pacman, rainbows, and roller s
Google69490f6862051cb8
google-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlBasheer journalist sharfadi14

Basheer journalist sharfadi14.jpg6
Basheer journalist sharfadi 11 1
Maraba Da Zuwa Wannan
Shafi Mai Al-barka 1

☀ Zabi inda kake son shiga ☀
Menunks
→Home
→Akidojin Ahlussunnah
→Addinin musulunci (35)
→40 Hadith (50)
→Fadakarwa (120)
→Neman labarai (20)
→Shi'a Kafirci (50)
→Hadith (55)
→Khudubobi (24)
→Tarihin magabata (60)
→Raddi / Maida martani (99)
→Face book post (30)
→Monthly Archives (60)
→Tambaya da Amsa (20)
→Sahabban Annabi {s.aw} (50)
→Taskar maluman sunnah (25)
→Akidar Y'an Shi'a Dangane da Al'kur'ani
→Fassarar Usulussunnah (20)
→Sheik Ja'afar {Rahimahullah} (65)
→Sheik Abubakar Gumi {Rahimahullah} (30)
→Sheik Dr. Muhammad Sani R/Lemo
→Salafiyyah Network Nigeria (100)
→Adam Sani Abu-Umayrah (99)
→Salaf Ustaz (79)
→Malama Ummi Ahmad Katsina
→Malama Amina Saleh Mande
→Labarai (40)
→Nishadantarwa (10)
→Siyasar Nigeria (9)
→Vidio (33)
→Audio (66)
→Hotuna (120)
→Internet Cheat (90)
→Site Achieve
→Application (10)
→Games (8)
→About me (01)

Wannan shafin mallakarCoollogo com-1281358 3
Ne




SHAFI DON KARUWAR MUSULMI
Daga @[420309128148902:0]

KIFI NA GANIN KA MAI JAR KOMA Kashi na 10 Audio Mp3

-Assalamu Alaikum Wanna Itace Cigaban Jerin Lakcocin Raddi da ake Gabatarwa ga Sarkin Kogo. Kamar Yadda aka saba wanna Karon Ma Matashin Malami Sheik Kabeer Basheer Abdulhamid Shine ya Gabatar da Lakcar,

-Shehin malamin ya maida Hankali akan Abinda Mal. Wazirin yayia Yan Tsakanin nan Inda aka jiyo Mal. Waziri yana murna akan wanda ya zagi Annabi Inda yace Wannan mutum rage masa Hanya yayi hassalima ya nuna shima abinda yake so yi kenan,

-Sannan Aka samu cikakkiyar sheda ga Ahlussunnah daga bakin Yayan sa. Kar na cika ku da surutu domin yin Downloading Shiga wannan Rubutun na Kasa:-

http://kiwi6.com/file/ld7vnif3o8

*Fatan Za'ayi Sauraro Lafiya Sannan muna neman Afwanku Game da Rashin Doro ta da wuri*

Basheer Journalist Sharfadi Abu Hafsah,
Jibwis Social Media Kano State PRO,
21/08/1436, 08/06/2015,


JIBWIS SOCIAL MEDIA KANO

Wannan kwamiti yayi zamansa a jiya kamar yadda ya sanar.

A zaman na jiya an gudanar da abubuwa dayawa, amma ga kadan daga ciki

* anyi nadin sababbin mukamai a mataki na jiha, inda aka nada mutane kamar Haka:-

- Vice chairman: Sani Abu-Unaisah
- Secretary: Lawal Mamman Bilbis
- Assistant secretary: Tasi'u Aliyu Bebeji
- P.R.Ò.: Basheer Journalist Sharfadi
- P.R.O II: sunusi Sa'idu Shekah
- Orgnz. Sec: Abdulmajid Nuhu
- Asst. Orgnz sec: Mu'azu Mustapha
- Treasure: Mahmud Abdulkadir Kofa
- financial Sec: Ahmad Ali Aliyu
- Editor: Ka'ab Muhd
- Auditor: Mustapha Muhammad
- Special Adviser: Dr. Tasi'u Rilwan R/Gado - Iyayen Tafiya: Mal. Ali Dan Abba & Mal. Anas Assalafiy Fagge.

* dama dai tun a wancan zaman Aka nada Awaisu Al'arabee Fagge a matsayin shugaban kwamitin na Jiha.

