fastabiqul khairat''
Ya Allah kasa mu a Al-jannah


***KAI ALLAHU AKBAR!!***
.
Allah (s.w.a) yana cewa:-
.
''Waf alul khaira la'allakum tuflihun'' (hajj 77)
.
'Ku Aikata Al-khairi kwa samu rabauta'
.
A wani hadisin kuma na Annabin mu (s.a.w) yace:-
.
''Wanda ya ya yewa musulmi wani bakinciki daga bakin cikin duniya Allah ze yaye masa bakin ciki daga bakin cikin lahira wanda ya saukakawa wani daga cikin tsanani Allah zai saukaka masa A duniya da lahira wanda ya suturta musulmi Allah ze sutur tashi a duniya da lahira Allah yana taimakon bawa matukar bawan yana taimakon y'an uwan sa''
.
(muslim & Ahmad)
.
Allahu Akbar ya dan uwa na Ahlussunnah
.
Shin kana so kaima Allah ya ye maka bakin ciki??
.
Kana so Allah ya saukaka maka??
.
Kana so Allah ya suturtaka??
.
Kana so Allah ya taimakeka??
.
Ni dai Ina soooooooo
.
Kaifa????
,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,
To ya dan Uwa Ahlussunnah ba xaka samu wadan can Abubuwanba se ka bi wadan can matakan da Annabinmu ya fada
Ya Allah ka bamu ikon Aikatawa


***ADDU'A IDAN ZAKA SHIGA BAN DAKI***
Yazo acikin hadisi kamar yadda Annabin rahama Ya koyar damu idan mutum ze shiga ban daki se yace:-
''ALLAHUMMA INNI A UZU BIKA MINAL KHUBSI WAL KHABA'IS''
[Bukhari 94]
A wata riwayar kuma kace:-
''A'UZU BILLAHI MINAL KHUBSI WAL-KHABA'IS''
[Abi dawud 6]
IDAN KUMA MUTUM ZE FITO DAGA BANDAKIN SE YACE:
''GUFRANAKA''
[Abi dawud 30]
Allah ka bamu ikon riko da sunnar Annabin mu muyi masa biyayya sau da kafa domin duk wanda yayi masa biyayya hakika xe shiga Al-jannah Allah kasa muna ciki
Wanda kuma ya sa6a masa........



¤¤¤ ME ZAKACE IDAN KA WAYI GARI DA SAFE??? ¤¤¤
.
Annabi {s.a.w} ya kasance idan ya wayi gari yana cewa:-
.
''As bahna Ala fidratil islam wa kalimatul ikhlas wa dini nabiyyina muhammadin {s.a.w} wa millati abiyna ibraheema haneefan musliman wama kana minal mushrikeen''
.
{jami'us sahih 2989, sahihul azkar 16,}
.
Wani lokacin kuma Shugaban mu yana cewa:-
.
'Subhanallahi wa bihamdihi adada khalqihi wa midada kalimatih '' sau 3
.
{jami'ussahih 2156, }
.
A wani hadisin kuma Annabi {s.a.w} yace:-

''Idan ya wayi gari yana yin istigfari a kalla sau 100''

{jami'ussahuh 1600}

Ya Allah ka tabbatar damu akan sunnar Annabinka da riko da ita garam gam



***ADDU'O'I DAGA ANNABI (S.A.W) IDAN ZE KWANTA BACCI***
.
Annabi {s.a.w} yakasance in ze kwanta bacci yana cewa:-
.
''Bismikal lahumma Amutu wa'ahya''
.
{Al-kalimuddayyib 24, Jami'ussahih 2754, Bukhariy 2425,}
.
Wani lokacin kuma yana cewa;-
.
''Allahummakiniy Azabaka yauma tab'asu ibadak''
.
{sahihul Azkar 23 }
.
Wani lokacinma yakan ce;-
.
''Bismika rabbiy wada'atu janbiy wabika arfu'uhu fa'in amsakta nafsiy farhamha wa'in arsaltaha fahfaxaha bima tahfixu bihi ibadaka s saliheen''
.
(Sahih tirmiziy 3401,)
.
Ya Allah ka bamu ikon riko da sunnar Annabinka daram dam kamar yadda yace muti riko da ita da fikoki


ABUBUWA [10] GOMA DA SUKE WARWARE MUSULUNCI
,
Daga;
SHEIKH MUHAMMAD BIN ABDULWAHAB
.
Ya yan uwa musulmai, dole ne mu san cewa akwai abubuwan da aikatasu yake warware musulunci [Idan ka aikata dayansu kafita daga musulunci kenan, Allah ya kiyaye].
,
NA DAYA (1) Tarayya a cikin bautawa Allah, [Misali; Kiran matattu da addu’a da neman tai mako daga garesu duk fannine na shirka]. Allah madaukakin sarki yace;
.
“Hakika, duk wanda yayi tarayya (shirka) da Allah, Allah ya haramta masa shiga aljannah, kuma makomansa wuta; kuma azzalumai babu wadansu mataimaka agare su’’
.
NA BIYU (2) Duk wanda yasanya tsani tsakanin shi da Allah. [Kamar; Mala’iku,Annabawa,Waliyyai ko makaman tansu] da mutum zai rinka kira da addu’a yana neman sucece shi, yana dogara dasu, To mai aikata haka ya kafirta, kamar yadda dukkan malamai suka tabbatar.
.
NA UKU (3) Duk wannda bai kafirta masu aikin shirka ba, da wanda yake shakkan kafircinsu, ko kuma yake inganta hanyansu; ma’ana [yana yabon aikinsu na shirka, yana basu goyon baya] Duk mai aikata haka shima ya zama kafiri].
.
NA HUDU (4) Duk wanda ya yadda da wata shari’a, hukuncin gwannatin zamani, data sabawa na Allah, da Manzo S.A.W, kuma ya fifita nasu akai.[Alhalin yana da daman aiki ko hukunci da shari’a Islama,] Wanda ya yadda da hakan yazama Kafiri.
.
NA BIYAR (5) Duk wanda yake kin abinda Manzo S.A.W yazo dashi, ko yaki yadda da halaccin abin, ko yaki aiki dashi, To wannan mutum ya zama kafiri. Saboda,fadin Allah, madaukakin sarki,
.
“Wannan saboda lallai su, sunki abinda Allah, ya saukar, domin haka ya bata ayyukansu”
.
NA SHIDA (6) Duk wanda yayi Izgilanci da wani abu na addini wanda Manzo S.A.W ya tabbatar, ko yayi Izgili ga masu aiki dashi, ko da lada ko ukubar da Allah ya tanada wa masu laifi, Shima wannan ya zama Kafiri. Saboda fadin Allah S.W. cewa;
.
‘‘Kace; shin da Allah da ayoyinsa da manzonsa kuka kasance kuna yin Izgili?. Kada ku kawo wani hanzari hakika kun riga kun kafirta bayan Imaninku’’.
.
NA BAKWAI (7) Aikata shirka; wanda a cikinsa hadda na raba masoya,kamar a jefa wa miji kin matansa; ko aikin mallakewa, wato asa mutum yaso abinda baya so ta hanyan sihiri (Bokanci) da dukkan makaman tan hakan. Duk wanda ya aikata daya daga ciki ya kafirta. Saboda fadin Allah, madaukakin sarki.
.
‘‘Su (mala’iku guda biyu Harut da Marut) basu koya ma wani (sihiri) ba, ba tare da sun gaya mishi (maganan kashedi) ba, sai suce ‘Hakika mufa fitinane kawai,don haka kada ku kafirta’’.
.
NA TAKWAS (8) Bawa mushirikai goyon baya, da basu taimako akan musulunci, shima kafirci ne. Saboda fadin Allah, ta’ala
.
‘‘Duk wanda ya jibin cesu daga cikin ku, to lallai ne shima yana daga cikinsu, hakika Allah baya shiryar da azzaluman mutane’’.
.
NA TARA (9) Duk wanda ya yadda da cewa wasu anyi musu izinin kauce wa shari’ar Annabi Muahammad S.A.W [ma’ana; zasu aikata dukkan abinda suka ga dama na sabon Allah] ba komai; Shima ya zama kafiri..
Saboda fadin Allah, madaukakin sarki.
.
‘‘Duk wanda yake neman wanin musulunci ya zama addini, to baza a karba daga gare shiba, kuma a lahira yana daga cikin wadanda sukayi hasara’’.
.
NA GOMA (10) Bijirewa addinin Allah gaba daya, ko bijirewa abinda Musulunci baya ingantuwa sai dashi, [misali; Mutum yaki yin Salla,ko Azumi, ko waninnsu] ko yaki koyon yadda ake aikata su, Yin hakan ma kafirci ne. Saboda fadin Allah ta’ala.
.
‘‘Kuma wa yafi zalunci (mugun aiki) Sama da wanda aka tunatar dashi ayoyin ubangijinsa, sa’an nan ya bijire musu hakika mu masu daukar fansa ne daga masu laifi (mujirimai)’’.
.
A wata aya Allah, madaukakin sarki. Yace;
.
‘‘Kuma wadanda suka kafirta, masu bijirewane daga abinda akayi musu gargadi dashi’’
.
Babu wani banbanci ga wanda ya aikata daya daga cikin wadannan abubuwa [10] goma da suke warware musulunci, da wasa yakeyi, ko da gaske yakeyi, ko kuma saboda tsoron wani abinda zai rasa na duniya,
.
Amma banda wanda aka tilasta..
Muna neman tsari daga Allah, ya karemu daga aikata duk wani abinda zai fitar damu daga wannan addini na gaskiya, ko ya janyo mana fushin Allah, da azabarsa. Ameeen.