* An tsayar da Masallacin Ihya'ussunnah dake kofar Nassarawa a matsayin wajen da za'a dinga zama meeting.

* An tsayar da cewa za'a dinga zama meeting sau daya a wata, sannan za'ayi online meeting sau daya a kowanne wata.

Wadannan sune kadan daga cikin abubuwan da aka zartar a taron da aka gudanar a yau.

Allah yasa mu dace.

Chairman, Jibwis
Social media
Kano State.
24-5-2015


*FADA YA BARKE TSAKANIN YAN DARIKAR TIJJANIYYA DA MUTANEN GARI A KANO*

A daren Jiya Laraba ne wasu mabiya darikan Tijjaniyya suka shirya gudanar da wani gagarumin Bikin Mauludin Shehu Ibrahim Inyass a Unguwar Makwarari dake Kano Municipal,

Bisa Al'ada dai wadannan batattu sun saba gudanar da wannan mauludi lokaci bayan lokaci Inda akan gayyato Shehunnai da Sayyadai a Tafiyar azo a Shantake a Sheqe aya a zagi #Allah a Zagi Annabi!

Wannan Unguwa dai ta Makwarari nan ce Inda aka Kyankyashe Darikar Kadiriyya Kuma cibiya ce Ta Yan Bidi'a a baya wanda a yanxu Alhamdulillah ana fara samun Sauyi,

A Mauludin na Jiya an gayyato Fitacce Kafirin nan Mawakin Darikar Tijjaniyya wato TAKA LAFIYA (L) Inda bayan gama cashewa se akaji suna jawo ayoyi suna baiwa Inyass can ana cewa:

''DUK ME SON AL'JANNAH GA ALLAH YAZO!!
GA ALLOLI ga......

Wai a cikin su ma akwai Alloli!!

Jin Hakan ya tun zura mutan gari inda sukai dango fita suka tinkare su bayan kai ruwa rana aka farfasa musu motoci ciki har da ta TAKA LAFIYAN wanda tuni matsiyaci ya tsere, Har Saida Jami'an tsaro suka kawo Dauki bayan shafe tsawon lokaci a daren ana Fafatawa,

Babu Asarar Rai se dai Raunuka, Izuwa yanzu dai komai ya Dai-daita a yankin Inda Tuni Jami'an Tsaro sukayi a won gaba da Sayyadar Yan Tijjaniyyar yankin wadda ita ke jagorantar su,

Alhamdulillah muna godewa Allah da yasa mutan kano musamman Kano Municipal Inda nan ake wa Kallon cibiyar Mushrikai a kano Mahaifar su Sarkin Kogo an jima ana irin wannan Amman ko damuwa ba ayi to se gashi yanxu karantarwa Maluman Sunnah ta saka Mutan gari sun Farka!!

Alhamdulillah wannan Nasarace a garemu!!

Basheer Journalist Sharfadi Abu Hafsah,
14/05/2015,

Like @[656168224503950:0]
Like @[656168224503950:0]

Inyas Kabari

HANI AKAN FITAR DA BAYANIN ABINDA KE FARUWA A WAJEN KARATU, WA'AZI KO TARO.

Bismillahirrahmanirrahim.
Dimbin jinjina da yabo ga yan uwa ahlussunnah masu yada da'awa ta hanyar amfani da hanyoyin fasahar zamani (social media) na jihar Kano.

Sakamakon halin da muka tsinci kanmu aciki na halin rashin tsaro da kuma kokarin cigaba da gudanar da aiyukanmu bisa cikakken tsari mai kyau; muna jan hankalin yan uwanmu masu wannan aikin da su kauracewa sakin rahoto na abinda yake faruwa a wajen karatu/wa'azi ko tarurruka na malaman sunnah dake wannan gari mai albarka.
Daukar wannan mataki ya biyo baya ne bisa jawaban da masanan wannan harka sukayi akan wannan lamari.

Mun gano cewa hakan yana haifar da matsalolin da sunfi gaban lissafi, amma kadan daga ciki sun hada da:-

- bayar da sirrin tsaro na wajen da ake karatun ko wa'azin.

- hakan yana haifar da kurakurai wajen fitar da rahoton (tunda a lokacin akeyi, shikuma labari yafi ma'ana idan aka bayar dashi bayan gama faruwar lamari).

- samar da rahotonni mabanbanta daga mutane mabanbanta, ta yadda har wani labarin zaici karo da wani (toh da wanne za'a yarda)????