ZA A HAQO QABARIN MANZON ALLAH {SAW}
A KOMA DASHI WAJEN MASSALLACIN MADINA.
"YAN BID'A NA TA YAYATA WANNAN
LABARIN DA JARIDAR INGILA (DAILY MAIL)
TA BUGA A FACEBOOK.
KUJE KU SAKE DUBAWA DA KYAU, IDAN KUMA
BAKU IYA TURANCIN BANE TO BA A GIRMA
DA KARATU SAI A KOMA MAKARANTA.
RAHOTON YACE BABU WATA A ALAMA KO
RAHOTON DA YANUNA SARKI ABDALLAH DA
MALAMAN DAKE KULA DA MASALLACIN
MADINA SUN YARDA DA HAKE QABARIN BA.
RUFE GAWAR MANZO {SAW} CIKIN
MASALLACIN MADINA DAI, SHINE SABANI NA
2 DA MUSULMAI SUKAYI BAYAN RASUWARSA.
WASU SUKA CE AKAISHI MAQABARTAR
MADINA. SAI SAYYIDNA ABUBAKAR (R.A) YA
KARANTA HADITHIN DA YAZO CIKIN
SUNANUT-TIRMIZIINDA MANZO {SAW}
YACE: "BABU WANI ANNABI DA ZA A KARBI
RANSA FACE AN BIZNESHI A INDA AKA KARBI
RANSA." NAN TAKE AKA DAGA TABARMAR DA
YAKE KAI AKA HAKA QABARI A DAIDAI KAN
TABARMAR AKA RUFESHI.
BANA TUNANIN KODA WASA SAUDIYA ZATA
SABAMA WANNAN HADITHIN. IDAN TA SABA
KUMA BAZAMU BITA BA DOMIN MU BA MASU
BAUTAR MALLAMAN MU BANE, MANZON
ALLAH NE KAWAI MUKEBI IDO RUFE

ALLARAMA NASIRU GWANDU MTN CALLERTUNE

NAMES OF ALLAH 018772

AL TAWASUL BIL QURAN 018773

DU'A HIZUL 018776

Txt shorcode to 4100 to make it your callertune —
10610571 10203606404872726 4942617755802176212 n

***LADABIN LIMANCI.***
.
An karbo daga Jabir dan Abdullahi Allah yaqara yarda a gareshi yace:
.
An tambayi Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama cewa:
.
wace Sallah ce tafi ?
.
Sai Manzon Allah (S.A.W) yace:
.
Wacce ake Doguwar tsayuwa.
.
Bukhary da Muslim.
.
wato sallar da tafi falala itace wacce akai doguwar tsayuwa acikinta ammafa idan mutum yana sallah shi kadai kuma musamman sallar dare, in kuma limamine to sai yayi aiki da hadisin da Annabi (S.A.W) yake cewa:
.
"idan zakuyi limanci toku sauqaqa saboda cikin namu akwai marasa lafiya da matafiya da tsofaffi.
.
Allah kabamu ikon yin dai dai.


Dukkan al'umata zasu shiga aljanna inji manzon Rahama
.
Daga Abu Hurairah (R.A) yace:
,
Manzon Allah (S.A.W) Yace:
.
"Dukkanin al'ummata zasu shiga Aljannah sai wanda yaki"
.
Sai sahabbai sukace:
.
"Ya Rasulullah Wane zaiki ?"
.
Sai yace:
.
"Duk wanda yabini zai shiga Aljannah.
.
Duk wanda ya saba mini,to lalle yaki.
.
Bukhary ya rawaito.
.
Ya Allah mun rokeka kabamu ikon yin biyayya agare ka da Annabinka (S.A.W).


***Kaji masu tsoron Allah da gaske.***
.
Wani mutum yace da Abdullahi dan Mas`ud (r.a):
.
Lallai ni ina son a tasheni ranar kiyama cikin As`habul yamini.
(wadanda aka bawa littafinsu a hannun dama).
.
Dan uwan namu bai tsaya nan ba yasake cewa:
.
Lallai ni inaso a tasheni cikin mukarrabai.
(makusanta Allah).
.
Sai Ibn Mas`ud (r.a) yace masa:
.
NI KUWA FATANA INAMA DA IDAN NA MUTU BAZA A TASHENI BA!!!!
(ya fadi haka saboda tsoron me zai je ya tarar).
SubhanAllah!
.
Kunjifa 'yan uwa.
.
Sunyi aiki tukuru amma ahaka suna tsoron gamuwa da Allah!!
.
NI DA KAI DA KE KO YAYA MUKE???
.
Allah Ya Shiryar Damu Hanya Madaidaiciya.


WANDA BAZAIGA ANNABI (S.A.W) BA RANAR AL-KIYAMA.
.
Daga Nana Aisha (ra) tace:
Nakasance acikin dakina ina dinke wani tufafi nawa sai fitila (aci balbal) ta mutu kuma dakin yayi duhu lokacin da alluran tafadi kasa, ina cikin wannan hali ina laluben alluran saiga Manzon Allah (s.a.w) ya bullo da fuskarsa daga kofar daki.
.
Ya daga labulen kofar sannan ya shigo da fuskarsa.
.
nana Aisha tace:
.
Na rantse da Allah wanda babu abin bautawa da gaskiya saishi hakika sassan dakin ya haskaka daga hasken fuskarsa.
.
Saina waigo zuwa gareshi nace:
.
Mahaifina fansa agareka ya manzon Allah
.
BABU ABIN DA YAKAI FUSKARKA HASKE!
.
Sai Annabi saw yace:
.
"ya Aisha, kwarin azaba ya tabbata ga wanda bazai ganni ba ranar alkiyama!
.
Sai nana Aisha (ra) tace:
.
Wanene bazai ganka ranar alkiyama ba, Ya manzon Allah?
.
Ta maimata sau biyu.
.
sai Annabi (s.a.w) yace:
.
"wanda aka ambaceni agurinsa baiyi SALATI agareni ba."
.
SALLALLAHU ALAIHI WA SALLAM.
.
TIRMIDHI & IMAM AHMAD
.
Ya Allah kasa muga Annabi Muhammad (s.a.w).


ME ZAKA CE IDAN KAJE TA'AZIYYA???