HAKANNE YASA------

Shugaban kwamitin masu yada da'awa a yanar Gizo na kungiyar izala na Kano yake umartar masu yada karatuttuka, hudubobi, wa'azuzzuka da ragowar tarurruka na malaman sunnah a jihar Kano da su kauracewa fitar da rahoton taro/wa'azi kafin tashi daga taro.

Allah yasa mudace da rabo mai girma.

Chairman, Jibwis
Social media
Kano state
9-5-2015


MALAMAI MAGADA ANNABAWA KASHI NA (5)

SHEIKH ABDULWAHAB ABDALLAH KANO

Shaikh Abu Abdullah Abdulwahab dan Mika’il dan Abdullahi dan Muhammad Sani . An fi saninsa da Shaikh Abdulwahab Abdallah. An haifeshi a ranar Juma’a 17 ga watan Zul Hijja shekara ta 1373 Hijiriyya wanda ya dace da 28 ga watan Agusta shekara ta 1953 Miladiyya.

Ya fara karatun alkur’ani a wajen wan mahaifinsa Alhaji Yahaya dan Imam Abdullahi. Sannan ya karanta littattafan fikihu har zuwa risala, a wurin babban almajirin kakansa Alhaji Tahir, wanda ya yi karatu a kasar Saudiyya. Sai gidan malam Shamsu a kabara wajen Malam Muhammad Ghali Inuwa,

A cikin Malamansa na kasar Saudiyya akwai Shaikh Abdul Muhsin Abbad, malamin da yake karatu a Masallacin Madina wanda malam ya karanci littafin sahihul Bukhari da sahih Muslim a wajensa.

A Zamansa na kasar Saudiyya kuma ya halarci karatun Shaikh Uthaimin na tafsir da muhaddarorin da yake yi lokacin watan Ramadan. Kuma ya karanta sunan At-Tirmizi da Nahawu a wurin Uztaz Sa’id Al-Ethiopy, wanda mazaunin Makkah ne da ke bayar da karatu a arewacin ka’aba. Haka kuma malam ya yi karatu wajen Shaikh Abdul’aziz Abdulladif da Shaikh Muhammad Madar Az-Zahrani da sauran malamai da dama.

Bayan Malam ya dawo Kano 1991 ya ci gaba da da’awa inda ya bude majalisan karatu a birnin Kano da kewaye. Daga ciki akwai karatun Sahihul Bukhari, wanda yake yi ranar asabar da lahadi da safe. Sai littafin Sunan Abi Dawud a kowace ranar Talata tsakanin magriba da issha. Sannan kuma ya karantar da littafin Sunan At-Tirmizi da Subulus Salam da Bulugul Maram da Umdatul Ahkam da sauransu a majalisai daban-daban dake birnin kano da kewaye.

Haka kuma malam yana rubuce-rubuce, daga cikin wadanda ya kammala akwai littafin fatawoyin azumin Ramadan da fatawoyin hajji da umra da fatawoyin falalar goman farko na watan babbar salla da littafin hisba da fatawoyin aure da matsalolinsa da sauransu. Sannan kuma malam yana gabatar da shirye-shirye a gidajen radiyo da talabijin na kasar nan da kuma kasashen waje kamar Togo da Benin da Niger da sauransu.

A yanzu haka Malam yana zaune a unguwar Sharada a birnin Kano, inda ya shagaltu da harkar da’awa da karantarwa da rubuce-rubuce. Kuma Allah ya albarkance shi da mata da `ya `ya.

ALLAH MADAUKAKIN SARKIMUKE ROKO YASANYA ALBARKA CIKIN RAYUWARSHI.

Sheik Abdulwahab Abdallah

MALAMAI MAGADA ANNABAWA KASHI NA (6)

SHEIKH ABUBAKAR MAHMUD GUMI.
An haifi Shaikh Abubakar Mahmud Gumi (R.A) ne a cikin garin Gumi a Jahar Sakkwato a Arewacin Nijeriya, a shekara ta 1340 bayan Hijira dai dai da shekarar Miladiyya 1922.

Mallam ya tashi ne cikin kyakkyawar tarbiyya da natsuwa da tsafta da neman Ilimi karkashin kulawar mahaifin sa (Alkalin Gumi a wancan zamanin). Kuma yayi karance-karancena zaure a majalisi daban-daban na Malaman da suka shahara anan kasar Hausa a wancan lokaci, tare da karatu na nizamiyya daga nan kasar har kasar Sudan da kasar Saudi Arabiya.