Idan kaje ta'aziyya seka ce kamar yadda yaxo acikin hadisi ingantacce wanda yaje ta'xiyya xece:-

''Inna lillahi ma akaxa wallahu ma a ada wa kullu shai in indahu ila ajalin musamman
Fal tabseer wal tahtasib''

Ahkamul jana'ix 206-207 sahihul axkar 375

Idan ka xiyarci makabarta kuma se kace:-

''Assalamu Alaikum Ahladdiyar minal mu'uminina wal muslimina
wa inna insha Allahu bikum lahikun Antum lana faradun wa nahnu lakum taba 'un as alullah lana wa lakumul afiyyah''

Ahkamul jana'ix 240 . Sahihul kalamul dayyib 123 sahihul axkar 376

Allah ya bamu ikon riko da sunnar Annabinmu


☀☀☀ {HADISIN MU NA YAU} ☀☀☀

An kar6o daga Abi hurairah (R.A) yace

"Hakika manzon #Allah (s.a.w) yace"

☀ Wani mutum yana tafiya akan hanya se yaga wata kaya (me cutarwa) se ya kawar da ita (ya dauketa daga kan hanya) se Allah ya gode masa kuma ya gafar ta masa ☀

(bukhari 654)
(muslim 1914)

☀☀ A wani hadisin me Alaqa da wannan manzon rahama (s.a.w) yace kawar da qazanta daga kan hanya sada qa ce
---------------------------------------
☀☀ Ya #Allah ka sanya mu cikin masu samun rahamar ka a wannan wata me Al-barka

KU ISAR MIN DA SAKONA KO DA AYA GUDA CE"

*TSARABATA GAREKU*

Ibn Qayyumul Jauziy ya fada cewa

ABU 4 SUNA CUTAR DA JIKI

1- yawan magana
2- yawan barci
3- yawan jima'i
4- yawan cin abinci

ABU 4 YANA RUGUZA JIKI

1- bakin ciki
2- bacin rai
3- rashin barci
4- yunwa

ABU 4 YANA JANYO ARZIKI

1- yawan istigfari
2- tsayuwar dare
3- yawan sadaka
4- Zikirin safiya da yammaci

ABU 4 YANA HANA ARZIKI

1- baccin asuba
2- karancin sallah
3- kasala
4- Ha'inci

ABU 4 YANA BUSAR DA FUSKA DA TAFIYAR DA HASKENTA

1- karya
2- bushewar zuciya
3- yawan tambaya ba akan ilimi ba
4- yawaita fajirci

ABU 4 YANA KARA HASKEN FUSKA

1- tsoron Allah
2- cika alkawari
3- yawan kyauta
4- kame kai

Allah ya sa mu lura kuma mu yi aiki da shi. Ameen thumma ameen.


RADDI GA AMIRUL JAHILINA ABDUL-JABBAR DAGA ABDULKADIR JILANI ALLAH YA GAFARTAMASA
.
.
ALLAH YA JIQAN SHEIKH ABDULQADIR JELANII ALLAH YA HASKAKA KABARIN SA, WALLAHI IDAN KA CIRE IRIN SU SHAIKHUL ISLAM AHMAD DAN TAIMIYA DA KYAR KA SAMU WAND YA KAI ABDULQADIR JELANI TONA AQIDUN SU, MAI SON SANIN HAKA YA SAMU LITTAFIN SA MAI SUNA ALGUNYA , KA GA YADDA YAYI KACA KACADA RAFILAWA DA MIYAGUN AQIDUN SU.
,
.
YACE DAGA CIKIN AQIDUN SU AKWAI FIFITA ALIYU AKAN DUKKANIN SAHABBAI, KUMA SUNA NASSANTA SHI A MATSAYIN IMAMI BAYAN ANNABI, KUMA SUNA BARRANTA DAGA ABUBAKARDA UMAR DA WASUNSU DAGA CIKIN SAHABBAI, 'YAN JAMA'A KADAN SUKA CIRE, SABANIN 'YAN ZAIDIYYA SU NA SU SHI'ANCIN BAI YI NISA BA
.
.
YACI GABA DA CEWA:
.
.
, DAGA CIKIN AQIDUN SU SUNA CEWA 'HAKIKA AL'UMMA
)SAHABBAI( SUN YI RIDDA SABODA SUN BAR IMAMANCIN ALIYU, SAI MUTUM SHIDA KAWAI SUNE ALIYU,DA AMMAR DA MIQDADU BNL ASWAD,SALMANUL FARISII DA WASU MUTUM BIYU DABAN,
:
.
YA CI GABA DA CEWA:
.
.
DAYAWA DAGA CIKIN 'YAN SHI'A
SUNA CEWA: DUK WAI DUK WANDA YA YAQI ALIYU R.A KAFIRI NE YA KAFIRCEWA ALLAH MAI GIRMA DA BUWAYA, KUMA SUN ANBACI WADAN SU ABUBUWA DABAN BANDA WADANNAN.
.
.
WANNAN RADDI NE ABDULQADEER JIILAANII YAKE YI AKAN SU AMIRUL JAHILINA MASU CEWA SU SAYYIDINA MU'AWUYA 'YAN WUTA NE TUN DA SUKA YAQI ALIYU.
.
.
KADUBA LITTAFIN SA ALGUNYAH
MUJALLADI NA 1 SHAFI NA 86TURATHUL ISLAMII