Shaikh Abubakar Gumi mutum ne mai kokarin binciken Al-kurani da Sunna kan hukunce-hukuncen Shari’a, tun daga abin daya shafi Tauhidi, Hadisi, Fikhu da luggar Larabci, wanda karantarwar da yayi ta tabbatar da haka.

Malam yayi rubuce-rubuce masu yawa, kadan daga cikin su akwai:-

Wannnan littafi da ke tare damu wato “Al Akeedatus Saheehah bi Muwaafakatish Shari’ah”

Tarjamar Ma’a’nonin Al-kur’ani Mai Girma.

Tafsirin Al-kur’ani: “Raddul Azhaan ilaa Ma’aanil Kur’an”.

Tarjamar littafin Hadisin “Arba’uunan Nawawiy”

Littafi mai suna “Manufata” ko (Where I Stand). Wannan littafi ya na da matukar anfani ga sanin tarin siyasar kasar nan data shafi Addini da Mulki, d.s.

Daga cikin daliban malam akwai su sheikh ismail idris da sheikh Yusuf Muh'd Sambo Rigachikun da sheikh ibrahim bawa mai shinkafa, da sheikh auwal albaniy zaria da sheikh rabiu daura da sheikh jafar adam da sauran malamanda bazasu girkuba
Malam ya rike mukamai masu dinbin yawa amma ga kadan daga cikinsu. Alkalin alkalai. Memba a rabidah wacce take saudiya.sannan uban kungiyar izala,sannan daya daga cikin wadanda suka assasah jama'atu nasril islam kuma shine mai baiwa sardauna shawara akan addinin musulunci. Sannan malam yasama kyautar faisal da ake bayarwa asaudiya ga manyan malamai da sukayiwa musulunci hidima.

Sir ahmad sardaunan sokoto yana cewa duk lokacinda malam abubakar gumi yashigo office dina sai gabana yafadi sabida inyashigo to ina tunanin wani kuskurene nayi wanda yazo yafadakardani shi domin baya barin ko ta kwana.

Muna fatan Allah (SWT) cikin Rahamar Sa yayi gafara da jin kai da daukaka ga wannan bawa na sa, wanda ya jaddada Da’wah ta Sunna a wannan kasa mai albarka, tun bayan rasuwar Shaikh Usman Dan Fodio (RH).

Sheik Abubakar Mahmud Gummi

SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!

Kungiyar Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa'ikamatis Sunnah ta Kasa Reshen Jihar kano karkashin jagorancin Sheikh D.R Imam Abdallah Saleh pakistan Tana jan hankalin daukacin Ahlussunnah da suyi watsi da wata sanarwa da wasu masu sojan gona sukeyi da sunan Kungiyar A Kafafan yada Labarai kan cewa Kungiyar Tana kira da a Zabi wani Dan takara,

Shugaban ya bayyana cewa Wannan ba Shine tsarinda kungiyar take tafiya Akaiba, domin kungiyace ta da'awa ta Yada Addinin Allah Ba ta Siyasa ba.

Allah yasa mu dace ya taimaki duk wanda yake taimakawa Addininmu.

Basheer Journalist Sharfadi
09/04/2015,


DR. AHMAD GUMI DA KUNGIYAR IZALA..!!

Ya Zama Dole ayi al'umma su rika yiwa Buhari Addu'ah ta alkhairi ____ Inji Dr. Ahmad.

A yammacin jiya Talata ne Kungiyar Izala reshen Jahar Kaduna suka Zauna zaman tattaunawa da Malamin addinin Musulunci mai kira akan Sunnah da tafarkin Magabata wato Dr. Ahmad Abubakar Mahmud Gumi a gidan sa dake cikin garin Kaduna.

Karkashin Jagorancin Shuwagabannin ta na Jaha

- Sheikh Muhammad Rabiu Daura
(Shugaban Majalisar Malamai na Jaha)
Alhaji Muh'd Tukur Isa
(Shugaban Kungiya na Jaha)
- Alh. Aliyu Jamfalan
(Sakataren Kungiya na Jaha)
- Sheikh Yusuf Kubau
(Mataimakin Shugaban Majalisar Malamai na Jaha)
- Sheikh Hamisu Ya'u
(Sakataren Masallacin Sultan Bello)

Zaman yakasance ne Sakamakon wasu rade-radin miyagun kalmomi da ake ta yadawa a gari cewa babban Malamim ne ya fade su, Na cewa Dr. Ahmad yace "Duk wanda suka zabi Gen. Buhari to sai sunyi dana sanin zaben sa."
Dalilin wannan ne yasa Kungiyar ta Jaha ta zauna dashi domin jin manufarsa da yi masa Nasiha.

Inda Malamin ya furta cewa wannan Magana Sharri ce 'kage ne aka masa, kuma karya ce, Sa'annan Kuma ya tabbatar ma Malaman da cewa tsakanin sa da Allah bashi da wata Manufa tsakanin sa da Wannan gwamnati wacca tayi Nasarar lashe zabe illa fatan alkhairi.

Ya kara da cewa idan jama'ah basu Manta ba, a Tafsirin sa na Watan Ramadan na Shekarar 2014 Shi da kansa ya jagoranci bude gidauniyar kudi domin yanda za'a kare zabe, kuma hakika yayi haka ne don a samu sauyi a kasar ganin yanda gwamnatin Azzalumai suka dade suna juya kasar da Zalunci da kashe-kashe.

Ya bayyana cewa idan da yana goyon bayan Azzalumai ta yaya zai gabatar da ita wannan gidauniya??

Sa'annan Shehin Malamin ya kirayi al'umma da cewa ya zama dole dasu tashi tsaye wajen yima Gen. Muhammadu Buhari Addu'ah neman Allah ya bashi ikon yin Adalci da kuma mataimakan sa na kwarai domin babu abinda Shugaban Kasan yake bukata a wajen mu yanzu bayan Addu'ah.

NASIHA.
Kungiyar Izala ta Jahar Kaduna tana yin Nasiha ga al'umma dasu ji Tsoron Allah..

Hakan ya fito ne Daga Magatakar kungiyar na Jaha
Alh. Aliyu Jamfalan.

Addinin Musulunci addini ne mai son Zaman lafiya a koda yaushe, Kuma mai tarbiyyan tar da Matasa akan yadda zasu bi Allah sau da kafa.
Addinin Musulunci shine tsira, kwata-kwata bai karantar da yada Jita-jita ba kamar yadda ake yinta yanzu.
Allah ta'ala da kansa yana fushi da mai yada jita-jita, Annabi s.a.w yayi tsawa ga masu irin wannan aika-aikan.

Shin Mutum zai so ranar alkiyama Allah yayi masa uquba (Azaba) mai tsanani akan wannan mummunar alkba'ira? Domin babu makawa Tilas Allah sai ya bibiyi hakkin wanda aka masa kage akayi gulmar sa a ranar da babu taro ko sisi.

Inda Daga Karshe Sakataren yaja hankulan ma'abota Internet (Yanar gizo) da suji Tsoron Allah su fadi alkhair su rubuta alkhairi, su yada alkhairi, Sai su samin Alkhairin Allah ranar gobe kiyama.

SAKO.
Sa'annan Kungiyar tana kara kira ga al'ummar jahar dasu mike da addu'ah akan Allah yasa ayi zaben nan na Asabar 11 ga watan April Lafiya a gama Lafiya, Kuma Suna kira da Mutane su fito suyi zabe su zabi Shuwagabanni na gari Nagartattu.

JIBWIS SOCIAL MEDIA KADUNA STATE.
08 April 2015


LAKCA! #LAKCA!! LAKCA!!!

Amadadin kwamitin masallacin jumu'a na

DARUS-SAHABA (kurna)
Karkashin jagorancin
Sheik Muhammad Usman

Yana farincikin gayyatar y'an uwa musulmai gagarumar lakcocin da ya shiryawa y'an uwa mata wadanda za'ayi kamar haka:-

LAKCA TA FARKO

Daga mai girma jami'in yada labarai na JIBWIS SOCIAL MEDIA KANO

Mal. @[100002581982587:0]

Daga bisa ni kuma malam @[100000580797862:0] ze yi masa ta'aliki

Rana:- Talata 13/12/1435 = 7/9/2014

LAKCA TA 2

Wadda shehin malami mujtahidi Na'ibi na biyu na masallacin Jumu'a na

ANSARUS-SUNNAH (fagge)

Sheik @[100001628771871:0]