Adalci wa Ahlussunnah
.
(Sheik Muhammad Rabi’u Rijiyar Lemo)
.
Wannan Batu Haka Yake
Masu hikimar zance sukan ce
.
“Mutum makiyin abin da bai sani
ba ne”. Babu ko shakka duk wanda ya kalli mafi yawan masu fada da Ahlissunnah, zaka gansu suna fadan ne akan jahiltar hakikanin tsarin (wato manhajin)
Ahlissunnah, wanda aka gina shi
akan ilimi gaskiya da adalci, mafi
yawansu suna dogara ne akan
abin da munanan malami suka
fada musu, ko kuma a kan wasu
dabi’u da ta’adu na jahilan
Ahlissunnah.
.
Alal misali idan mutum ya dauki
bajimin malamin nan na sunnah,
shahararre mai dimbin sani,
.
shehun musulunci Ibnu Taimiyyah,
.
zai ga da yawa daga cikin masu
zaginsa da kafirta shi da munana
shi, basu san komai a kan tarihinsa ba, basu karanta littattafansa ba,
kawai suna daukar abin da
makiyansa suka rubuta a kanshi na karya da taawilin maganganunsa su shiga yadawa da jayayya a kai,
amma duk wanda yake karanta
littattafansa da idon basira zai yi
mamakin irin adalci da tausasa da
fadin gaskiya na wannan bawan
Allah
.
Allah ya jikan wani malaminmu a Jami’ar Musulunci ta Madinah, ya kasance yana cewa,
.
“Mafi yawancin mutane suna
karanta littattafan Ibnu Taimiyyah
amma basa daukar ladabinsa da
halayensa”
.
Don haka dan uwa zama mai adalci wajen yin hukunci
ga wani mutum ko kungiya ko
wasu mutane, karanta abin da
suka rubuta da kansu, koma cikin
jiga-jigan littattafansu, tana nan ne zaka gane gaskiya,
.
Allah ya raba mu da son zuciya.

KOMA SAMAN SHAfI


→Labarai

Share|

Kaima shiga a tattauna da kai
* No boards.

Online: Guests: 1


→Ra'ayin jama'a game damu

 IDAN KANA BUKATAR A TALLATA MAKA HAJAR KA A WANNAN SHAFIN DA SAURAN SHAFUKAN MU KANA IYA TUNTUBAR MU TA WADANNAN HANYOYIN KAMAR HAKA:


Email: bjournalist55@hotmail.com

Phone No: 09035830253

Facebook: Basheer Journalist Sharfadi

Address: Ittihad Computer Centre,  No 92 Daneji Kano


MAI TALLA SHI KE DA RIBA


*Bayanan ka*
Browser din da ka hawo Mozilla

Kasar da kake United States

Adadin Maziyarta 924208

Adadin Wadanda Sukayi Comment 65691

A Wadanda Suka Shiga Tattaunawar Mu 54


Follow @bjournalist55
→Yi Adding Dina Ta Facebook
→Yi Like Na Dakarun Sunnah Page
→Yi Like Dina Ta Facebook

*Shafuka Masu Alaka Da Mu*

→Basheer Sharfadi wordpress
Basheer Sharfadi Blog Spot
UP
→Home

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah)
ISLAMIC DATE
  • phpimg2.php?it&ic=yellow



  • Click to Sms
    Click to Call


    Basheer journalist sharfadi3
    Coollogo com-1281358