Ze gabatar wanda malam Abubakar Datti ze masa ta'aliki

Rana:- Laraba 14/12/1435 = 8/9/2014

Dukkan wadannan lakcoci za'ayisu a masallacin jumu'a na DARUS-SAHABA dake kurna kan titin smogal a cikin birnin kano da misalin karfe 9:30 na safe

Allah ya bada ikon zuwa

Sanarwa daga mal. @[100004656256798:0]


Y''an gudun hijira suna bara a maiduguri
.
'Yan Gudun Hijira Na Bara A Maiduguri . Rahotanni daga Maiduguri a jihar Borno sun bayyana cewa wasu daga cikin 'yan gudun hijirar rikicin Boko Haram musamman mata da kananan yara sun fara fita yin bara, saboda halin kuncin da suka shiga. . Dubban mutane ne suka tsere wa rikicin Boko Haram daga sassa da dama na jihar ta Borno. . Wani mazaunin birnin Maiduguri ya fadawa BBC cewa 'akwai su da yawa wadanda suke cikin gari yanzu haka basu san inda zasu je su kwana ba, suna bara kan tituna kuma suna cin abinci'. . Yayinda wasu 'yan gudun hijirar ke zaune a sansanonin da gwamnati ta tanadar musu, wasu kuwa na zaune ne a gidajen 'yan uwa. . Hukumomi da sauran jama'a na cewa suna iya kokarinsu wajen taimakawa 'yan gudun hijirar.
Created at 2014-09-25 07:50:50


An sace wani dan kasar china a Nigeria
,
'Yan sanda a Najeriya sun ce wasu 'yan bindiga waɗanda ba a shaida su ba sun sace wani ɗan kasar China a jihar Kogi da ke a yankin tsakiya na ƙasar. Wani kakakin 'yan sandar na jihar Elvis Aguebor ya shaida wa manema labarai cewar mutumin wanda ma,aikaci ne a ma'aikatar ruwa ta gwamnati,an sace shi tun ranar Talata. Kuma mutanen da ke ɗauke da makamai sun taras da shi a gidansa idan suka yi awan aba da shi.Tun da farko sai da maharan suka yi harbi cikin iska kafin su tafi da shi.A ranar Lahadin da ta wuce ma, wasu 'yan bindigar sun kai famarki a kan wani ofshin 'yan sanda a jihar.
Created at 2014-09-25 07:47:36


*** 'Gawawwaki warwatse a kan tituna a Bama'***
.
Dan majalisar dattawa daga jihar Borno a Nigeria, Sanata Ahmad Zanna ya shaida wa BBC cewa gawawwaki na nan warwatse a kan tituna a garin Bama kwanaki biyu bayan 'yan Boko Haram sun kwace iko da garin. . A cewarsa, 'yan Boko Haram na sinturi a kan titunan garin Bama abinda ya hana mazauna garin yin jana'izar mutanen da suka mutu. Bayanai sun nuna cewar dubban mazauna garin Bama sun tsere zuwa Maiduguri sakamakon hare-haren da 'yan Boko Haram suka kaddamar a garin. . Sai dai gwamnatin Nigeria ta karyata rahotannin da ke cewar garin Bama na karkashin ikon Boko Haram. . Sanata Zanna ya bukaci gwamnatin Nigeria ta tura karin sojoji Maiduguri, babban birnin jihar ta Borno domin kare birnin daga harin 'yan Boko Haram, yana gargadi da cewa idan ba a dauki wannan matakin ba, to ba za ji dadin abin da zai biyo baya ba. . Hukumomi a jamhuriyar Kamaru sun ce yanzu haka 'yan gudun hijira fiye da 30,000 ne suka shigo kasar daga Nigeria sakamakon rikicin Boko Haram. . A yanzu haka dai 'yan gudun hijirar na zaune a wasu makarantu a yayin da wasu kuma suke zaune a karkashin bishiyoyi.


***Za a rage hutun makarantu a Nigeria***
,
Gwamnatin Nigeria ta sanar da cewa za a bude makarantu a fadin kasar a cikin watan Satumbar da muke ciki a maimakon watan Oktoba. . A watan Agusta ne hukumomi a kasar suka sanar da kara wa'adin hutun da makarantu ke yi zuwa watan Oktoba mai kamawa saboda a samu damar shawo kan bazuwar cutar Ebola da ta barke a kasar. . Cutar Ebola ta hallaka mutane bakwai a Nigeria tun lokacin da dan kasar Liberia, Patrick Sawyer ya shigo da cutar cikin kasar. Hukumar lafiya ta duniya dai ta kiyasta cewa mutane dubu daya da dari tara ne suka rasa rayukansu a Yammacin Afrika tun bayan barkewar cutar a watan Fabarairun wannan shekarar.
Created at 2014-09-05 08:46:33


*** NASARORIN DA ME MALAFA YA KAWO AKAN MULIKN SA ***
.
KADAN DAGA CIKIN NASARORIN DA JONATHAN
YA SAMU A
MATSAYIN SA NA SHUGABAN KASA 2O11-2O14.
1) Habbaka cutar H.I.V zuwa
Ebola
2) Sace 'Yan mata sama da 200
3) Mayar da Borno da Yobe filayen yaki
4) Inganta gaba tsakanin
Fulani da manoma
5) Batan Dollar sama Billiyan 20
6) kyale Boko-haram cin karan
su ba baabbaka
7) Yawan tashin bama-bamai a
Arewa
kashe malamai da 'ya'yan
su
9) Amfani da karfin soja a
kowane bangare amma banda kan boko haram
10) kashe kasuwancin arewa
Ya Allah ka kawo mana karshen wannan mulkin
Albarkacin Annabi.
Don son ku da Annabi kuce amin.
Created at 2014-09-04 11:29:59


BUHARI ZE TSAYA TAKARA A 2015
.
Wasu magoya bayan tsohon Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari sun ce, tabbas zai fito neman takarar shugabancin kasa a zaben da za' a yi a badi.
A fagen siyasar Najeriyar dai ana ta tababa a kan ko Janar Buharin zai sake fitowa takara a jam'iyyarsu ta APC mai adawa.
Hon Faruk Adamu Aliyu, makusanci Janar Buharin shine ya tabbatarwa da BBC shigar Buharin takara a zabe mai zuwa.
'Takarar Muhammadu Buhari tana nan daram dam' in ji Hon. Faruku Adamu Aliyu.
Kwankwaso ma yana tuntuba akan tsayawa takarar
Wani na hannun daman Janar Muhammadu Buharin kuma gwamnan jahar Kano Injiniya Rabi'u Musa Kwankwaso shima ya ce yana kan tuntubar magoya baya domin yanke shawarar tsayarwarsa takara.
Gwamnan ya ce kodayake bai kaiga ayyana takarar tasa ba, amma mutane da dama a ciki da wajen jam'iyyar su ta APCn na yi masa kiraye- kirayen ya fito.
Masana harkokin siyasa na kallon za a iya samun baraka a jam'iyyar adawa ta APC mai neman karbe iko daga PDP idan aka zo maganar wanda jam'iyyar zata baiwa tutar takarar Shugaban Kasa.
To sai dai Gwamnan Kano ya ce babu wani sabani tsakaninsa da Janar Muhammadu Buhari akan maganar takarar.
Created at 2014-09-04 11:27:47

koma saman shafi

→Labarai
1234...9899100»

Share|

Kaima shiga a tattauna da kai
* No boards.

Online: Guests: 1


→Ra'ayin jama'a game damu

 IDAN KANA BUKATAR A TALLATA MAKA HAJAR KA A WANNAN SHAFIN DA SAURAN SHAFUKAN MU KANA IYA TUNTUBAR MU TA WADANNAN HANYOYIN KAMAR HAKA:


Email: bjournalist55@hotmail.com

Phone No: 09035830253

Facebook: Basheer Journalist Sharfadi

Address: Ittihad Computer Centre,  No 92 Daneji Kano


MAI TALLA SHI KE DA RIBA


*Bayanan ka*
Browser din da ka hawo Unknown

Kasar da kake United States

Adadin Maziyarta 431097

Adadin Wadanda Sukayi Comment 65691

A Wadanda Suka Shiga Tattaunawar Mu 54


Follow @bjournalist55
→Yi Adding Dina Ta Facebook
→Yi Like Na Dakarun Sunnah Page
→Yi Like Dina Ta Facebook

*Shafuka Masu Alaka Da Mu*

→Basheer Sharfadi wordpress
Basheer Sharfadi Blog Spot
UP
→Home

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah)
ISLAMIC DATE
  • phpimg2.php?it&ic=yellow



  • Click to Sms
    Click to Call


    Basheer journalist sharfadi3
    Coollogo com-1281358